Sourate: Suratul Baqara

Verset : 151

كَمَآ أَرۡسَلۡنَا فِيكُمۡ رَسُولٗا مِّنكُمۡ يَتۡلُواْ عَلَيۡكُمۡ ءَايَٰتِنَا وَيُزَكِّيكُمۡ وَيُعَلِّمُكُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَيُعَلِّمُكُم مَّا لَمۡ تَكُونُواْ تَعۡلَمُونَ

Kamar yadda Muka aiko muku da wani manzo daga cikinku, yana karanta muku ayoyinmu, kuma yana tsarkake ku, kuma yana koyar da ku Littafi da Hikima[1], kuma yana koyar da ku abin da a da can ba ku sani ba


1- Hikima, ita ce sunnar Annabi ().


Sourate: Suratul Baqara

Verset : 152

فَٱذۡكُرُونِيٓ أَذۡكُرۡكُمۡ وَٱشۡكُرُواْ لِي وَلَا تَكۡفُرُونِ

Don haka ku ambace Ni, Ni ma zan ambace ku, kuma ku gode Mini, kada kuma ku kafirce Mini



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 153

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱسۡتَعِينُواْ بِٱلصَّبۡرِ وَٱلصَّلَوٰةِۚ إِنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani ku nemi taimako ta hanyar haquri da salla. Lalle Allah Yana tare da masu haquri



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 154

وَلَا تَقُولُواْ لِمَن يُقۡتَلُ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ أَمۡوَٰتُۢۚ بَلۡ أَحۡيَآءٞ وَلَٰكِن لَّا تَشۡعُرُونَ

Kada kuma ku ce wa waxanda ake kashewa a kan hanyar Allah su matattu ne. A’a, rayayyu ne, sai dai ku ne ba ku sani ba



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 155

وَلَنَبۡلُوَنَّكُم بِشَيۡءٖ مِّنَ ٱلۡخَوۡفِ وَٱلۡجُوعِ وَنَقۡصٖ مِّنَ ٱلۡأَمۡوَٰلِ وَٱلۡأَنفُسِ وَٱلثَّمَرَٰتِۗ وَبَشِّرِ ٱلصَّـٰبِرِينَ

Kuma lalle za Mu jarrabe ku da wani abin tsoro da yunwa da tawayar dukiya da ta rayuka da ta ‘ya’yan itatuwa. Don haka ka yi albishir ga masu haquri



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 156

ٱلَّذِينَ إِذَآ أَصَٰبَتۡهُم مُّصِيبَةٞ قَالُوٓاْ إِنَّا لِلَّهِ وَإِنَّآ إِلَيۡهِ رَٰجِعُونَ

(Su ne) waxanda idan wata musiba ta same su sai su ce: “Lalle mu na Allah ne, kuma lalle mu gare Shi muke komawa.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 157

أُوْلَـٰٓئِكَ عَلَيۡهِمۡ صَلَوَٰتٞ مِّن رَّبِّهِمۡ وَرَحۡمَةٞۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُهۡتَدُونَ

Waxannan suna da yabo daga Ubangijinsu da rahama, kuma waxannan su ne shiryayyu



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 158

۞إِنَّ ٱلصَّفَا وَٱلۡمَرۡوَةَ مِن شَعَآئِرِ ٱللَّهِۖ فَمَنۡ حَجَّ ٱلۡبَيۡتَ أَوِ ٱعۡتَمَرَ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡهِ أَن يَطَّوَّفَ بِهِمَاۚ وَمَن تَطَوَّعَ خَيۡرٗا فَإِنَّ ٱللَّهَ شَاكِرٌ عَلِيمٌ

Lalle dutsen Safa da na Marwa suna cikin alamomin bautar Allah, don haka wanda ya je Hajji ga Xakin Allah ko ya je Umara, to babu wani laifi a gare shi ya yi xawafi tsakaninsu. Kuma wanda ya yi biyayya ta hanyar aikata alheri, to lalle Allah Mai godiya ne kuma Masani



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 159

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَكۡتُمُونَ مَآ أَنزَلۡنَا مِنَ ٱلۡبَيِّنَٰتِ وَٱلۡهُدَىٰ مِنۢ بَعۡدِ مَا بَيَّنَّـٰهُ لِلنَّاسِ فِي ٱلۡكِتَٰبِ أُوْلَـٰٓئِكَ يَلۡعَنُهُمُ ٱللَّهُ وَيَلۡعَنُهُمُ ٱللَّـٰعِنُونَ

Lalle waxanda suke voye abin da Muka saukar na hujjoji da shiriya bayan Mun yi bayanin su ga mutane a cikin Littafi, to waxannan su ne Allah Yake la’antar su, kuma masu la’anta su ma suke la’antar su



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 160

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ وَأَصۡلَحُواْ وَبَيَّنُواْ فَأُوْلَـٰٓئِكَ أَتُوبُ عَلَيۡهِمۡ وَأَنَا ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Sai dai waxanda suka tuba kuma suka gyara kuma suka bayyana, to waxannan zan karvi tubansu, kuma lalle Ni Mai karvar tuba ne, Mai jin qai



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 161

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَمَاتُواْ وَهُمۡ كُفَّارٌ أُوْلَـٰٓئِكَ عَلَيۡهِمۡ لَعۡنَةُ ٱللَّهِ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ وَٱلنَّاسِ أَجۡمَعِينَ

Lalle waxanda suka kafirta kuma suka mutu suna kafirai, to waxannan la’anar Allah ta tabbata a kansu da ta mala’iku da mutane gaba xaya



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 162

خَٰلِدِينَ فِيهَا لَا يُخَفَّفُ عَنۡهُمُ ٱلۡعَذَابُ وَلَا هُمۡ يُنظَرُونَ

Suna masu dawwama a cikinta, ba za a sassauta masu azaba ba kuma ba za a saurara musu ba



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 163

وَإِلَٰهُكُمۡ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۖ لَّآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ٱلرَّحۡمَٰنُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma abin bautarku abin bauta ne Guda Xaya, babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Shi ne Mai rahama, Mai jin qai



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 164

إِنَّ فِي خَلۡقِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱخۡتِلَٰفِ ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ وَٱلۡفُلۡكِ ٱلَّتِي تَجۡرِي فِي ٱلۡبَحۡرِ بِمَا يَنفَعُ ٱلنَّاسَ وَمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مِن مَّآءٖ فَأَحۡيَا بِهِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَا وَبَثَّ فِيهَا مِن كُلِّ دَآبَّةٖ وَتَصۡرِيفِ ٱلرِّيَٰحِ وَٱلسَّحَابِ ٱلۡمُسَخَّرِ بَيۡنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Lalle a cikin halittar sammai da qasa da sassavawar dare da rana da jiragen ruwa da suke tafiya a kan ruwa da abin da yake amfanar mutane da kuma abin da Allah Ya saukar daga sama na ruwa, Ya rayar da qasa da shi bayan mutuwarta, Ya kuma yaxa duk wata halitta mai tafiya a cikin (qasa) da jujjuyawar iska, da kuma girgije da aka hore shi tsakanin sama da qasa, lalle akwai ayoyi ga mutane masu hankali



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 165

وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يَتَّخِذُ مِن دُونِ ٱللَّهِ أَندَادٗا يُحِبُّونَهُمۡ كَحُبِّ ٱللَّهِۖ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَشَدُّ حُبّٗا لِّلَّهِۗ وَلَوۡ يَرَى ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ إِذۡ يَرَوۡنَ ٱلۡعَذَابَ أَنَّ ٱلۡقُوَّةَ لِلَّهِ جَمِيعٗا وَأَنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعَذَابِ

Kuma akwai wasu mutane waxanda suke bauta wa wasu kishiyoyi ba Allah ba; suna son su kamar son Allah; waxanda kuwa suka yi imani sun fi son Allah (fiye da komai). Da a ce waxanda suka yi zalunci za su ga lokacin da suke ido huxu da azaba (to da sun gane) cewa, lalle duk wani qarfi na Allah ne gaba xaya, kuma lalle Allah Mai tsananin azaba ne



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 166

إِذۡ تَبَرَّأَ ٱلَّذِينَ ٱتُّبِعُواْ مِنَ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُواْ وَرَأَوُاْ ٱلۡعَذَابَ وَتَقَطَّعَتۡ بِهِمُ ٱلۡأَسۡبَابُ

Lokacin da waxanda aka yi wa biyayya (shugabanni) za su nisantar da kansu daga waxanda suka yi musu biyayya (mabiya), kuma suka yi arba da azaba, kuma duk wasu alaqoqi da ke tsakaninsu suka yanke



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 167

وَقَالَ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُواْ لَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةٗ فَنَتَبَرَّأَ مِنۡهُمۡ كَمَا تَبَرَّءُواْ مِنَّاۗ كَذَٰلِكَ يُرِيهِمُ ٱللَّهُ أَعۡمَٰلَهُمۡ حَسَرَٰتٍ عَلَيۡهِمۡۖ وَمَا هُم بِخَٰرِجِينَ مِنَ ٱلنَّارِ

Kuma waxanda suka yi biyayya suka ce: “Ina ma dai muna da wata dama ta komawa (duniya) don mu ma mu nisantar da kanmu daga gare su, kamar yadda suka nisanta kansu daga gare mu?” Kamar haka ne Allah Yake nuna musu ayyukansu suka zama nadama a gare su, kuma su ba masu samun fita ne daga wuta ba



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 168

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ كُلُواْ مِمَّا فِي ٱلۡأَرۡضِ حَلَٰلٗا طَيِّبٗا وَلَا تَتَّبِعُواْ خُطُوَٰتِ ٱلشَّيۡطَٰنِۚ إِنَّهُۥ لَكُمۡ عَدُوّٞ مُّبِينٌ

Ya ku mutane, ku ci halal mai daxi na abin da ke bayan qasa, kada kuma ku bi hanyoyin Shaixan, lalle shi maqiyi ne mai bayyana qiyayya a gare ku



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 169

إِنَّمَا يَأۡمُرُكُم بِٱلسُّوٓءِ وَٱلۡفَحۡشَآءِ وَأَن تَقُولُواْ عَلَى ٱللَّهِ مَا لَا تَعۡلَمُونَ

Yana umartar ku ne kawai da savo da ayyukan assha da kuma faxin abin da ba ku da ilimi game da shi ku jingina wa Allah



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 170

وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ ٱتَّبِعُواْ مَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ قَالُواْ بَلۡ نَتَّبِعُ مَآ أَلۡفَيۡنَا عَلَيۡهِ ءَابَآءَنَآۚ أَوَلَوۡ كَانَ ءَابَآؤُهُمۡ لَا يَعۡقِلُونَ شَيۡـٔٗا وَلَا يَهۡتَدُونَ

Idan kuma aka ce musu: “Ku bi abin da Allah Ya saukar”, sai su ce: “A’a, za dai mu bi abin da muka samu iyayenmu a kansa”. To, ko da iyayensu ba sa hankaltar komai, kuma ba sa shiryuwa?



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 171

وَمَثَلُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ كَمَثَلِ ٱلَّذِي يَنۡعِقُ بِمَا لَا يَسۡمَعُ إِلَّا دُعَآءٗ وَنِدَآءٗۚ صُمُّۢ بُكۡمٌ عُمۡيٞ فَهُمۡ لَا يَعۡقِلُونَ

Misalin wadanda suka kafirta kamar misalin wanda yake daga sauti ne ga wanda ba ya jin (komai) sai kira da sowa. Kurame ne, bebaye ne, makafi ne, don haka su ba sa hankalta



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 172

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُلُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا رَزَقۡنَٰكُمۡ وَٱشۡكُرُواْ لِلَّهِ إِن كُنتُمۡ إِيَّاهُ تَعۡبُدُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku ci daga daxaxan abin da Muka arzuta ku (da shi), kuma ku yi godiya ga Allah in har kun kasance Shi kaxai kuke bauta wa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 173

إِنَّمَا حَرَّمَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَيۡتَةَ وَٱلدَّمَ وَلَحۡمَ ٱلۡخِنزِيرِ وَمَآ أُهِلَّ بِهِۦ لِغَيۡرِ ٱللَّهِۖ فَمَنِ ٱضۡطُرَّ غَيۡرَ بَاغٖ وَلَا عَادٖ فَلَآ إِثۡمَ عَلَيۡهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

(Allah) Ya haramta muku mushe ne kawai da jini da naman alade da abin da aka kira sunan wani ba Allah ba (lokacin yanka shi). Don haka duk wanda ya matsu, ba mai zalunci ba, kuma ba mai qetare iyaka ba, to babu laifi a kansa ya ci. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 174

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَكۡتُمُونَ مَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلۡكِتَٰبِ وَيَشۡتَرُونَ بِهِۦ ثَمَنٗا قَلِيلًا أُوْلَـٰٓئِكَ مَا يَأۡكُلُونَ فِي بُطُونِهِمۡ إِلَّا ٱلنَّارَ وَلَا يُكَلِّمُهُمُ ٱللَّهُ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ وَلَا يُزَكِّيهِمۡ وَلَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٌ

Lalle waxanda suke voye abin da Allah Ya saukar na Littafi, kuma suke musanya shi da xan kuxi kaxan, waxannan babu abin da suke ci a cikkunansu sai wuta, kuma Allah ba zai yi musu magana ba ranar tashin alqiyama, kuma ba zai tsarkake su ba, kuma suna da wata azaba mai raxaxi



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 175

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ ٱشۡتَرَوُاْ ٱلضَّلَٰلَةَ بِٱلۡهُدَىٰ وَٱلۡعَذَابَ بِٱلۡمَغۡفِرَةِۚ فَمَآ أَصۡبَرَهُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ

Waxannan su ne waxanda suka zavi vata a madadin shiriya da kuma azaba a madadin gafara. Don haka yi mamakin haqurin (zamansu) a cikin wuta



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 176

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ نَزَّلَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّۗ وَإِنَّ ٱلَّذِينَ ٱخۡتَلَفُواْ فِي ٱلۡكِتَٰبِ لَفِي شِقَاقِۭ بَعِيدٖ

Wannan ya faru ne saboda lalle Allah Ya saukar da Littafinsa da gaskiya. Kuma lalle duk waxanda suka yi savani dangane da Littafin, tabbas suna cikin savawa mai nisa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 177

۞لَّيۡسَ ٱلۡبِرَّ أَن تُوَلُّواْ وُجُوهَكُمۡ قِبَلَ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَلَٰكِنَّ ٱلۡبِرَّ مَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ وَٱلۡكِتَٰبِ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ وَءَاتَى ٱلۡمَالَ عَلَىٰ حُبِّهِۦ ذَوِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينَ وَٱبۡنَ ٱلسَّبِيلِ وَٱلسَّآئِلِينَ وَفِي ٱلرِّقَابِ وَأَقَامَ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتَى ٱلزَّكَوٰةَ وَٱلۡمُوفُونَ بِعَهۡدِهِمۡ إِذَا عَٰهَدُواْۖ وَٱلصَّـٰبِرِينَ فِي ٱلۡبَأۡسَآءِ وَٱلضَّرَّآءِ وَحِينَ ٱلۡبَأۡسِۗ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ صَدَقُواْۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُتَّقُونَ

Ba wai aikin xa’a shi ne ku juyar da fuskokinku mahudar rana ko mafaxarta ba ; sai dai aikin xa’a shi ne, wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira da mala’iku da littattafai da annabawa, kuma ya bayar da dukiyarsa, alhalin yana son ta, ga dangi na kusa da marayu da mabuqata da matafiyi da kuma masu roqo (bisa larura) da ‘yantar da bayi, sannan kuma ya tsayar da salla, kuma ya bayar da zakka, da kuma masu cika alqawarinsu idan suka qulla alqawari ; da masu haquri a cikin halin talauci da halin rashin lafiya da lokacin yaqi. Waxannan su ne waxanda suka yi gaskiya, kuma waxannan su ne masu taqawa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 178

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُتِبَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡقِصَاصُ فِي ٱلۡقَتۡلَىۖ ٱلۡحُرُّ بِٱلۡحُرِّ وَٱلۡعَبۡدُ بِٱلۡعَبۡدِ وَٱلۡأُنثَىٰ بِٱلۡأُنثَىٰۚ فَمَنۡ عُفِيَ لَهُۥ مِنۡ أَخِيهِ شَيۡءٞ فَٱتِّبَاعُۢ بِٱلۡمَعۡرُوفِ وَأَدَآءٌ إِلَيۡهِ بِإِحۡسَٰنٖۗ ذَٰلِكَ تَخۡفِيفٞ مِّن رَّبِّكُمۡ وَرَحۡمَةٞۗ فَمَنِ ٱعۡتَدَىٰ بَعۡدَ ذَٰلِكَ فَلَهُۥ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, an wajabta muku qisasi dangane da waxanda aka kashe; xa da xa, bawa da bawa, mace da mace[1]. To duk wanda aka yafe masa qisasin xan uwansa, to sai ya bibiye shi ta hanyar da ta dace, shi kuma ya biya diyyar ta hanyar kyautatawa. Wannan (abin da aka ambata), sauqi ne da rahama daga wajen Ubangijinku. Don haka duk wanda ya qetare iyaka bayan haka, to yana da azaba mai raxaxi


1- Haka hukuncin yake yayin da namiji xa ya kashe ‘ya mace, ko mace ta kashe xa namiji. Amma idan magadan wanda aka kashe suka yafe, to babu zancen qisasi, sai a biya diyya kawai.


Sourate: Suratul Baqara

Verset : 179

وَلَكُمۡ فِي ٱلۡقِصَاصِ حَيَوٰةٞ يَـٰٓأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Kuma a cikin (hukuncin) qisasi akwai (tsare) rayuwa a gare ku, ya ku ma’abota hankula, don ku samu taqawa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 180

كُتِبَ عَلَيۡكُمۡ إِذَا حَضَرَ أَحَدَكُمُ ٱلۡمَوۡتُ إِن تَرَكَ خَيۡرًا ٱلۡوَصِيَّةُ لِلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَ بِٱلۡمَعۡرُوفِۖ حَقًّا عَلَى ٱلۡمُتَّقِينَ

An wajabta muku, idan alamun mutuwa suka zo wa xayanku, idan har ya bar wani alheri (dukiya), to ya yi wasiyya ga mahaifa biyu da dangi mafiya kusanci, ta hanyar da ta dace (a shari’a). Haqqi ne tabbatacce a kan masu taqawa[1]


1- Wasu malamai suna ganin cewa, ayar rabon gado ta Suratun Nisa’i aya ta 11 ta shafe hukuncin wannan ayar. Wasu kuma suna ganin hukuncinta dangane da wasiyya ga makusanta da ba za su ci gado ba yana nan, amma da sharaxin kada wasiyyar ta wuce sulusin abin da ya bari na dukiya.