Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 1

ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَهُ ٱلۡحَمۡدُ فِي ٱلۡأٓخِرَةِۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡخَبِيرُ

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Wanda duk abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa nasa ne, kuma godiya ta tabbata a gare Shi a lahira. Shi kuwa Mai hikima ne, Masani



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 2

يَعۡلَمُ مَا يَلِجُ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا يَخۡرُجُ مِنۡهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا يَعۡرُجُ فِيهَاۚ وَهُوَ ٱلرَّحِيمُ ٱلۡغَفُورُ

Yana sane da abin da yake shiga cikin qasa da abin da yake fitowa daga cikinta, da kuma abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa cikinta. Kuma Shi Mai rahama ne, Mai gafara



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 3

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَا تَأۡتِينَا ٱلسَّاعَةُۖ قُلۡ بَلَىٰ وَرَبِّي لَتَأۡتِيَنَّكُمۡ عَٰلِمِ ٱلۡغَيۡبِۖ لَا يَعۡزُبُ عَنۡهُ مِثۡقَالُ ذَرَّةٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَآ أَصۡغَرُ مِن ذَٰلِكَ وَلَآ أَكۡبَرُ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

Kuma waxanda suka kafirta suka ce: “Ranar alqiyama ba za ta zo mana ba.” Ka ce: “A’a, na rantse da Ubangijina, tabbas za ta zo muku, (Allah) Shi ne Masanin gaibu; ba abin da yake voye a gare Shi; daidai da qwayar zarra a cikin sammai ko a qasa, ko wanda ya fi wannan qanqanta ko ya fi girma, face yana nan (a rubuce) a cikin Lauhul-Mahafuzu



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 4

لِّيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُم مَّغۡفِرَةٞ وَرِزۡقٞ كَرِيمٞ

“Don Ya saka wa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka kyawawa. Waxannan suna da gafara da arziki na karamci.”



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 5

وَٱلَّذِينَ سَعَوۡ فِيٓ ءَايَٰتِنَا مُعَٰجِزِينَ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٞ مِّن رِّجۡزٍ أَلِيمٞ

Waxanda kuwa suka yi varna a cikin ayoyinmu don su nuna gazawarmu[1], waxannan suna da mummunar azaba mai raxaxi


1- Watau suna sukar ayoyin Allah da cewa sihiri ne ko bokanci ko waqa.


Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 6

وَيَرَى ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ ٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡكَ مِن رَّبِّكَ هُوَ ٱلۡحَقَّ وَيَهۡدِيٓ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Waxanda aka bai wa ilimi kuma suna ganin abin da aka saukar maka daga Ubangijinka shi ne gaskiya, kuma yana shiryarwa ne zuwa hanyar (Allah) Mabuwayi, Sha-yabo



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 7

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ هَلۡ نَدُلُّكُمۡ عَلَىٰ رَجُلٖ يُنَبِّئُكُمۡ إِذَا مُزِّقۡتُمۡ كُلَّ مُمَزَّقٍ إِنَّكُمۡ لَفِي خَلۡقٖ جَدِيدٍ

Waxanda suka kafirta suka ce: “Shin ma nuna muku wani mutum da zai ba ku labarin cewa, idan an yayyaga ku yugu-yugu lallai za ku dawo cikin wata halitta sabuwa?



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 8

أَفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبًا أَم بِهِۦ جِنَّةُۢۗ بَلِ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ فِي ٱلۡعَذَابِ وَٱلضَّلَٰلِ ٱلۡبَعِيدِ

“Shin ya yi wa Allah qarya ne, ko kuma yana da wani tavin hankali ne?” Ba haka ba ne, waxanda ba sa yin imani da lahira suna cikin azaba da vata mai nisa



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 9

أَفَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَىٰ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِن نَّشَأۡ نَخۡسِفۡ بِهِمُ ٱلۡأَرۡضَ أَوۡ نُسۡقِطۡ عَلَيۡهِمۡ كِسَفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّكُلِّ عَبۡدٖ مُّنِيبٖ

Ba sa dubawa su ga abin da yake gabansu da abin da yake bayansu na sama da qasa? In da Mun ga dama sai Mu nutsar da su cikin qasa ko kuma Mu rufto musu da wani yanki daga sama. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga duk wani bawa mai komawa ga Allah



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 10

۞وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ مِنَّا فَضۡلٗاۖ يَٰجِبَالُ أَوِّبِي مَعَهُۥ وَٱلطَّيۡرَۖ وَأَلَنَّا لَهُ ٱلۡحَدِيدَ

Kuma haqiqa Mun bai wa Dawuda falala daga gare Mu; cewa: “Ya ku duwatsu ku riqa amsa tasbihi tare da shi,” da kuma tsuntsaye; Muka kuma tausasa masa qarfe



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 11

أَنِ ٱعۡمَلۡ سَٰبِغَٰتٖ وَقَدِّرۡ فِي ٱلسَّرۡدِۖ وَٱعۡمَلُواْ صَٰلِحًاۖ إِنِّي بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

(Muka ce da shi): “Ka riqa yin cikakken silke, kuma ka kintata wajen yin saqar; kuma (kai Dawuda da iyalinka) ku yi ayyuka nagari; lalle Ni Mai ganin abin da kuke aikatawa ne.”



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 12

وَلِسُلَيۡمَٰنَ ٱلرِّيحَ غُدُوُّهَا شَهۡرٞ وَرَوَاحُهَا شَهۡرٞۖ وَأَسَلۡنَا لَهُۥ عَيۡنَ ٱلۡقِطۡرِۖ وَمِنَ ٱلۡجِنِّ مَن يَعۡمَلُ بَيۡنَ يَدَيۡهِ بِإِذۡنِ رَبِّهِۦۖ وَمَن يَزِغۡ مِنۡهُمۡ عَنۡ أَمۡرِنَا نُذِقۡهُ مِنۡ عَذَابِ ٱلسَّعِيرِ

Kuma (Muka hore wa) Sulaimanu iska, tafiyarta ta safe wata guda ce, ta yamma ma kuma wata guda ce; Muka kuma vuvvugo masa da narkakkiyar tagulla tana gudana. Daga aljannu kuma akwai masu aiki a wajensa da umarnin Ubangijinsa; wanda kuwa ya kauce wa umarninmu daga cikinsu, to za Mu xanxana masa azabar wutar Sa’ira



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 13

يَعۡمَلُونَ لَهُۥ مَا يَشَآءُ مِن مَّحَٰرِيبَ وَتَمَٰثِيلَ وَجِفَانٖ كَٱلۡجَوَابِ وَقُدُورٖ رَّاسِيَٰتٍۚ ٱعۡمَلُوٓاْ ءَالَ دَاوُۥدَ شُكۡرٗاۚ وَقَلِيلٞ مِّنۡ عِبَادِيَ ٱلشَّكُورُ

Suna aikata masa abubuwan da yake bukata na manya-manyan gine-gine[1] da mutum-mutumi[2] da akusa manya-manya kamar tafkuna da kafaffun tukwane. Ya ku iyalin Dawuda, ku yi aikin (xa’a) domin godiya. Masu godiya daga bayina kuwa kaxan ne


1- Watau wuraren ibada.


2- A wancan lokacin ba a haramta yin su ba. Sai bayan zuwan Annabi () ne ya haramta suranta su ko gina su.


Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 14

فَلَمَّا قَضَيۡنَا عَلَيۡهِ ٱلۡمَوۡتَ مَا دَلَّهُمۡ عَلَىٰ مَوۡتِهِۦٓ إِلَّا دَآبَّةُ ٱلۡأَرۡضِ تَأۡكُلُ مِنسَأَتَهُۥۖ فَلَمَّا خَرَّ تَبَيَّنَتِ ٱلۡجِنُّ أَن لَّوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ ٱلۡغَيۡبَ مَا لَبِثُواْ فِي ٱلۡعَذَابِ ٱلۡمُهِينِ

Sannan lokacin da Muka qaddara masa mutuwa ba abin da ya nuna musu mutuwarsa sai gara da ta riqa cin sandarsa[1]; to lokacin da ya faxi sai aljannu suka gane cewa da sun san gaibu da ba su zauna cikin azabar wulaqanci ba


1- Sandarsa da yake tsaye a kanta.


Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 15

لَقَدۡ كَانَ لِسَبَإٖ فِي مَسۡكَنِهِمۡ ءَايَةٞۖ جَنَّتَانِ عَن يَمِينٖ وَشِمَالٖۖ كُلُواْ مِن رِّزۡقِ رَبِّكُمۡ وَٱشۡكُرُواْ لَهُۥۚ بَلۡدَةٞ طَيِّبَةٞ وَرَبٌّ غَفُورٞ

Haqiqa akwai aya game da gidajen qabilar Saba’u (ta qasar Yaman); ita ce gonakai guda biyu na lambu a hagu da dama; (aka ce da su): “Ku ci daga arzikin Ubangijinku, kuma ku gode masa. Qasa ce mai daxin zama da kuma Ubangiji mai gafara



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 16

فَأَعۡرَضُواْ فَأَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ سَيۡلَ ٱلۡعَرِمِ وَبَدَّلۡنَٰهُم بِجَنَّتَيۡهِمۡ جَنَّتَيۡنِ ذَوَاتَيۡ أُكُلٍ خَمۡطٖ وَأَثۡلٖ وَشَيۡءٖ مِّن سِدۡرٖ قَلِيلٖ

Sai suka bijire, sai Muka aiko musu da ambaliyar madatsar ruwan Arimu, Muka kuma musanya musu gonakin nan nasu biyu da wasu gonakin biyu ma’abota ‘ya’ya masu xaci da kuma itacen tsamiya, da wani abu kaxan na ‘ya’yan magarya



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 17

ذَٰلِكَ جَزَيۡنَٰهُم بِمَا كَفَرُواْۖ وَهَلۡ نُجَٰزِيٓ إِلَّا ٱلۡكَفُورَ

Wannan shi ne Muka saka musu (da shi) saboda kafircinsu; ba kuwa Ma yin sakamako (irin wannan) sai ga mai butulci



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 18

وَجَعَلۡنَا بَيۡنَهُمۡ وَبَيۡنَ ٱلۡقُرَى ٱلَّتِي بَٰرَكۡنَا فِيهَا قُرٗى ظَٰهِرَةٗ وَقَدَّرۡنَا فِيهَا ٱلسَّيۡرَۖ سِيرُواْ فِيهَا لَيَالِيَ وَأَيَّامًا ءَامِنِينَ

Muka kuma sanya wasu alqaryu mabayyana a tsakaninsu (mutan Saba’u) da alqaryar da Muka sa albarka a cikinta (wato qasar Sham)[1], Muka kuma taqaita zangon tafiya a tsakaninsu (alqaryun; Muka ce): “Ku yi tafiya a cikinsu dare da rana cikin aminci.”


1- Watau Allah () ya sanya wasu fitattun alqaryu da matafiya kan iya hango su daga nesa, wanda hakan ya sauqaqa musu tafiye-tafiyensu.


Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 19

فَقَالُواْ رَبَّنَا بَٰعِدۡ بَيۡنَ أَسۡفَارِنَا وَظَلَمُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فَجَعَلۡنَٰهُمۡ أَحَادِيثَ وَمَزَّقۡنَٰهُمۡ كُلَّ مُمَزَّقٍۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّكُلِّ صَبَّارٖ شَكُورٖ

Sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, Ka qaddara nisa tsakanin zangunan tafiyarmu,” suka kuwa zalunci kansu, sai Muka mai da su tarihi[1], Muka kuma warwatsa su wuri-wuri. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga duk wani mai yin haquri, mai yin godiya


1- Watau Allah () ya tarwatsa su suka warwatsu a garuruwa daban-daban har haxuwa da junansu ta yi musu wahala.


Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 20

وَلَقَدۡ صَدَّقَ عَلَيۡهِمۡ إِبۡلِيسُ ظَنَّهُۥ فَٱتَّبَعُوهُ إِلَّا فَرِيقٗا مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Kuma haqiqa Iblisu ya tabbatar da zatonsa a kansu gaskiya ne[1], sai suka bi shi, in ban da wata qungiya ta muminai


1- Watau na cewa zai iya vatar da su ya raba su da gaskiya.


Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 21

وَمَا كَانَ لَهُۥ عَلَيۡهِم مِّن سُلۡطَٰنٍ إِلَّا لِنَعۡلَمَ مَن يُؤۡمِنُ بِٱلۡأٓخِرَةِ مِمَّنۡ هُوَ مِنۡهَا فِي شَكّٖۗ وَرَبُّكَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٍ حَفِيظٞ

Shi kuwa ba shi da wani qarfi a kansu, sai dai (Mun yi haka ne) don Mu bayyana wanda yake imani da ranar lahira da kuma wanda yake cikin shakka game da ita. Ubangijinka kuwa Mai kiyaye komai ne



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 22

قُلِ ٱدۡعُواْ ٱلَّذِينَ زَعَمۡتُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ لَا يَمۡلِكُونَ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا لَهُمۡ فِيهِمَا مِن شِرۡكٖ وَمَا لَهُۥ مِنۡهُم مِّن ظَهِيرٖ

Ka ce: “Ku kirawo waxanda kuka riya (cewa su ne iyayen giji) ba Allah ba;” ba sa mallakar wani abu daidai da qwayar zarra a cikin sammai ko a cikin qasa, ba kuma su da wata tarayya a cikinsu, ba Shi kuma da wani mataimaki daga cikinsu



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 23

وَلَا تَنفَعُ ٱلشَّفَٰعَةُ عِندَهُۥٓ إِلَّا لِمَنۡ أَذِنَ لَهُۥۚ حَتَّىٰٓ إِذَا فُزِّعَ عَن قُلُوبِهِمۡ قَالُواْ مَاذَا قَالَ رَبُّكُمۡۖ قَالُواْ ٱلۡحَقَّۖ وَهُوَ ٱلۡعَلِيُّ ٱلۡكَبِيرُ

Kuma ceto ba ya amfani a wurinsa sai ga wanda Ya yi wa izinin yin sa. Har idan an cire tsoro daga cikin zukatansu[1], sai su ce: “Me Ubangijinku Ya ce ne?” Suka ce: “Gaskiya Ya faxa, kuma Shi ne Maxaukaki, Mai girma.”


1- Saboda cikar mulkin Allah idan ya yi wata magana mala’iku gaba xaya sukan buga fukafukansu suna masu rusunawa ga maganarsa, suna masu cike da tsoro.


Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 24

۞قُلۡ مَن يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ قُلِ ٱللَّهُۖ وَإِنَّآ أَوۡ إِيَّاكُمۡ لَعَلَىٰ هُدًى أَوۡ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Ka ce: “Wane ne yake arzuta ku daga sammai da qasa?” Ka ce: “Allah ne; kuma mu ko ku (xaya daga cikinmu) lalle yana a kan shiriya ko kuma yana cikin vata mabayyani.”



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 25

قُل لَّا تُسۡـَٔلُونَ عَمَّآ أَجۡرَمۡنَا وَلَا نُسۡـَٔلُ عَمَّا تَعۡمَلُونَ

Ka ce: “Ba za a tambaye ku ba game da laifin da muka yi, mu ma kuma ba za a tambaye mu ba game da abin da kuke aikatawa.”



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 26

قُلۡ يَجۡمَعُ بَيۡنَنَا رَبُّنَا ثُمَّ يَفۡتَحُ بَيۡنَنَا بِٱلۡحَقِّ وَهُوَ ٱلۡفَتَّاحُ ٱلۡعَلِيمُ

Ka ce: “Ubangijinmu zai tattara mu sannan Ya yi hukunci a tsakaninmu da gaskiya, Shi ne kuwa Mai hukunci, Masani.”



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 27

قُلۡ أَرُونِيَ ٱلَّذِينَ أَلۡحَقۡتُم بِهِۦ شُرَكَآءَۖ كَلَّاۚ بَلۡ هُوَ ٱللَّهُ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Ka ce: “Ku nuna min waxanda kuka riskar da su a matsayin abokan tarayya da Shi; ku bar wannan magana! Shi ne Allah Mabuwayi Mai hikima.”



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 28

وَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ إِلَّا كَآفَّةٗ لِّلنَّاسِ بَشِيرٗا وَنَذِيرٗا وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Ba Mu kuma aiko ka ba sai ga mutane baki xaya kana mai albishir mai kuma gargaxi, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (hakan)



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 29

وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا ٱلۡوَعۡدُ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Suna kuma cewa: “Yaushe ne wannan alqawarin (na ranar alqiyama) zai zo, idan kun kasance masu gaskiya?”



Sourate: Suratu Saba’i

Verset : 30

قُل لَّكُم مِّيعَادُ يَوۡمٖ لَّا تَسۡتَـٔۡخِرُونَ عَنۡهُ سَاعَةٗ وَلَا تَسۡتَقۡدِمُونَ

Ka ce: “Kuna da ajiyayyar rana da ba za ku jinkirta ba daga gare ta daidai da sa’a, ba kuma za ku wuce ta ba.”