Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 1

حمٓ

HA MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 2

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Saukar da Alqur’ani daga Allah ne Mabuwayi, Mai hikima



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 3

إِنَّ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ لَأٓيَٰتٖ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle a cikin sammai da qasa tabbas akwai ayoyi ga muminai



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 4

وَفِي خَلۡقِكُمۡ وَمَا يَبُثُّ مِن دَآبَّةٍ ءَايَٰتٞ لِّقَوۡمٖ يُوقِنُونَ

A cikin halittarku ma da abin da Yake bazawa na dabbobi, akwai ayoyi ga mutane masu sakankancewa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 5

وَٱخۡتِلَٰفِ ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ وَمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مِن رِّزۡقٖ فَأَحۡيَا بِهِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَا وَتَصۡرِيفِ ٱلرِّيَٰحِ ءَايَٰتٞ لِّقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Da kuma sassavawar dare da yini da abin da Ya saukar daga sama na arziki, sai Ya raya qasa da shi bayan mutuwarta, da kuma jujjuyawar iska, akwai ayoyi ga mutanen da suke hankalta



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 6

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱللَّهِ نَتۡلُوهَا عَلَيۡكَ بِٱلۡحَقِّۖ فَبِأَيِّ حَدِيثِۭ بَعۡدَ ٱللَّهِ وَءَايَٰتِهِۦ يُؤۡمِنُونَ

Waxannan su ne ayoyin Allah da Muke karanta maka su da gaskiya; to da wane zance ne za su yi imani bayan (zancen) Allah da ayoyinsa?



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 7

وَيۡلٞ لِّكُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٖ

Tsananin azaba ya tabbata ga duk wani maqaryaci mai yawan savo



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 8

يَسۡمَعُ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ثُمَّ يُصِرُّ مُسۡتَكۡبِرٗا كَأَن لَّمۡ يَسۡمَعۡهَاۖ فَبَشِّرۡهُ بِعَذَابٍ أَلِيمٖ

Yana jin ana karanta masa ayoyin Allah, sai ya doge yana mai girman kai kamar bai ji su ba; to ka yi masa albishir da azaba mai raxaxi



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 9

وَإِذَا عَلِمَ مِنۡ ءَايَٰتِنَا شَيۡـًٔا ٱتَّخَذَهَا هُزُوًاۚ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٞ مُّهِينٞ

Idan kuma ya san wani abu daga ayoyinmu sai ya xauke su abin yi wa izgili. Waxannan suna da wata azaba mai wulaqantarwa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 10

مِّن وَرَآئِهِمۡ جَهَنَّمُۖ وَلَا يُغۡنِي عَنۡهُم مَّا كَسَبُواْ شَيۡـٔٗا وَلَا مَا ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِ ٱللَّهِ أَوۡلِيَآءَۖ وَلَهُمۡ عَذَابٌ عَظِيمٌ

A gabansu akwai (wutar) Jahannama, kuma abin da suka tsuwurwurta (na dukiya da waninta), da abubuwan da suka riqa majivinta ba Allah ba, (duk) ba za su amfana musu komai ba; suna kuma da (sakamakon) azaba mai girma



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 11

هَٰذَا هُدٗىۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِمۡ لَهُمۡ عَذَابٞ مِّن رِّجۡزٍ أَلِيمٌ

Wannan (Alqur’ani) shiriya ne; waxanda kuwa suka kafirce da ayoyin Ubangijinsu, suna da (sakamakon) wata mummunar azaba mai raxaxi



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 12

۞ٱللَّهُ ٱلَّذِي سَخَّرَ لَكُمُ ٱلۡبَحۡرَ لِتَجۡرِيَ ٱلۡفُلۡكُ فِيهِ بِأَمۡرِهِۦ وَلِتَبۡتَغُواْ مِن فَضۡلِهِۦ وَلَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Allah ne wanda Ya hore muku kogi don jiragen ruwa su riqa gudu a cikinsa da umarninsa, don kuma ku nema daga falalarsa don kuma ku gode



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 13

وَسَخَّرَ لَكُم مَّا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا مِّنۡهُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يَتَفَكَّرُونَ

Ya kuma hore muku abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa gaba xayansu daga gare Shi. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutanen da suke yin tunani



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 14

قُل لِّلَّذِينَ ءَامَنُواْ يَغۡفِرُواْ لِلَّذِينَ لَا يَرۡجُونَ أَيَّامَ ٱللَّهِ لِيَجۡزِيَ قَوۡمَۢا بِمَا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ

Ka ce da waxanda suka yi imani su yi gafara ga waxanda ba su damu da ni’imomi ko musibu na Allah ba[1], don Ya saka wa mutane game da irin abin da suka kasance suna aikatawa


1- Watau domin Allah zai saka wa bayinsa muminai masu haquri.


Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 15

مَنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا فَلِنَفۡسِهِۦۖ وَمَنۡ أَسَآءَ فَعَلَيۡهَاۖ ثُمَّ إِلَىٰ رَبِّكُمۡ تُرۡجَعُونَ

Duk wanda ya yi aiki nagari to kansa ya yi wa; wanda kuma duk ya munana to a kansa; sannan wurin Ubangijinku ne kawai za a mayar da ku



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 16

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحُكۡمَ وَٱلنُّبُوَّةَ وَرَزَقۡنَٰهُم مِّنَ ٱلطَّيِّبَٰتِ وَفَضَّلۡنَٰهُمۡ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Haqiqa kuma Mun bai wa Banu Isra’ila littafin (Attaura) da hukunci da annabta. Muka kuma arzuta su da tsarkakan (abubuwa), kuma Muka fifita su a kan talikai



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 17

وَءَاتَيۡنَٰهُم بَيِّنَٰتٖ مِّنَ ٱلۡأَمۡرِۖ فَمَا ٱخۡتَلَفُوٓاْ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَهُمُ ٱلۡعِلۡمُ بَغۡيَۢا بَيۡنَهُمۡۚ إِنَّ رَبَّكَ يَقۡضِي بَيۡنَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فِيمَا كَانُواْ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَ

Muka kuma kawo musu (hujjoji) mabayyana na addini; to ba su sassava ba, sai bayan da ilimi ya zo musu don hassada a tsakaninsu. Lalle Ubangijinka zai yi hukunci a tsakaninsu a ranar alqiyama game da abin da suka kasance suna yin savani cikinsa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 18

ثُمَّ جَعَلۡنَٰكَ عَلَىٰ شَرِيعَةٖ مِّنَ ٱلۡأَمۡرِ فَٱتَّبِعۡهَا وَلَا تَتَّبِعۡ أَهۡوَآءَ ٱلَّذِينَ لَا يَعۡلَمُونَ

Sannan Muka sanya ka a kan wata shari’a ta addini, to sai ka bi ta, kada kuma ka bi soye-soyen zukatan waxanda ba sa sanin (gaskiya)



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 19

إِنَّهُمۡ لَن يُغۡنُواْ عَنكَ مِنَ ٱللَّهِ شَيۡـٔٗاۚ وَإِنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ بَعۡضُهُمۡ أَوۡلِيَآءُ بَعۡضٖۖ وَٱللَّهُ وَلِيُّ ٱلۡمُتَّقِينَ

Lalle su ba za su maganta maka komai ba daga Allah. Kuma lalle azzalumai sashinsu masoya sashi ne; Allah kuwa Shi ne Majivincin al’amarin masu taqawa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 20

هَٰذَا بَصَـٰٓئِرُ لِلنَّاسِ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٞ لِّقَوۡمٖ يُوقِنُونَ

Wannan (Alqur’ani) izina ne ga mutane da shiriya da rahama ga mutanen da suke sakankancewa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 21

أَمۡ حَسِبَ ٱلَّذِينَ ٱجۡتَرَحُواْ ٱلسَّيِّـَٔاتِ أَن نَّجۡعَلَهُمۡ كَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ سَوَآءٗ مَّحۡيَاهُمۡ وَمَمَاتُهُمۡۚ سَآءَ مَا يَحۡكُمُونَ

Yanzu waxanda suka aikata munanan (ayyuka) suna tsammanin za Mu sanya su ne kamar waxanda suka yi imani suka kuma yi kyawawan ayyuka, ya zamana rayuwarsu ta duniya da mutuwarsu sun zama daidai? Abin da suke hukuntawa ya munana



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 22

وَخَلَقَ ٱللَّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّ وَلِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Allah kuma Ya halicci sammai da qasa da gaskiya, don kuma a saka wa kowane rai irin abin da ya aikata, alhali kuma su ba za a zalunce su ba



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 23

أَفَرَءَيۡتَ مَنِ ٱتَّخَذَ إِلَٰهَهُۥ هَوَىٰهُ وَأَضَلَّهُ ٱللَّهُ عَلَىٰ عِلۡمٖ وَخَتَمَ عَلَىٰ سَمۡعِهِۦ وَقَلۡبِهِۦ وَجَعَلَ عَلَىٰ بَصَرِهِۦ غِشَٰوَةٗ فَمَن يَهۡدِيهِ مِنۢ بَعۡدِ ٱللَّهِۚ أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

Shin kuwa ka ga wanda ya xauki son zuciyarsa (shi ne) abin bautarsa, Allah kuwa Ya vatar da shi a kan yana sane[1], Ya kuma rufe jinsa da zuciyarsa, kuma Ya sanya yana a kan ganinsa, to wane ne zai shiryar da shi in ba Allah ba? Me ya sa ba kwa wa’azantuwa?


1- Watau ya vatar da shi bayan ilimi ya zo masa, saboda Allah ya san cewa ya cancanci vata.


Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 24

وَقَالُواْ مَا هِيَ إِلَّا حَيَاتُنَا ٱلدُّنۡيَا نَمُوتُ وَنَحۡيَا وَمَا يُهۡلِكُنَآ إِلَّا ٱلدَّهۡرُۚ وَمَا لَهُم بِذَٰلِكَ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِنۡ هُمۡ إِلَّا يَظُنُّونَ

Suka kuma ce: “Ai ba wata (rayuwa) sai rayuwarmu ta duniya, da za mu mutu, kuma mu rayu (watau ‘ya’yansu)[1], ba kuwa wani abu da yake hallaka mu sai juyin zamani”. Alhali kuwa ba su da wani sani game da wannan; ba abin da suke yi sai zato


1- Watau bayan sun mutu ‘ya’yansu za su ci gaba da rayuwa.


Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 25

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ مَّا كَانَ حُجَّتَهُمۡ إِلَّآ أَن قَالُواْ ٱئۡتُواْ بِـَٔابَآئِنَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu mabayyana, ba su da wata hujja sai kawai su ce: “Ku zo da iyayenmu idan kun kasance masu gaskiya.”



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 26

قُلِ ٱللَّهُ يُحۡيِيكُمۡ ثُمَّ يُمِيتُكُمۡ ثُمَّ يَجۡمَعُكُمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ لَا رَيۡبَ فِيهِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Ka ce: “Allah ne zai raya ku sannan ya kashe ku sannan ya tara ku a ranar alqiyama wadda babu kokwanto game da ita, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (haka).”



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 27

وَلِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ يَوۡمَئِذٖ يَخۡسَرُ ٱلۡمُبۡطِلُونَ

Mulkin sammai da qasa kuma na Allah ne. Kuma ranar da alqiyama za ta tashi, a wannan ranar mavarnata za su yi asara



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 28

وَتَرَىٰ كُلَّ أُمَّةٖ جَاثِيَةٗۚ كُلُّ أُمَّةٖ تُدۡعَىٰٓ إِلَىٰ كِتَٰبِهَا ٱلۡيَوۡمَ تُجۡزَوۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Za kuma ka ga kowace al’umma a durqushe, kowace al’umma ana kiran ta zuwa ga littafinta, a wannan rana ne za a saka muku abin da kuka kasance kuna aikatawa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 29

هَٰذَا كِتَٰبُنَا يَنطِقُ عَلَيۡكُم بِٱلۡحَقِّۚ إِنَّا كُنَّا نَسۡتَنسِخُ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

(Za a ce da su): “Wannan Littafinmu ne da yake yi muku furuci da gaskiya[1]. Lalle Mu mun kasance Muna rubuta abin da kuka kasance kuna aikatawa[2].”


1- Watau littafin da mala’iku suka rubuta na ayyukansu yana ba da shaida a kansu da tsantsar gaskiya.


2- Domin Allah ne da kansa ya umarci waxannan mala’ikun su riqa rubuta ayyukan mutane a duniya.


Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 30

فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَيُدۡخِلُهُمۡ رَبُّهُمۡ فِي رَحۡمَتِهِۦۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡمُبِينُ

To amma waxanda suka yi imani suka yi ayyuka nagari, to Ubangijinsu zai shigar da su cikin rahamarsa. Wannan shi ne rabo mabayyani