Sourate: Suratul Qamar

Verset : 1

ٱقۡتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلۡقَمَرُ

Alqiyama ta kusanto, wata kuma ya tsage[1]


1- Watau a zamanin Manzon Allah () wanda mushirikan Quraishawa suka gani da idonsu, bayan sun nemi ya nuna musu mu’ujiza.


Sourate: Suratul Qamar

Verset : 2

وَإِن يَرَوۡاْ ءَايَةٗ يُعۡرِضُواْ وَيَقُولُواْ سِحۡرٞ مُّسۡتَمِرّٞ

Idan kuma suka ga wata aya sai su kau da kai kuma su ce: “Wannan sihiri ne qaqqarfa.”



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 3

وَكَذَّبُواْ وَٱتَّبَعُوٓاْ أَهۡوَآءَهُمۡۚ وَكُلُّ أَمۡرٖ مُّسۡتَقِرّٞ

Suka kuma qaryata, suka bi soye-soyen zukatansu. Kowane al’amari kuwa (na alheri ko na sharri) mai tabbata ne



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 4

وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّنَ ٱلۡأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزۡدَجَرٌ

Haqiqa kuma wasu labarai waxanda tsawatarwa take cikinsu sun zo musu



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 5

حِكۡمَةُۢ بَٰلِغَةٞۖ فَمَا تُغۡنِ ٱلنُّذُرُ

Hikima ce mai kaiwa matuqa, sai dai kuma gargaxin ba ya amfanarwa



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 6

فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡۘ يَوۡمَ يَدۡعُ ٱلدَّاعِ إِلَىٰ شَيۡءٖ نُّكُرٍ

Saboda haka ka rabu da su. A ranar da mai kira[1] zai yi kira zuwa ga wani abu na qi a rai[2]


1- Shi ne Mala’ika Israfilu () mai busa a qaho.


2- Watau lokacin fitowa daga qaburbura.


Sourate: Suratul Qamar

Verset : 7

خُشَّعًا أَبۡصَٰرُهُمۡ يَخۡرُجُونَ مِنَ ٱلۡأَجۡدَاثِ كَأَنَّهُمۡ جَرَادٞ مُّنتَشِرٞ

Idanuwansu suna a qasqance suna fitowa daga qaburbura, kai ka ce su farin xango ne masu bazuwa



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 8

مُّهۡطِعِينَ إِلَى ٱلدَّاعِۖ يَقُولُ ٱلۡكَٰفِرُونَ هَٰذَا يَوۡمٌ عَسِرٞ

Suna gaggawa zuwa ga mai kiran; kafirai za su riqa cewa: “Wannan rana ce mai tsanani.”



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 9

۞كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ فَكَذَّبُواْ عَبۡدَنَا وَقَالُواْ مَجۡنُونٞ وَٱزۡدُجِرَ

Mutanen Nuhu sun qaryata kafin su (Quraishawa), sai suka qaryata Bawanmu suka kuma ce, mahaukaci ne, aka kuma kyare (shi)



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 10

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّي مَغۡلُوبٞ فَٱنتَصِرۡ

Sai ya roqi Ubangijinsa (cewa): “Lalle an fi qarfina, sai Ka taimaka.”



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 11

فَفَتَحۡنَآ أَبۡوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٖ مُّنۡهَمِرٖ

Sai Muka buxe qofofin sama da ruwa mai kwararowa



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 12

وَفَجَّرۡنَا ٱلۡأَرۡضَ عُيُونٗا فَٱلۡتَقَى ٱلۡمَآءُ عَلَىٰٓ أَمۡرٖ قَدۡ قُدِرَ

Muka kuma vuvvugar da idanuwan ruwa daga qasa, sai ruwayen suka haxu a bisa al’amarin da aka riga aka qaddara



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 13

وَحَمَلۡنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلۡوَٰحٖ وَدُسُرٖ

Muka kuma xauke shi a kan (jirgin ruwa) mai alluna da qusoshi



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 14

تَجۡرِي بِأَعۡيُنِنَا جَزَآءٗ لِّمَن كَانَ كُفِرَ

Yana gudu a kan idonmu, don ya zama sakayya ga wanda aka kafirce wa (watau Nuhu)



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 15

وَلَقَد تَّرَكۡنَٰهَآ ءَايَةٗ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun bar (abin da ya faru) ya zama aya, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 16

فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 17

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunasarwa da hadda, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 18

كَذَّبَتۡ عَادٞ فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

Adawa sun qaryata (Annabinsu), to qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 19

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ رِيحٗا صَرۡصَرٗا فِي يَوۡمِ نَحۡسٖ مُّسۡتَمِرّٖ

Lalle Mu Mun aiko musu da iska mai qarfi a ranar shu’umci mai zarcewa



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 20

تَنزِعُ ٱلنَّاسَ كَأَنَّهُمۡ أَعۡجَازُ نَخۡلٖ مُّنقَعِرٖ

Tana tumvuko mutane[1] ta kayar su, kai ka ce su kututturan dabinai ne da aka tuttunvuke


1- Watau daga doron qasa ta yi sama da su sannan ta kifo da su ta kawunansu su faxo qasa a mace.


Sourate: Suratul Qamar

Verset : 21

فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 22

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Kuma haqiqa Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 23

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ

Samudawa sun qaryata gargaxi



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 24

فَقَالُوٓاْ أَبَشَرٗا مِّنَّا وَٰحِدٗا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذٗا لَّفِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٍ

Sannan suka ce: “Yanzu mutum xaya daga cikinmu ne za mu bi? To lalle idan mun yi haka, mun tabbata cikin vata da hauka



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 25

أَءُلۡقِيَ ٱلذِّكۡرُ عَلَيۡهِ مِنۢ بَيۡنِنَا بَلۡ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٞ

“Yanzu (zai yiwu) a saukar masa da wahayi a tsakaninmu? A’a, shi dai maqaryaci ne mai tsananin girman kai.”



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 26

سَيَعۡلَمُونَ غَدٗا مَّنِ ٱلۡكَذَّابُ ٱلۡأَشِرُ

A gobe lalle za su san wane ne maqaryacin mai girman kai



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 27

إِنَّا مُرۡسِلُواْ ٱلنَّاقَةِ فِتۡنَةٗ لَّهُمۡ فَٱرۡتَقِبۡهُمۡ وَٱصۡطَبِرۡ

Lalle Mu Masu aiko taguwa ne don ta zama fitina a gare su, saboda haka ka saurara musu, kuma ka jure



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 28

وَنَبِّئۡهُمۡ أَنَّ ٱلۡمَآءَ قِسۡمَةُۢ بَيۡنَهُمۡۖ كُلُّ شِرۡبٖ مُّحۡتَضَرٞ

Kuma ka ba su labarin cewa ruwan sha an raba ne tsakaninsu (da ita taguwar); kowane akwai ranar shansa



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 29

فَنَادَوۡاْ صَاحِبَهُمۡ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ

Sai suka kirawo (shaqiyin) abokin nasu sai ya xauki (abin sara) sai ya sare ta



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 30

فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?