Sourate: Suratus Shura

Verset : 1

حمٓ

HA MIM



Sourate: Suratus Shura

Verset : 2

عٓسٓقٓ

AIN SIN QAF[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Sourate: Suratus Shura

Verset : 3

كَذَٰلِكَ يُوحِيٓ إِلَيۡكَ وَإِلَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكَ ٱللَّهُ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Kamar haka ne Allah Mabuwayi, Mai hikima Yake yi maka wahayi da kuma waxanda suka gabace ka



Sourate: Suratus Shura

Verset : 4

لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلۡعَلِيُّ ٱلۡعَظِيمُ

Abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa nasa ne; kuma Shi Maxaukaki ne, Mai girma



Sourate: Suratus Shura

Verset : 5

تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِن فَوۡقِهِنَّۚ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يُسَبِّحُونَ بِحَمۡدِ رَبِّهِمۡ وَيَسۡتَغۡفِرُونَ لِمَن فِي ٱلۡأَرۡضِۗ أَلَآ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Sammai suna neman su tsattsage ta samansu (don girmansa). Mala’iku kuma suna yin tasbihi da yabon Ubangijinsu, suna kuma neman gafara ga waxanda suke cikin qasa. Ku saurara, Lalle Allah Shi ne Mai gafara, Mai rahama



Sourate: Suratus Shura

Verset : 6

وَٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ ٱللَّهُ حَفِيظٌ عَلَيۡهِمۡ وَمَآ أَنتَ عَلَيۡهِم بِوَكِيلٖ

Waxanda kuwa suka riqi wasu majivinta ba shi ba, Allah Mai kiyaye da su ne, kai kuma ba wakili ne ba a kansu



Sourate: Suratus Shura

Verset : 7

وَكَذَٰلِكَ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ قُرۡءَانًا عَرَبِيّٗا لِّتُنذِرَ أُمَّ ٱلۡقُرَىٰ وَمَنۡ حَوۡلَهَا وَتُنذِرَ يَوۡمَ ٱلۡجَمۡعِ لَا رَيۡبَ فِيهِۚ فَرِيقٞ فِي ٱلۡجَنَّةِ وَفَرِيقٞ فِي ٱلسَّعِيرِ

Kuma kamar haka Muka yiwo maka wahayin Alqur’ani Balarabe, don ka gargaxi mutanen Makka da waxanda suke kewaye da ita (watau duniya baki xaya), ka kuma yi gargaxin ranar taruwa da babu kokwanto a game da ita. Wata qungiya tana cikin Aljanna, wata qungiya kuma tana cikin wutar Sa’ira



Sourate: Suratus Shura

Verset : 8

وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَجَعَلَهُمۡ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ وَلَٰكِن يُدۡخِلُ مَن يَشَآءُ فِي رَحۡمَتِهِۦۚ وَٱلظَّـٰلِمُونَ مَا لَهُم مِّن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٍ

Da kuma Allah Ya ga dama da Ya sanya su al’umma xaya (watau a kan addini xaya), sai dai kuma Yana shigar da wanda Ya ga dama cikin rahamarsa. Azzalumai kuma ba su da wani majivinci ko wani mataimaki



Sourate: Suratus Shura

Verset : 9

أَمِ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَۖ فَٱللَّهُ هُوَ ٱلۡوَلِيُّ وَهُوَ يُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Ko dai sun riqi wasu majivinta ne ba Shi ba. To Allah Shi ne Majivinci, Shi ne kuma Yake raya matattu, Shi kuma Mai iko ne a kan komai



Sourate: Suratus Shura

Verset : 10

وَمَا ٱخۡتَلَفۡتُمۡ فِيهِ مِن شَيۡءٖ فَحُكۡمُهُۥٓ إِلَى ٱللَّهِۚ ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبِّي عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُ وَإِلَيۡهِ أُنِيبُ

Kuma duk wani abu da kuka yi savani a kansa, to sai ku mai da hukuncinsa ga Allah. Wannan Shi ne Allah Ubangijina, gare Shi kawai na dogara, kuma wurinsa kawai nake mayar da al’amarina



Sourate: Suratus Shura

Verset : 11

فَاطِرُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ جَعَلَ لَكُم مِّنۡ أَنفُسِكُمۡ أَزۡوَٰجٗا وَمِنَ ٱلۡأَنۡعَٰمِ أَزۡوَٰجٗا يَذۡرَؤُكُمۡ فِيهِۚ لَيۡسَ كَمِثۡلِهِۦ شَيۡءٞۖ وَهُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡبَصِيرُ

(Shi ne) Mahaliccin sammai da qasa. Ya halitta muku mataye daga jinsinku, daga dabbobi ma (Ya halicce su) maza da mata; Yana yaxa ku ta hanyarsa (haxin jinsin biyu). Babu wani abu da ya yi kama da Shi[1]; kuma Shi Mai ji ne, Mai gani


1- Watau ba ya da mai kama da shi a Zatinsa da siffofinsa da sunayensa da ayyukansa.


Sourate: Suratus Shura

Verset : 12

لَهُۥ مَقَالِيدُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ وَيَقۡدِرُۚ إِنَّهُۥ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Mabuxan taskokin sammai da qasa nasa ne; Yana shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama, yana kuma quntatawa. Lalle shi Masanin komai ne



Sourate: Suratus Shura

Verset : 13

۞شَرَعَ لَكُم مِّنَ ٱلدِّينِ مَا وَصَّىٰ بِهِۦ نُوحٗا وَٱلَّذِيٓ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ وَمَا وَصَّيۡنَا بِهِۦٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ وَعِيسَىٰٓۖ أَنۡ أَقِيمُواْ ٱلدِّينَ وَلَا تَتَفَرَّقُواْ فِيهِۚ كَبُرَ عَلَى ٱلۡمُشۡرِكِينَ مَا تَدۡعُوهُمۡ إِلَيۡهِۚ ٱللَّهُ يَجۡتَبِيٓ إِلَيۡهِ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِيٓ إِلَيۡهِ مَن يُنِيبُ

Ya shar’anta muku (irin) abin da Ya yi wa Nuhu wahayi da shi na addini, da kuma wanda Muka yiwo maka wahayinsa, da kuma abin da Muka yi wa Ibrahimu da Musa da Isa wasiyya da shi cewa: “Ku tsayar da addini, kuma kada ku rarraba a cikinsa.” Abin da kake kiran kafirai zuwa gare shi ya yi musu nauyi. Allah Yana zavar wanda Ya ga dama zuwa gare shi (addini) Yana kuma shiryar da wanda Ya mayar da al’amarinsa zuwa gare Shi



Sourate: Suratus Shura

Verset : 14

وَمَا تَفَرَّقُوٓاْ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَهُمُ ٱلۡعِلۡمُ بَغۡيَۢا بَيۡنَهُمۡۚ وَلَوۡلَا كَلِمَةٞ سَبَقَتۡ مِن رَّبِّكَ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗى لَّقُضِيَ بَيۡنَهُمۡۚ وَإِنَّ ٱلَّذِينَ أُورِثُواْ ٱلۡكِتَٰبَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡ لَفِي شَكّٖ مِّنۡهُ مُرِيبٖ

Ba su kuma rarrabu ba sai bayan ilimi ya zo musu don zalunci da ke tsakaninsu. Ba don kalmar da ta riga ta gabata daga Ubangijinka ba (ta jinkirta musu) zuwa ga wani lokaci qayyadajje, da lalle an yi hukunci tsakaninsu. Kuma lalle waxanda aka gadar wa da littafi a bayansu lallai suna cikin shakka mai sa kokwanto game da shi (Annabi Muhammadu)



Sourate: Suratus Shura

Verset : 15

فَلِذَٰلِكَ فَٱدۡعُۖ وَٱسۡتَقِمۡ كَمَآ أُمِرۡتَۖ وَلَا تَتَّبِعۡ أَهۡوَآءَهُمۡۖ وَقُلۡ ءَامَنتُ بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ مِن كِتَٰبٖۖ وَأُمِرۡتُ لِأَعۡدِلَ بَيۡنَكُمُۖ ٱللَّهُ رَبُّنَا وَرَبُّكُمۡۖ لَنَآ أَعۡمَٰلُنَا وَلَكُمۡ أَعۡمَٰلُكُمۡۖ لَا حُجَّةَ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكُمُۖ ٱللَّهُ يَجۡمَعُ بَيۡنَنَاۖ وَإِلَيۡهِ ٱلۡمَصِيرُ

Saboda wannan sai ka yi kira (zuwa ga addinin Allah), kuma ka tsaya kyam kamar yadda aka umarce ka, kada ka bi son ransu; ka kuma ce: “Na yi imani da abin da Allah Ya saukar na littattafai; an kuma umarce ni da yin adalci a tsakaninku; Allah ne Ubangijinmu kuma Ubangijinku; (sakamakon) ayyukanmu namu ne, ku ma (sakamakon) ayyukanku naku ne; babu wata jayayya a tsakaninmu da ku; Allah zai tara mu; kuma zuwa gare Shi ne kaxai makoma



Sourate: Suratus Shura

Verset : 16

وَٱلَّذِينَ يُحَآجُّونَ فِي ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مَا ٱسۡتُجِيبَ لَهُۥ حُجَّتُهُمۡ دَاحِضَةٌ عِندَ رَبِّهِمۡ وَعَلَيۡهِمۡ غَضَبٞ وَلَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدٌ

Waxanda kuma suke jayayya game da Allah bayan an amsa masa (kiransa), to hujjarsu vatacciya ce a wurin Ubangijinsu, kuma fushi ya hau kansu, kuma suna da azaba mai tsanani



Sourate: Suratus Shura

Verset : 17

ٱللَّهُ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ وَٱلۡمِيزَانَۗ وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّ ٱلسَّاعَةَ قَرِيبٞ

Allah ne Ya saukar da Littafi da gaskiya da kuma adalci. Me yake sanar da kai cewa ko alqiyama kusa take



Sourate: Suratus Shura

Verset : 18

يَسۡتَعۡجِلُ بِهَا ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِهَاۖ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مُشۡفِقُونَ مِنۡهَا وَيَعۡلَمُونَ أَنَّهَا ٱلۡحَقُّۗ أَلَآ إِنَّ ٱلَّذِينَ يُمَارُونَ فِي ٱلسَّاعَةِ لَفِي ضَلَٰلِۭ بَعِيدٍ

Waxanda ba sa yin imani da ita suna gaggauto da ita; waxanda kuwa suka yi imani a tsorace suke da ita, kuma suna sane da cewa ita gaskiya ce. Ku saurara, lalle waxanda suke jayayya game da tashin alqiyama tabbas suna cikin vata mai nisa



Sourate: Suratus Shura

Verset : 19

ٱللَّهُ لَطِيفُۢ بِعِبَادِهِۦ يَرۡزُقُ مَن يَشَآءُۖ وَهُوَ ٱلۡقَوِيُّ ٱلۡعَزِيزُ

Allah Mai tausasa wa bayinsa ne, Yana arzuta wanda ya ga dama; kuma Shi Qaqqarfa ne, Mabuwayi



Sourate: Suratus Shura

Verset : 20

مَن كَانَ يُرِيدُ حَرۡثَ ٱلۡأٓخِرَةِ نَزِدۡ لَهُۥ فِي حَرۡثِهِۦۖ وَمَن كَانَ يُرِيدُ حَرۡثَ ٱلدُّنۡيَا نُؤۡتِهِۦ مِنۡهَا وَمَا لَهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ مِن نَّصِيبٍ

Wanda ya kasance yana nufin ladan lahira to za Mu qara masa a kan ladansa; wanda kuwa ya kasance yana nufin ladan duniya to za Mu ba shi (wani abu) daga gare ta, kuma ba shi da wani rabo a lahira



Sourate: Suratus Shura

Verset : 21

أَمۡ لَهُمۡ شُرَكَـٰٓؤُاْ شَرَعُواْ لَهُم مِّنَ ٱلدِّينِ مَا لَمۡ يَأۡذَنۢ بِهِ ٱللَّهُۚ وَلَوۡلَا كَلِمَةُ ٱلۡفَصۡلِ لَقُضِيَ بَيۡنَهُمۡۗ وَإِنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Ko dai suna da wasu abokan tarayya ne da suka shar’anta musu wani abu na addini wanda Allah bai yi izinin yin sa ba? Ba don kalmar yin hukunci (a lahira) ta tabbata ba, da lalle an yi hukunci a tsakaninsu (tun a duniya). Lalle kuma azzalumai suna da azaba mai raxaxi



Sourate: Suratus Shura

Verset : 22

تَرَى ٱلظَّـٰلِمِينَ مُشۡفِقِينَ مِمَّا كَسَبُواْ وَهُوَ وَاقِعُۢ بِهِمۡۗ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فِي رَوۡضَاتِ ٱلۡجَنَّاتِۖ لَهُم مَّا يَشَآءُونَ عِندَ رَبِّهِمۡۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَضۡلُ ٱلۡكَبِيرُ

Za ka ga azzalumai suna tsoron sakamakon abin da suka aikata, alhali kuwa ga shi zai faxa musu. Waxanda kuwa suka yi imani suka kuma yi aiki nagari, to suna cikin dausayoyin gidajen Aljanna; suna samun duk abin da suka ga dama a wurin Ubangijinsu. Wannan ita ce falala mai girma



Sourate: Suratus Shura

Verset : 23

ذَٰلِكَ ٱلَّذِي يُبَشِّرُ ٱللَّهُ عِبَادَهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِۗ قُل لَّآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ أَجۡرًا إِلَّا ٱلۡمَوَدَّةَ فِي ٱلۡقُرۡبَىٰۗ وَمَن يَقۡتَرِفۡ حَسَنَةٗ نَّزِدۡ لَهُۥ فِيهَا حُسۡنًاۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ شَكُورٌ

Wannan fa shi ne abin da Allah Yake yin albishir da shi ga bayinsa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari. Ka ce: “Ba na tambayar ku wani lada a kansa (isar da saqon), sai dai kawai soyayya ta zumunta”. Duk wanda ya aikata wani aiki kyakkyawa za Mu qara masa kyakkyawan sakamako a kansa. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai godiya



Sourate: Suratus Shura

Verset : 24

أَمۡ يَقُولُونَ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبٗاۖ فَإِن يَشَإِ ٱللَّهُ يَخۡتِمۡ عَلَىٰ قَلۡبِكَۗ وَيَمۡحُ ٱللَّهُ ٱلۡبَٰطِلَ وَيُحِقُّ ٱلۡحَقَّ بِكَلِمَٰتِهِۦٓۚ إِنَّهُۥ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

A’a, suna dai cewa ya qaga wa Allah qarya ne; to da Allah Ya ga dama da sai Ya rufe zuciyarka[1]. Allah kuma Yana shafe qarya Yana kuma tabbatar da gaskiya da kalmominsa. Lalle Shi Masanin abubuwan da suke cikin zukata ne


1- Watau da a ce zuciyarsa ta riya masa ya qirqiri Alqur’ani da kansa ya jingina wa Allah, to da Allah ya toshe masa zuciyarsa yadda ba zai qara fahimtar komai ba.


Sourate: Suratus Shura

Verset : 25

وَهُوَ ٱلَّذِي يَقۡبَلُ ٱلتَّوۡبَةَ عَنۡ عِبَادِهِۦ وَيَعۡفُواْ عَنِ ٱلسَّيِّـَٔاتِ وَيَعۡلَمُ مَا تَفۡعَلُونَ

Shi ne kuma wanda Yake karvar tuba daga bayinsa, Yake kuma yin afuwa game da munanan (ayyuka), Yana kuma sane da abin da kuke aikatawa



Sourate: Suratus Shura

Verset : 26

وَيَسۡتَجِيبُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَيَزِيدُهُم مِّن فَضۡلِهِۦۚ وَٱلۡكَٰفِرُونَ لَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدٞ

Kuma Yana amsa wa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, Yana kuma qara musu daga falalarsa. Kafirai kuwa suna da azaba mai tsanani



Sourate: Suratus Shura

Verset : 27

۞وَلَوۡ بَسَطَ ٱللَّهُ ٱلرِّزۡقَ لِعِبَادِهِۦ لَبَغَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَٰكِن يُنَزِّلُ بِقَدَرٖ مَّا يَشَآءُۚ إِنَّهُۥ بِعِبَادِهِۦ خَبِيرُۢ بَصِيرٞ

Da kuma Allah Ya shimfixa wa bayinsa arziki to da sun yi tsaurin kai a bayan qasa, sai dai kuma Yana saukarwa ne daidai gwargwado yadda Ya ga dama. Lalle Shi Masani ne game da bayinsa, Mai ganin (ayyukansu)



Sourate: Suratus Shura

Verset : 28

وَهُوَ ٱلَّذِي يُنَزِّلُ ٱلۡغَيۡثَ مِنۢ بَعۡدِ مَا قَنَطُواْ وَيَنشُرُ رَحۡمَتَهُۥۚ وَهُوَ ٱلۡوَلِيُّ ٱلۡحَمِيدُ

Shi ne kuma Yake saukar da ruwan sama bayan sun xebe qauna, Ya kuma yaxa rahamarsa. Kuma Shi ne Majivincin al’amura, Sha-yabo



Sourate: Suratus Shura

Verset : 29

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦ خَلۡقُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَثَّ فِيهِمَا مِن دَآبَّةٖۚ وَهُوَ عَلَىٰ جَمۡعِهِمۡ إِذَا يَشَآءُ قَدِيرٞ

Yana kuma daga cikin ayoyinsa halittar sammai da qasa da kuma dabbobin da Ya yaxa a cikinsu. Kuma shi Mai iko ne a kan Ya tara su idan Ya ga dama



Sourate: Suratus Shura

Verset : 30

وَمَآ أَصَٰبَكُم مِّن مُّصِيبَةٖ فَبِمَا كَسَبَتۡ أَيۡدِيكُمۡ وَيَعۡفُواْ عَن كَثِيرٖ

Abin da kuma ya same ku na wata masifa, to saboda abin da hannayenku ne suka tsuwurwurta, Yana kuma yin afuwa ga wasu (laifuka) masu yawa