Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 1

إِنَّا فَتَحۡنَا لَكَ فَتۡحٗا مُّبِينٗا

Lalle Mu ne Muka yi maka buxi, buxi mabayyani[1]


1- Watau ya ba shi nasara ta hanyar sulhun Hudaibiyya, wata yarjejeniya da Musulmi suka qulla da Quraishawa a shekara ta shida, don tsagaita yaqi a tsakaninsu har tsawon shekara goma.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 2

لِّيَغۡفِرَ لَكَ ٱللَّهُ مَا تَقَدَّمَ مِن ذَنۢبِكَ وَمَا تَأَخَّرَ وَيُتِمَّ نِعۡمَتَهُۥ عَلَيۡكَ وَيَهۡدِيَكَ صِرَٰطٗا مُّسۡتَقِيمٗا

Don Allah Ya gafarta maka abin da ya gabata na zunubinka, da kuma wanda ya jinkirta, Ya kuma cika maka ni’imarsa, kuma Ya shiryar da kai hanya madaidaiciya



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 3

وَيَنصُرَكَ ٱللَّهُ نَصۡرًا عَزِيزًا

Allah kuma zai taimake ka da nasara mai girma



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 4

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ ٱلسَّكِينَةَ فِي قُلُوبِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ لِيَزۡدَادُوٓاْ إِيمَٰنٗا مَّعَ إِيمَٰنِهِمۡۗ وَلِلَّهِ جُنُودُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Shi ne wanda Ya sanya nutsuwa a zukatan muminai[1] don su qara imani a kan imaninsu. Rundunonin sammai da qasa kuma na Allah ne, kuma Allah Ya kasance Masani ne, Mai hikima


1- Watau bayan muminai suna ganin sharuxxan sulhun ba su yi musu daxi ba, amma Allah ya saukar musu da nutsuwa a cikin zukatansu.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 5

لِّيُدۡخِلَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَا وَيُكَفِّرَ عَنۡهُمۡ سَيِّـَٔاتِهِمۡۚ وَكَانَ ذَٰلِكَ عِندَ ٱللَّهِ فَوۡزًا عَظِيمٗا

(Ya yi haka ne) don Ya shigar da muminai maza da mata gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu suna masu dawwama a cikinsu, Ya kuma kankare musu laifukansu. Wannan kuwa ya kasance babban rabo ne a wurin Allah



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 6

وَيُعَذِّبَ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱلۡمُنَٰفِقَٰتِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ وَٱلۡمُشۡرِكَٰتِ ٱلظَّآنِّينَ بِٱللَّهِ ظَنَّ ٱلسَّوۡءِۚ عَلَيۡهِمۡ دَآئِرَةُ ٱلسَّوۡءِۖ وَغَضِبَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡ وَلَعَنَهُمۡ وَأَعَدَّ لَهُمۡ جَهَنَّمَۖ وَسَآءَتۡ مَصِيرٗا

Ya kuma azabtar da munafukai maza da mata, da mushirikai maza da mata, masu munana zato ga Allah. Mummunar azaba ta koma a kansu; kuma Allah Ya yi fushi da su, Ya kuma la’ance su, Ya kuma tanadar musu Jahannama; makoma kuwa ta munana



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 7

وَلِلَّهِ جُنُودُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَزِيزًا حَكِيمًا

Kuma rundunonin sammai da qasa na Allah ne. Allah kuwa Ya kasance Mabuwayi ne, Mai hikima



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 8

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَٰكَ شَٰهِدٗا وَمُبَشِّرٗا وَنَذِيرٗا

Lalle Mu Muka aiko ka don ka zama sheda kuma mai albishir mai gargaxi



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 9

لِّتُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَتُعَزِّرُوهُ وَتُوَقِّرُوهُۚ وَتُسَبِّحُوهُ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلًا

Don (ku mutane) ku yi imani da Allah da Manzonsa ku kuma taimake shi (wato Annabinsa), kuma ku girmama shi, ku kuma tsarkake Shi (wato Allah) safe da yamma



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ يُبَايِعُونَكَ إِنَّمَا يُبَايِعُونَ ٱللَّهَ يَدُ ٱللَّهِ فَوۡقَ أَيۡدِيهِمۡۚ فَمَن نَّكَثَ فَإِنَّمَا يَنكُثُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦۖ وَمَنۡ أَوۡفَىٰ بِمَا عَٰهَدَ عَلَيۡهُ ٱللَّهَ فَسَيُؤۡتِيهِ أَجۡرًا عَظِيمٗا

Lalle waxanda suka yi maka mubaya’a[1] Allah kawai suke yi wa mubaya’a, Hannun Allah yana saman hannayensu. To duk wanda ya warware, to kansa kawai ya warware wa, wanda kuwa ya cika abin da ya yi wa Allah alqawarinsa, to ba da daxewa ba za Mu ba shi lada mai girma


1- Su ne sahabbai dubu da xari huxu da suka yi wa Annabi () mubaya’ar yaqi a Hudaibiyya, watau Bai’atur Ridhwan.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 11

سَيَقُولُ لَكَ ٱلۡمُخَلَّفُونَ مِنَ ٱلۡأَعۡرَابِ شَغَلَتۡنَآ أَمۡوَٰلُنَا وَأَهۡلُونَا فَٱسۡتَغۡفِرۡ لَنَاۚ يَقُولُونَ بِأَلۡسِنَتِهِم مَّا لَيۡسَ فِي قُلُوبِهِمۡۚ قُلۡ فَمَن يَمۡلِكُ لَكُم مِّنَ ٱللَّهِ شَيۡـًٔا إِنۡ أَرَادَ بِكُمۡ ضَرًّا أَوۡ أَرَادَ بِكُمۡ نَفۡعَۢاۚ بَلۡ كَانَ ٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرَۢا

Waxanda suka qi fita da kai daga cikin mutanen qauye za su ce maka: “Dukiyoyinmu da iyalinmu ne suka shagaltar da mu, sai ka nema mana gafara.” Da harsunansu suna faxar abin da ba ya cikin zukatansu. Ka ce: “To wa zai amfana muku wani abu ne a wajen Allah idan Ya yi nufin ku da cutuwa, ko kuma Ya yi nufin ku da alhairi?” A’a, Allah yana sane da abin da kuka kasance kuna aikatawa



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 12

بَلۡ ظَنَنتُمۡ أَن لَّن يَنقَلِبَ ٱلرَّسُولُ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ إِلَىٰٓ أَهۡلِيهِمۡ أَبَدٗا وَزُيِّنَ ذَٰلِكَ فِي قُلُوبِكُمۡ وَظَنَنتُمۡ ظَنَّ ٱلسَّوۡءِ وَكُنتُمۡ قَوۡمَۢا بُورٗا

“A’a, ku dai kun zaci cewa Manzo da muminai ba za su komo wajen iyalinsu ba har abada, aka kuma qawata wannan a cikin zukatanku, kuka kuma yi mummunan zato, kuma kun kasance mutane halakakku.”



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 13

وَمَن لَّمۡ يُؤۡمِنۢ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ فَإِنَّآ أَعۡتَدۡنَا لِلۡكَٰفِرِينَ سَعِيرٗا

Duk kuwa wanda bai yi imani da Allah da Manzonsa ba, to lalle Mu Mun tanadi wutar Sa’ira ga kafirai



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 14

وَلِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ يَغۡفِرُ لِمَن يَشَآءُ وَيُعَذِّبُ مَن يَشَآءُۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma mulkin sammai da qasa na Allah ne. Yana yin gafara ga wanda Ya ga dama, Yana kuma azabtar da wanda Ya ga dama. Allah kuwa Ya kasance Mai gafara ne, Mai rahama



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 15

سَيَقُولُ ٱلۡمُخَلَّفُونَ إِذَا ٱنطَلَقۡتُمۡ إِلَىٰ مَغَانِمَ لِتَأۡخُذُوهَا ذَرُونَا نَتَّبِعۡكُمۡۖ يُرِيدُونَ أَن يُبَدِّلُواْ كَلَٰمَ ٱللَّهِۚ قُل لَّن تَتَّبِعُونَا كَذَٰلِكُمۡ قَالَ ٱللَّهُ مِن قَبۡلُۖ فَسَيَقُولُونَ بَلۡ تَحۡسُدُونَنَاۚ بَلۡ كَانُواْ لَا يَفۡقَهُونَ إِلَّا قَلِيلٗا

Waxanda suka qi fita tare da kai[1] za su ce, lokacin da kuka tafi zuwa wasu wuraren ganima don ku samo ta: “Ku bar mu mu bi ku”[2], suna nufin su musanya zancen Allah ne. Ka ce: “Ba za ku bi mu ba, da ma tuni haka Allah Ya faxa.” To za su ce: “A’a, kuna yi mana hassada ne kawai.” Ba haka ba ne, sun kasance ba sa fahimta ne sai ‘yan kaxan


1- Watau suka fita tare da Annabi () zuwa Makka.


2- Watau zuwa Khaibar.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 16

قُل لِّلۡمُخَلَّفِينَ مِنَ ٱلۡأَعۡرَابِ سَتُدۡعَوۡنَ إِلَىٰ قَوۡمٍ أُوْلِي بَأۡسٖ شَدِيدٖ تُقَٰتِلُونَهُمۡ أَوۡ يُسۡلِمُونَۖ فَإِن تُطِيعُواْ يُؤۡتِكُمُ ٱللَّهُ أَجۡرًا حَسَنٗاۖ وَإِن تَتَوَلَّوۡاْ كَمَا تَوَلَّيۡتُم مِّن قَبۡلُ يُعَذِّبۡكُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا

Ka ce da waxanda suka qi fita tare da kai[1] daga mutanen qauye: “Ba da daxewa ba za a kirawo ku zuwa wurin wasu mutane masu tsananin yaqi don ku yaqe su ko su musulunta. To idan kuka bi (wannan umarni), Allah zai ba ku lada kyakkyawa, idan kuwa kuka ba da baya kamar yadda kuka ba da baya a da can, zai azabtar da ku azaba mai raxaxi.”


1- Watau zuwa Makka.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 17

لَّيۡسَ عَلَى ٱلۡأَعۡمَىٰ حَرَجٞ وَلَا عَلَى ٱلۡأَعۡرَجِ حَرَجٞ وَلَا عَلَى ٱلۡمَرِيضِ حَرَجٞۗ وَمَن يُطِعِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ يُدۡخِلۡهُ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۖ وَمَن يَتَوَلَّ يُعَذِّبۡهُ عَذَابًا أَلِيمٗا

Babu wani laifi a kan makaho, babu kuma wani laifi a kan gurgu, kuma babu wani laifi a kan marar lafiya (game da rashin fita yaqi). Wanda kuwa ya bi Allah da Manzonsa to zai shigar da shi gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, wanda kuma ya ba da baya to zai azabtar da shi azaba mai raxaxi



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 18

۞لَّقَدۡ رَضِيَ ٱللَّهُ عَنِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ إِذۡ يُبَايِعُونَكَ تَحۡتَ ٱلشَّجَرَةِ فَعَلِمَ مَا فِي قُلُوبِهِمۡ فَأَنزَلَ ٱلسَّكِينَةَ عَلَيۡهِمۡ وَأَثَٰبَهُمۡ فَتۡحٗا قَرِيبٗا

Haqiqa Allah Ya yarda da muminai yayin da suke yi maka mubaya’a a qarqashin bishiyar[1] nan, to Allah Ya san abin da yake cikin zukatansu, sai Ya saukar musu da nutsuwa Ya kuma saka musu da buxi na kurkusa[2]


1- Su ne sahabban Annabi () kimanin su dubu da xari huxu da suka yi wa Manzon Allah () mubaya’a a Hudaibiyya a kan za su jajirce wajen yaqi tare da shi.


2- Watau buxe Khaibar a madadin rashin samun shiga garin Makka su yi umara.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 19

وَمَغَانِمَ كَثِيرَةٗ يَأۡخُذُونَهَاۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَزِيزًا حَكِيمٗا

Da kuma ganimomi masu yawa da za su yi ta kwasar su. Allah kuwa Ya kasance Mabuwayi ne, Mai hikima



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 20

وَعَدَكُمُ ٱللَّهُ مَغَانِمَ كَثِيرَةٗ تَأۡخُذُونَهَا فَعَجَّلَ لَكُمۡ هَٰذِهِۦ وَكَفَّ أَيۡدِيَ ٱلنَّاسِ عَنكُمۡ وَلِتَكُونَ ءَايَةٗ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ وَيَهۡدِيَكُمۡ صِرَٰطٗا مُّسۡتَقِيمٗا

Allah kuma Ya yi muku alqawarin wasu ganimomi masu yawa da za ku yi ta kwasar su, sai Ya gaggauto muku da wannan (ganimar Khaibara) Ya kuma kame muku hannayen mutanen (wato Yahudu), don kuwa (wannan) ya zama aya ga muminai, Ya kuma shiryar da su hanya madaidaiciya



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 21

وَأُخۡرَىٰ لَمۡ تَقۡدِرُواْ عَلَيۡهَا قَدۡ أَحَاطَ ٱللَّهُ بِهَاۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٗا

Xaya (ganimar) kuwa ba ku sami iko a kanta ba[1], haqiqa Allah Ya san da ita, Allah kuwa Ya kasance Mai iko ne a kan komai


1- Kamar abin da suka samu na ganimomin Farisawa da Rumawa lokacin da suka cinye su da yaqi.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 22

وَلَوۡ قَٰتَلَكُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَوَلَّوُاْ ٱلۡأَدۡبَٰرَ ثُمَّ لَا يَجِدُونَ وَلِيّٗا وَلَا نَصِيرٗا

Da kuwa waxanda suka kafirta za su yaqe ku, tabbas da sun juya da baya, sannan ba za su sami wani majivinci ko mataimaki ba



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 23

سُنَّةَ ٱللَّهِ ٱلَّتِي قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلُۖ وَلَن تَجِدَ لِسُنَّةِ ٱللَّهِ تَبۡدِيلٗا

(Wannan ita ce) sunnar Allah wadda ta riga ta gabata tun tuni; ba kuwa za ka tava samun canji ba game da sunnar Allah



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 24

وَهُوَ ٱلَّذِي كَفَّ أَيۡدِيَهُمۡ عَنكُمۡ وَأَيۡدِيَكُمۡ عَنۡهُم بِبَطۡنِ مَكَّةَ مِنۢ بَعۡدِ أَنۡ أَظۡفَرَكُمۡ عَلَيۡهِمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرًا

Shi ne kuma Wanda Ya kame muku hannayensu[1], kuma (Ya kame) musu hannayenku a cikin Makka bayan kuwa Ya riga ya ba ku nasara a kansu. Allah kuma Ya zamanto Mai ganin abin da kuke aikatawa ne


1- Watau yayin da mayaqa mutum tamanin suka nufo su da Hudaibiyya da niyyar cutar da su.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 25

هُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَصَدُّوكُمۡ عَنِ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ وَٱلۡهَدۡيَ مَعۡكُوفًا أَن يَبۡلُغَ مَحِلَّهُۥۚ وَلَوۡلَا رِجَالٞ مُّؤۡمِنُونَ وَنِسَآءٞ مُّؤۡمِنَٰتٞ لَّمۡ تَعۡلَمُوهُمۡ أَن تَطَـُٔوهُمۡ فَتُصِيبَكُم مِّنۡهُم مَّعَرَّةُۢ بِغَيۡرِ عِلۡمٖۖ لِّيُدۡخِلَ ٱللَّهُ فِي رَحۡمَتِهِۦ مَن يَشَآءُۚ لَوۡ تَزَيَّلُواْ لَعَذَّبۡنَا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡهُمۡ عَذَابًا أَلِيمًا

Su ne waxanda suka kafirta suka kuma hana ku isa ga Masallaci mai alfarma, suka kuma hana dabbobin hadaya isa wurin yankansu. Kuma ba don wasu mazaje muminai da wasu mataye muminai da ba ku san su ba, don kada ku kashe su, sannan wani laifi nasu ya same ku ba tare da sani ba, (da Ya ba ku damar yaqar su. Wannan ya faru ne) don Allah Ya shigar da wanda Ya ga dama cikin rahamarsa. Da sun ware to lalle da Mun azabtar da waxanda suka kafirta daga cikinsu azaba mai tsanani



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 26

إِذۡ جَعَلَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي قُلُوبِهِمُ ٱلۡحَمِيَّةَ حَمِيَّةَ ٱلۡجَٰهِلِيَّةِ فَأَنزَلَ ٱللَّهُ سَكِينَتَهُۥ عَلَىٰ رَسُولِهِۦ وَعَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَأَلۡزَمَهُمۡ كَلِمَةَ ٱلتَّقۡوَىٰ وَكَانُوٓاْ أَحَقَّ بِهَا وَأَهۡلَهَاۚ وَكَانَ ٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٗا

Yayin da waxanda suka kafirta suka sanya kishi irin kishin jahiliyya a cikin zukatansu, sai Allah Ya saukar da nutsuwarsa ga Manzonsa da muminai, Ya kuma kimsa musu kalmar imani[1], da ma kuma su suka fi cancantarta, kuma (su ne) masu ita. Allah kuma Ya kasance Masanin komai ne


1- Watau kalmar shahada.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 27

لَّقَدۡ صَدَقَ ٱللَّهُ رَسُولَهُ ٱلرُّءۡيَا بِٱلۡحَقِّۖ لَتَدۡخُلُنَّ ٱلۡمَسۡجِدَ ٱلۡحَرَامَ إِن شَآءَ ٱللَّهُ ءَامِنِينَ مُحَلِّقِينَ رُءُوسَكُمۡ وَمُقَصِّرِينَ لَا تَخَافُونَۖ فَعَلِمَ مَا لَمۡ تَعۡلَمُواْ فَجَعَلَ مِن دُونِ ذَٰلِكَ فَتۡحٗا قَرِيبًا

Haqiqa Allah Ya tabbatar wa Manzonsa gaskiyar mafarkin cewa, lalle za ku shiga Masallaci mai alfarma insha Allahu, kuna cikin aminci kuna masu aske kawunanku da masu yin saisaye, ba tare da kuna jin tsoron (komai) ba, to Ya san abin da ba ku sani ba, sai Ya sanya buxi na kusa[1] kafin wannan


1- Watau sulhul Hudaibiyya da buxe Khaibar.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 28

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ رَسُولَهُۥ بِٱلۡهُدَىٰ وَدِينِ ٱلۡحَقِّ لِيُظۡهِرَهُۥ عَلَى ٱلدِّينِ كُلِّهِۦۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ شَهِيدٗا

Shi ne Wanda Ya aiko Manzonsa da shiriya da kuma addini na gaskiya don Ya xora shi a kan kowane addini. Allah kuma Ya isa Mai shaida



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 29

مُّحَمَّدٞ رَّسُولُ ٱللَّهِۚ وَٱلَّذِينَ مَعَهُۥٓ أَشِدَّآءُ عَلَى ٱلۡكُفَّارِ رُحَمَآءُ بَيۡنَهُمۡۖ تَرَىٰهُمۡ رُكَّعٗا سُجَّدٗا يَبۡتَغُونَ فَضۡلٗا مِّنَ ٱللَّهِ وَرِضۡوَٰنٗاۖ سِيمَاهُمۡ فِي وُجُوهِهِم مِّنۡ أَثَرِ ٱلسُّجُودِۚ ذَٰلِكَ مَثَلُهُمۡ فِي ٱلتَّوۡرَىٰةِۚ وَمَثَلُهُمۡ فِي ٱلۡإِنجِيلِ كَزَرۡعٍ أَخۡرَجَ شَطۡـَٔهُۥ فَـَٔازَرَهُۥ فَٱسۡتَغۡلَظَ فَٱسۡتَوَىٰ عَلَىٰ سُوقِهِۦ يُعۡجِبُ ٱلزُّرَّاعَ لِيَغِيظَ بِهِمُ ٱلۡكُفَّارَۗ وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ مِنۡهُم مَّغۡفِرَةٗ وَأَجۡرًا عَظِيمَۢا

Muhammadu Manzon Allah ne. Waxanda kuma suke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, kuma masu tausayin junansu ne; za ka gan su suna ruku’i suna sujjada suna neman falala daga Allah da yardarsa; alamominsu na gurbin sujjada suna bayyana a fuskokinsu. Wannan shi ne misalinsu a cikin Attaura. Misalinsu kuwa a cikin Linjila kamar shuka ce da ta fitar da reshenta sai ya qarfafe ta, sannan ta yi kauri sai ta daidaita a kan tushiyarta ta riqa qayatar da manoma, don Ya cusa wa kafirai haushi. Allah Ya yi wa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari daga cikinsu alqawarin gafara da lada mai girma