Sourate: Suratul Buruj

Verset : 1

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡبُرُوجِ

Na rantse da sama ma’abociyar manziloli[1]


1- Watau manziloli na rana da wata da taurari.


Sourate: Suratul Buruj

Verset : 2

وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡمَوۡعُودِ

Da ranar da aka yi alqawarin zuwanta[1]


1- Watau ranar alqiyama.


Sourate: Suratul Buruj

Verset : 3

وَشَاهِدٖ وَمَشۡهُودٖ

Da mai shaida[1] da kuma abin yi wa shaida


1- Watau kamar Annabi da zai ba da shaida game da al’ummarsa.


Sourate: Suratul Buruj

Verset : 4

قُتِلَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأُخۡدُودِ

An la’anci ma’abota rami (na azabtar da muminai)[1]


1- Wani azzalumin sarki ne da aka yi a Najrana ta qasar Yaman kafin aiko Annabi () wanda aka haqa masa rami aka hura wuta, ya riqa jefa muminai a cikinsa yana qona su da ransu.


Sourate: Suratul Buruj

Verset : 5

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلۡوَقُودِ

Na wuta mai ruruwa



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 6

إِذۡ هُمۡ عَلَيۡهَا قُعُودٞ

Yayin da suke zaune a gefenta



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 7

وَهُمۡ عَلَىٰ مَا يَفۡعَلُونَ بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ شُهُودٞ

Alhali su suna kallon abin da suke aikata wa muminai



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 8

وَمَا نَقَمُواْ مِنۡهُمۡ إِلَّآ أَن يُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Babu kuwa abin da suke tuhumar su da shi sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 9

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Wanda Yake da mulkin sammai da qasa. Allah kuma Mai ganin komai ne



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ

Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 12

إِنَّ بَطۡشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

Lalle damqar Ubangijinka tabbas mai tsanani ce



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 14

وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلۡوَدُودُ

Shi ne kuma Mai gafara, Mai qaunar (bayinsa na qwarai)



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 15

ذُو ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡمَجِيدُ

Ma’abocin Al’arshi Mai girma



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 16

فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Mai aikata abin da Yake nufi



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 17

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡجُنُودِ

Shin labarin rundunoni ya zo maka?



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 18

فِرۡعَوۡنَ وَثَمُودَ

(Su ne) Fir’auna da Samudawa



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 19

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي تَكۡذِيبٖ

A’a, su dai waxanda suka kafirta suna cikin qaryatawa ne



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 20

وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطُۢ

Allah kuwa Yana kewaye da su (da iliminsa)



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 21

بَلۡ هُوَ قُرۡءَانٞ مَّجِيدٞ

A’a, shi dai Alqur’ani ne mai girma



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 22

فِي لَوۡحٖ مَّحۡفُوظِۭ

A cikin Lauhul-Mahafuzu