Sourate: Suratun Najm

Verset : 1

وَٱلنَّجۡمِ إِذَا هَوَىٰ

Na rantse da tauraro yayin da ya faxi



Sourate: Suratun Najm

Verset : 2

مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمۡ وَمَا غَوَىٰ

Mutumin naku[1] bai vata ba, kuma bai kauce hanya ba


1- Watau Annabi Muhammadu ().


Sourate: Suratun Najm

Verset : 3

وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلۡهَوَىٰٓ

Kuma ba ya yin magana bisa son rai



Sourate: Suratun Najm

Verset : 4

إِنۡ هُوَ إِلَّا وَحۡيٞ يُوحَىٰ

Shi (Alqur’ani) ba wani abu ne ba in ban da wahayi da ake yiwo (masa)



Sourate: Suratun Najm

Verset : 5

عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلۡقُوَىٰ

Mai tsananin qarfi ne (watau Jibrilu) ya koyar da shi



Sourate: Suratun Najm

Verset : 6

ذُو مِرَّةٖ فَٱسۡتَوَىٰ

Mai kyawawan halitta ne, sai ya daidaita



Sourate: Suratun Najm

Verset : 7

وَهُوَ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Alhali kuwa shi yana a sassa na can sama



Sourate: Suratun Najm

Verset : 8

ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ

Sannan sai ya kusanto, sai ya qara matsawa[1]


1- Watau Jibrilu () ya kusanto Annabi () ya matso kusa don yi masa wahayi.


Sourate: Suratun Najm

Verset : 9

فَكَانَ قَابَ قَوۡسَيۡنِ أَوۡ أَدۡنَىٰ

Sai ya kasance kamar kusancin kamu biyu ko qasa da haka



Sourate: Suratun Najm

Verset : 10

فَأَوۡحَىٰٓ إِلَىٰ عَبۡدِهِۦ مَآ أَوۡحَىٰ

Sannan (Allah) Ya yiyo wahayin abin da Ya yi wahayi zuwa ga Bawansa (Ma’aiki)



Sourate: Suratun Najm

Verset : 11

مَا كَذَبَ ٱلۡفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ

Zuciyar (ta Ma’aiki) ba ta yi qaryar abin da ta gani ba



Sourate: Suratun Najm

Verset : 12

أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ

Yanzu kwa riqa jayayya da shi kan abin da yake gani?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 13

وَلَقَدۡ رَءَاهُ نَزۡلَةً أُخۡرَىٰ

Haqiqa ya gan shi (Jibrilu) a wani karon ma[1]


1- Watau lokacin Isra’i da Mi’iraji, inda ya gan shi a halittarsa ta asali.


Sourate: Suratun Najm

Verset : 14

عِندَ سِدۡرَةِ ٱلۡمُنتَهَىٰ

A wurin Magaryar tuqewa



Sourate: Suratun Najm

Verset : 15

عِندَهَا جَنَّةُ ٱلۡمَأۡوَىٰٓ

A wurinta ne Aljannar makoma take



Sourate: Suratun Najm

Verset : 16

إِذۡ يَغۡشَى ٱلسِّدۡرَةَ مَا يَغۡشَىٰ

A yayin da abin da ya lulluve Magaryar (na ban mamaki) ya lulluve ta



Sourate: Suratun Najm

Verset : 17

مَا زَاغَ ٱلۡبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ

Ganin (nasa) bai karkace ba, kuma bai zarme ba



Sourate: Suratun Najm

Verset : 18

لَقَدۡ رَأَىٰ مِنۡ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ

Haqiqa ya ga wasu ayoyin Ubangijinsa manya-manya



Sourate: Suratun Najm

Verset : 19

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱللَّـٰتَ وَٱلۡعُزَّىٰ

Ku ba ni labarin (gumakan) Lata da Uzza



Sourate: Suratun Najm

Verset : 20

وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰٓ

Da Manata cikon ta ukunsu



Sourate: Suratun Najm

Verset : 21

أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلۡأُنثَىٰ

Yanzu xa namiji zai zama naku, Shi kuma Ya tashi da ‘ya mace?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 22

تِلۡكَ إِذٗا قِسۡمَةٞ ضِيزَىٰٓ

Idan haka ne wannan rabon na zalunci ne[1]


1- Domin ya qunshi Fifita mahaluki a kan Mahalicci.


Sourate: Suratun Najm

Verset : 23

إِنۡ هِيَ إِلَّآ أَسۡمَآءٞ سَمَّيۡتُمُوهَآ أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلۡطَٰنٍۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهۡوَى ٱلۡأَنفُسُۖ وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلۡهُدَىٰٓ

Su ba komai ba ne face sunaye da kuka sa musu, ku da iyayenku, Allah bai saukar muku da wata hujja ba game da su. Ba abin da suke bi sai zato da son zuciya. Haqiqa kuwa shiriya ta zo musu daga Ubangijinsu



Sourate: Suratun Najm

Verset : 24

أَمۡ لِلۡإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ

Ko kuwa sai mutum ya sami abin da yake buri ne?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 25

فَلِلَّهِ ٱلۡأٓخِرَةُ وَٱلۡأُولَىٰ

To lahira da duniya duka na Allah ne



Sourate: Suratun Najm

Verset : 26

۞وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ

Mala’iku nawa ne a cikin sammai cetonsu ba ya amfanar da komai sai da izinin Allah ga waxanda Ya ga dama Ya kuma yarda (da shi)?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 27

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ تَسۡمِيَةَ ٱلۡأُنثَىٰ

Lalle waxanda ba sa yin imani da ranar lahira suna kiran mala’iku da sunan mata



Sourate: Suratun Najm

Verset : 28

وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـٔٗا

Kuma ba su da wani ilimi game da haka; ba abin da suke bi sai zato; shi kuma zato, lalle ba ya wadatar da komai game da gaskiya



Sourate: Suratun Najm

Verset : 29

فَأَعۡرِضۡ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكۡرِنَا وَلَمۡ يُرِدۡ إِلَّا ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Sai ka kau da kai daga duk wanda ya ba da baya daga ambatonmu, bai kuma yi nufin komai ba sai rayuwar duniya



Sourate: Suratun Najm

Verset : 30

ذَٰلِكَ مَبۡلَغُهُم مِّنَ ٱلۡعِلۡمِۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱهۡتَدَىٰ

Wannan ne maqurar iliminsu. Lalle Ubangijinka Shi ne Ya fi sanin wanda ya vace daga hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin wanda ya shiriya