Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ عَدُوِّي وَعَدُوَّكُمۡ أَوۡلِيَآءَ تُلۡقُونَ إِلَيۡهِم بِٱلۡمَوَدَّةِ وَقَدۡ كَفَرُواْ بِمَا جَآءَكُم مِّنَ ٱلۡحَقِّ يُخۡرِجُونَ ٱلرَّسُولَ وَإِيَّاكُمۡ أَن تُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ رَبِّكُمۡ إِن كُنتُمۡ خَرَجۡتُمۡ جِهَٰدٗا فِي سَبِيلِي وَٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِيۚ تُسِرُّونَ إِلَيۡهِم بِٱلۡمَوَدَّةِ وَأَنَا۠ أَعۡلَمُ بِمَآ أَخۡفَيۡتُمۡ وَمَآ أَعۡلَنتُمۡۚ وَمَن يَفۡعَلۡهُ مِنكُمۡ فَقَدۡ ضَلَّ سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi maqiyana kuma maqiyanku masoya, kuna nuna musu soyayya, alhali kuwa sun kafirce wa abin da ya zo muku na gaskiya, suna fitar da Manzo har da ku kanku don kun yi imani da Allah Ubangijinku, idan har kun zamanto kun fito don yin jihadi saboda Ni da kuma neman yardata. Kuna voye qaunarku gare su, alhali kuwa Ina sane da abin da kuka voye da kuma abin da kuka bayyana. Duk kuwa wanda ya aikata haka daga cikinku, to haqiqa ya vace wa hanya madaidaiciya



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 2

إِن يَثۡقَفُوكُمۡ يَكُونُواْ لَكُمۡ أَعۡدَآءٗ وَيَبۡسُطُوٓاْ إِلَيۡكُمۡ أَيۡدِيَهُمۡ وَأَلۡسِنَتَهُم بِٱلسُّوٓءِ وَوَدُّواْ لَوۡ تَكۡفُرُونَ

Idan suka samu nasara a kanku za su zama abokan gabanku, kuma za su miqa hannayensu da harsunansu zuwa gare ku don munanawa, sun kuma yi burin ina ma da za ku kafirta



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 3

لَن تَنفَعَكُمۡ أَرۡحَامُكُمۡ وَلَآ أَوۡلَٰدُكُمۡۚ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ يَفۡصِلُ بَيۡنَكُمۡۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Danginku da ‘ya’yanku ba za su amfana muku komai ba. A ranar alqiyama kuma za a yi hukunci a tsakaninku da su. Kuma Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 4

قَدۡ كَانَتۡ لَكُمۡ أُسۡوَةٌ حَسَنَةٞ فِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَٱلَّذِينَ مَعَهُۥٓ إِذۡ قَالُواْ لِقَوۡمِهِمۡ إِنَّا بُرَءَـٰٓؤُاْ مِنكُمۡ وَمِمَّا تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ كَفَرۡنَا بِكُمۡ وَبَدَا بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكُمُ ٱلۡعَدَٰوَةُ وَٱلۡبَغۡضَآءُ أَبَدًا حَتَّىٰ تُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ وَحۡدَهُۥٓ إِلَّا قَوۡلَ إِبۡرَٰهِيمَ لِأَبِيهِ لَأَسۡتَغۡفِرَنَّ لَكَ وَمَآ أَمۡلِكُ لَكَ مِنَ ٱللَّهِ مِن شَيۡءٖۖ رَّبَّنَا عَلَيۡكَ تَوَكَّلۡنَا وَإِلَيۡكَ أَنَبۡنَا وَإِلَيۡكَ ٱلۡمَصِيرُ

Haqiqa kyakkyawan abin koyi ya kasance a gare ku game da Ibrahimu da waxanda suke tare da shi, lokacin da suka ce da mutanensu: “Lalle mu ba ruwanmu da ku, har ma da abin da kuke bauta wa ba Allah ba, mun kafirce muku, kuma gaba da qiyayya sun bayyana a tsakaninmu da ku har abada, har sai kun yi imani da Allah Shi kaxai, in ban da faxar Ibrahimu ga babansa cewa: ‘Lalle zan nema maka gafara, ba na kuma amfana maka komai game da (sakamakon) Allah’; ya Ubangijinmu gare Ka muka dogara, kuma zuwa wurinka muka mayar da lamuranmu, kuma makoma zuwa gare Ka ne



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 5

رَبَّنَا لَا تَجۡعَلۡنَا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ وَٱغۡفِرۡ لَنَا رَبَّنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Ya Ubangijinmu, kada Ka sanya mu fitina ga waxanda suka kafirta, Ka kuma gafarta mana ya Ubangijinmu; lalle Kai ne Mabuwayi, Mai hikima.”



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 6

لَقَدۡ كَانَ لَكُمۡ فِيهِمۡ أُسۡوَةٌ حَسَنَةٞ لِّمَن كَانَ يَرۡجُواْ ٱللَّهَ وَٱلۡيَوۡمَ ٱلۡأٓخِرَۚ وَمَن يَتَوَلَّ فَإِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡغَنِيُّ ٱلۡحَمِيدُ

Haqiqa abin koyi kyakkyawa ya kasance a gare ku game da su, ga duk wanda ya kasance yana kyakkyawan fatar haxuwa da Allah da ranar lahira. Duk kuma wanda ya ba da baya, to lalle Allah Shi ne Mawadaci, Sha-Yabo



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 7

۞عَسَى ٱللَّهُ أَن يَجۡعَلَ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَ ٱلَّذِينَ عَادَيۡتُم مِّنۡهُم مَّوَدَّةٗۚ وَٱللَّهُ قَدِيرٞۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Zai yiwu Allah Ya sanya qauna tsakaninku da waxanda kuka yi gaba da su. Allah kuwa Mai ikon (yin haka) ne. Allah kuma Mai gafara ne Mai jin qai



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 8

لَّا يَنۡهَىٰكُمُ ٱللَّهُ عَنِ ٱلَّذِينَ لَمۡ يُقَٰتِلُوكُمۡ فِي ٱلدِّينِ وَلَمۡ يُخۡرِجُوكُم مِّن دِيَٰرِكُمۡ أَن تَبَرُّوهُمۡ وَتُقۡسِطُوٓاْ إِلَيۡهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُقۡسِطِينَ

Allah bai hana ku ba game da waxanda ba su yaqe ku don addini ba, ba su kuma fitar da ku daga gidajenku ba, kan ku kyautata musu, ku kuma yi musu adalci. Lalle Allah Yana son masu adalci



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 9

إِنَّمَا يَنۡهَىٰكُمُ ٱللَّهُ عَنِ ٱلَّذِينَ قَٰتَلُوكُمۡ فِي ٱلدِّينِ وَأَخۡرَجُوكُم مِّن دِيَٰرِكُمۡ وَظَٰهَرُواْ عَلَىٰٓ إِخۡرَاجِكُمۡ أَن تَوَلَّوۡهُمۡۚ وَمَن يَتَوَلَّهُمۡ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Allah kawai Yana hana ku ne a kan ku qaunaci waxanda suka yaqe ku don addini, suka kuma fitar da ku daga gidajenku, suka kuma taimaka a kan fitar da ku. Duk kuwa wanda ya qaunace su, to waxannan su ne azzalumai



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 10

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا جَآءَكُمُ ٱلۡمُؤۡمِنَٰتُ مُهَٰجِرَٰتٖ فَٱمۡتَحِنُوهُنَّۖ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِإِيمَٰنِهِنَّۖ فَإِنۡ عَلِمۡتُمُوهُنَّ مُؤۡمِنَٰتٖ فَلَا تَرۡجِعُوهُنَّ إِلَى ٱلۡكُفَّارِۖ لَا هُنَّ حِلّٞ لَّهُمۡ وَلَا هُمۡ يَحِلُّونَ لَهُنَّۖ وَءَاتُوهُم مَّآ أَنفَقُواْۚ وَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ أَن تَنكِحُوهُنَّ إِذَآ ءَاتَيۡتُمُوهُنَّ أُجُورَهُنَّۚ وَلَا تُمۡسِكُواْ بِعِصَمِ ٱلۡكَوَافِرِ وَسۡـَٔلُواْ مَآ أَنفَقۡتُمۡ وَلۡيَسۡـَٔلُواْ مَآ أَنفَقُواْۚ ذَٰلِكُمۡ حُكۡمُ ٱللَّهِ يَحۡكُمُ بَيۡنَكُمۡۖ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan muminai mata sun zo muku suna masu yin hijira, sai ku jarraba su; Allah ne Ya fi sanin imaninsu; to idan kuka san cewa su muminai ne, to kada ku mayar da su wurin kafirai; su ba halal ba ne gare su (kafirai), su ma (kafiran) ba halal ba ne a gare su; kuma ku ba su abin da suka kashe. Kuma babu laifi a kanku ku aure su idan kun ba su sadakinsu. Kada kuma ku riqe igiyar auren mata kafirai, ku tambayi abin da kuka kashe, su ma su tambayi abin da suka kashe[1]. Wannan shi ne hukuncin Allah da Yake hukuntawa a tsakaninku. Allah kuma Masani ne, Mai hikima


1- Watau duk matan da suka yi ridda suka gudu zuwa wajen kafirai, to Musulmi su nemi kafiran su biya su abin da suka kashe wajen auren su. Su ma kafiran su nemi Musulmi su biya su sadakin matansu da suka musulunta suka gudo wajen Musulmi.


Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 11

وَإِن فَاتَكُمۡ شَيۡءٞ مِّنۡ أَزۡوَٰجِكُمۡ إِلَى ٱلۡكُفَّارِ فَعَاقَبۡتُمۡ فَـَٔاتُواْ ٱلَّذِينَ ذَهَبَتۡ أَزۡوَٰجُهُم مِّثۡلَ مَآ أَنفَقُواْۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ ٱلَّذِيٓ أَنتُم بِهِۦ مُؤۡمِنُونَ

Idan wasu matanku sun guje muku zuwa ga kafirai, sai kuka yi yaqi kuka samu galaba, to ku bai wa waxanda matansu suka guje musu kamar abin da suka kashe[1]. Ku kuma ku kiyaye dokokin Allah wanda kuke imani da Shi


1- Watau daga ganimar da aka samu ta yaqi.


Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 12

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ إِذَا جَآءَكَ ٱلۡمُؤۡمِنَٰتُ يُبَايِعۡنَكَ عَلَىٰٓ أَن لَّا يُشۡرِكۡنَ بِٱللَّهِ شَيۡـٔٗا وَلَا يَسۡرِقۡنَ وَلَا يَزۡنِينَ وَلَا يَقۡتُلۡنَ أَوۡلَٰدَهُنَّ وَلَا يَأۡتِينَ بِبُهۡتَٰنٖ يَفۡتَرِينَهُۥ بَيۡنَ أَيۡدِيهِنَّ وَأَرۡجُلِهِنَّ وَلَا يَعۡصِينَكَ فِي مَعۡرُوفٖ فَبَايِعۡهُنَّ وَٱسۡتَغۡفِرۡ لَهُنَّ ٱللَّهَۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya kai wannan Annabi, idan muminai mata suka zo maka suna yi maka mubaya’a a kan ba za su yi shirka da Allah ba, kuma ba za su yi sata ba, ba kuma za su yi zina ba, kuma ba za su kashe ‘ya’yansu ba, kuma ba za su zo da wani qage ba wanda za su qirqira (game da xan da suka haifa) a tsakanin hannayensu da qafafuwansu[1], kuma ba za su sava maka ba game da wani aiki na kirki, to sai ka yi musu mubaya’a, ka kuma nema musu gafarar Allah. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai


1- Kamar yadda suke yi a jahiliyya idan mace ta yi zina da mazaje da yawa sai ta zavi xaya ta danganta masa xan da ta haifa.


Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 13

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَوَلَّوۡاْ قَوۡمًا غَضِبَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡ قَدۡ يَئِسُواْ مِنَ ٱلۡأٓخِرَةِ كَمَا يَئِسَ ٱلۡكُفَّارُ مِنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلۡقُبُورِ

Ya ku waxanda kuka yi imani, kada ku jivinci mutanen da Allah ya yi fushi da su[1], haqiqa sun xebe qauna daga lahira kamar yadda kafirai suka xebe qauna daga na qabarurruka[2]


1- Su ne Yahudawan, waxanda saboda yawan savonsu da kafircinsu har Allah ya yi fushi da su.


2- Watau bayan an nuna musu makomarsu a wutar jahannama suka fitar da tsammanin samun kuvuta a ranar alqiyama.