Sourate: Suratul An’am

Verset : 121

وَلَا تَأۡكُلُواْ مِمَّا لَمۡ يُذۡكَرِ ٱسۡمُ ٱللَّهِ عَلَيۡهِ وَإِنَّهُۥ لَفِسۡقٞۗ وَإِنَّ ٱلشَّيَٰطِينَ لَيُوحُونَ إِلَىٰٓ أَوۡلِيَآئِهِمۡ لِيُجَٰدِلُوكُمۡۖ وَإِنۡ أَطَعۡتُمُوهُمۡ إِنَّكُمۡ لَمُشۡرِكُونَ

Kuma kada ku ci daga abin da ba a ambaci sunan Allah a kansa ba, kuma lalle shi tabbas fasiqanci ne. Haqiqa shaixanu tabbas suna kimsa wa masoyansu, don su yi jayayya da ku; idan kuwa kuka bi su to lalle tabbas ku mushirikai ne



Sourate: Suratul An’am

Verset : 122

أَوَمَن كَانَ مَيۡتٗا فَأَحۡيَيۡنَٰهُ وَجَعَلۡنَا لَهُۥ نُورٗا يَمۡشِي بِهِۦ فِي ٱلنَّاسِ كَمَن مَّثَلُهُۥ فِي ٱلظُّلُمَٰتِ لَيۡسَ بِخَارِجٖ مِّنۡهَاۚ كَذَٰلِكَ زُيِّنَ لِلۡكَٰفِرِينَ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Shin yanzu wanda ya kasance matacce (kafiri), sai Muka rayar da shi, kuma Muka sanya masa haske (na shiriya), yana tafiya da shi cikin mutane, (yanzu) zai zama kamar wanda yake cikin duhu (na kafirci), ta yadda ba zai iya fita daga cikinsa ba? Kamar haka ne aka qawata wa kafirai abin da suka kasance suna aikatawa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 123

وَكَذَٰلِكَ جَعَلۡنَا فِي كُلِّ قَرۡيَةٍ أَكَٰبِرَ مُجۡرِمِيهَا لِيَمۡكُرُواْ فِيهَاۖ وَمَا يَمۡكُرُونَ إِلَّا بِأَنفُسِهِمۡ وَمَا يَشۡعُرُونَ

Kuma kamar haka ne a cikin kowace qasa Muka sanya manyan masu laifinta, don su yi makirci a cikinta; kuma ba wanda suke qulla wa makirci sai kawunansu, amma su ba sa jin (haka)



Sourate: Suratul An’am

Verset : 124

وَإِذَا جَآءَتۡهُمۡ ءَايَةٞ قَالُواْ لَن نُّؤۡمِنَ حَتَّىٰ نُؤۡتَىٰ مِثۡلَ مَآ أُوتِيَ رُسُلُ ٱللَّهِۘ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ حَيۡثُ يَجۡعَلُ رِسَالَتَهُۥۗ سَيُصِيبُ ٱلَّذِينَ أَجۡرَمُواْ صَغَارٌ عِندَ ٱللَّهِ وَعَذَابٞ شَدِيدُۢ بِمَا كَانُواْ يَمۡكُرُونَ

Kuma idan wata aya ta zo musu, sai su ce: “Ba za mu yi imani ba, har sai an ba mu kwatankwacin abin da aka ba wa manzannin Allah.” Ai Allah Shi ne Mafi sanin inda ya dace Ya sanya manzancinsa. Da sannu qasqanci daga Allah zai auka wa waxanda suka aikata manyan laifuka da kuma azaba mai tsanani, saboda abin da suka kasance suna shiryawa na makirci



Sourate: Suratul An’am

Verset : 125

فَمَن يُرِدِ ٱللَّهُ أَن يَهۡدِيَهُۥ يَشۡرَحۡ صَدۡرَهُۥ لِلۡإِسۡلَٰمِۖ وَمَن يُرِدۡ أَن يُضِلَّهُۥ يَجۡعَلۡ صَدۡرَهُۥ ضَيِّقًا حَرَجٗا كَأَنَّمَا يَصَّعَّدُ فِي ٱلسَّمَآءِۚ كَذَٰلِكَ يَجۡعَلُ ٱللَّهُ ٱلرِّجۡسَ عَلَى ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ

Sannan duk wanda Allah Ya yi nufin shiryar da shi, sai Ya yalwata qirjinsa ga karvar Musulunci. Duk wanda kuwa Ya yi nufin Ya vatar da shi, sai Ya sanya qirjinsa a quntace ainun kamar wanda yake yunqurin hawa sama. Kamar haka ne Allah Yake sanya vata a kan waxanda ba sa yin imani



Sourate: Suratul An’am

Verset : 126

وَهَٰذَا صِرَٰطُ رَبِّكَ مُسۡتَقِيمٗاۗ قَدۡ فَصَّلۡنَا ٱلۡأٓيَٰتِ لِقَوۡمٖ يَذَّكَّرُونَ

Kuma wannan shi ne tafarkin Ubangijinka miqaqqe. Haqiqa Mun bayyana ayoyi ga mutanen da suke tuntuntuni



Sourate: Suratul An’am

Verset : 127

۞لَهُمۡ دَارُ ٱلسَّلَٰمِ عِندَ رَبِّهِمۡۖ وَهُوَ وَلِيُّهُم بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Suna da gida na aminci a wurin Ubangijinsu, kuma Shi ne Majivincinsu, saboda abin da suka kasance suna aikatawa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 128

وَيَوۡمَ يَحۡشُرُهُمۡ جَمِيعٗا يَٰمَعۡشَرَ ٱلۡجِنِّ قَدِ ٱسۡتَكۡثَرۡتُم مِّنَ ٱلۡإِنسِۖ وَقَالَ أَوۡلِيَآؤُهُم مِّنَ ٱلۡإِنسِ رَبَّنَا ٱسۡتَمۡتَعَ بَعۡضُنَا بِبَعۡضٖ وَبَلَغۡنَآ أَجَلَنَا ٱلَّذِيٓ أَجَّلۡتَ لَنَاۚ قَالَ ٱلنَّارُ مَثۡوَىٰكُمۡ خَٰلِدِينَ فِيهَآ إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّ رَبَّكَ حَكِيمٌ عَلِيمٞ

Kuma (ka tuna) ranar da zai tara su gaba xaya (Ya ce): “Ya ku jama’ar aljannu, haqiqa kun samu mabiya da yawa daga cikin mutane.” Sai majivinta lamarinsu cikin mutane su ce: “Ya Ubangijinmu; mun dai daxaxa wa junanmu kuma mun kawo qarshen lokacin da Ka yanka mana.” Sai Ya ce: “Wuta ita ce makomarku, za ku dawwama a cikinta, sai dai abin da Allah Ya ga dama.” Lalle Ubangijinka Mai hikima ne, Mai yawan sani



Sourate: Suratul An’am

Verset : 129

وَكَذَٰلِكَ نُوَلِّي بَعۡضَ ٱلظَّـٰلِمِينَ بَعۡضَۢا بِمَا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ

Kuma kamar haka ne Muke xora wani sashi na azzalumai a kan wani sashi, saboda abin da suka kasance suna aikatawa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 130

يَٰمَعۡشَرَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ رُسُلٞ مِّنكُمۡ يَقُصُّونَ عَلَيۡكُمۡ ءَايَٰتِي وَيُنذِرُونَكُمۡ لِقَآءَ يَوۡمِكُمۡ هَٰذَاۚ قَالُواْ شَهِدۡنَا عَلَىٰٓ أَنفُسِنَاۖ وَغَرَّتۡهُمُ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا وَشَهِدُواْ عَلَىٰٓ أَنفُسِهِمۡ أَنَّهُمۡ كَانُواْ كَٰفِرِينَ

Ya ku jama’ar aljannu da mutane, shin manzanni daga cikinku ba su zo muku ba, suna karanta muku ayoyina, kuma suna gargaxin ku game da saduwarku da wannan yini?” Sai su ce: “Mun ba da shaida a kan kawunanmu;” rayuwar duniya kuma ta ruxe su, kuma suka yi wa kansu shaidar cewa lalle su sun kasance kafirai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 131

ذَٰلِكَ أَن لَّمۡ يَكُن رَّبُّكَ مُهۡلِكَ ٱلۡقُرَىٰ بِظُلۡمٖ وَأَهۡلُهَا غَٰفِلُونَ

Haka ta faru ne, saboda Ubangijinka bai zamanto Mai hallakar da wata alqarya saboda kafircewarta ba, alhali mutanenta suna cikin gafala



Sourate: Suratul An’am

Verset : 132

وَلِكُلّٖ دَرَجَٰتٞ مِّمَّا عَمِلُواْۚ وَمَا رَبُّكَ بِغَٰفِلٍ عَمَّا يَعۡمَلُونَ

Kuma kowanne yana da nasa matsayi game da abin da suka aikata, kuma Ubangijinka bai zama Mai rafkana ba dangane da abin da suke aikatawa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 133

وَرَبُّكَ ٱلۡغَنِيُّ ذُو ٱلرَّحۡمَةِۚ إِن يَشَأۡ يُذۡهِبۡكُمۡ وَيَسۡتَخۡلِفۡ مِنۢ بَعۡدِكُم مَّا يَشَآءُ كَمَآ أَنشَأَكُم مِّن ذُرِّيَّةِ قَوۡمٍ ءَاخَرِينَ

Kuma Ubangijinka Shi ne Mawadaci, Mai rahama. Idan Ya ga dama sai Ya tafiyar da ku, kuma Ya maye gurbinku da waxanda Ya ga dama, kamar yadda Ya fare ku daga zurriyar waxansu mutanen daban



Sourate: Suratul An’am

Verset : 134

إِنَّ مَا تُوعَدُونَ لَأٓتٖۖ وَمَآ أَنتُم بِمُعۡجِزِينَ

Lalle abin da ake yi Muku alqawarinsa mai zuwa ne; kuma ku ba za ku iya kuvucewa (daga azabarmu) ba



Sourate: Suratul An’am

Verset : 135

قُلۡ يَٰقَوۡمِ ٱعۡمَلُواْ عَلَىٰ مَكَانَتِكُمۡ إِنِّي عَامِلٞۖ فَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَ مَن تَكُونُ لَهُۥ عَٰقِبَةُ ٱلدَّارِۚ إِنَّهُۥ لَا يُفۡلِحُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Ka ce: “Ya ku mutanena, ku yi aiki a kan irin hanyarku, lalle ni ma mai yin aiki ne (kan hanyata); don haka da sannu za ku san wanda zai yi kyakkyawan qarshe. Lalle su dai azzalumai ba za su rabauta ba



Sourate: Suratul An’am

Verset : 136

وَجَعَلُواْ لِلَّهِ مِمَّا ذَرَأَ مِنَ ٱلۡحَرۡثِ وَٱلۡأَنۡعَٰمِ نَصِيبٗا فَقَالُواْ هَٰذَا لِلَّهِ بِزَعۡمِهِمۡ وَهَٰذَا لِشُرَكَآئِنَاۖ فَمَا كَانَ لِشُرَكَآئِهِمۡ فَلَا يَصِلُ إِلَى ٱللَّهِۖ وَمَا كَانَ لِلَّهِ فَهُوَ يَصِلُ إِلَىٰ شُرَكَآئِهِمۡۗ سَآءَ مَا يَحۡكُمُونَ

Kuma sun sanya wa Allah wani kaso cikin abin da Ya halitta na amfanin gona da dabbobin gida, sai suka riqa cewa: “Wannan kaso na Allah ne”, a riyawarsu, “Wannan kuma na gumakanmu ne;” sannan abin da ya kasance na gumakansu ba zai isa ga Allah ba; abin da kuwa ya kasance na Allah, to shi zai isa ga gumakansu. Abin da suke hukuntawa ya munana[1]


1- Mushirikan Larabawa sukan kasa amfanin gonarsu da dabbobinsu kaso biyu, kaso xaya su ce na Allah ne, kaso na biyun kuma su ce na gumakansu ne. To idan kason gumakansu ya shiga cikin kason Allah sai su dawo da shi wurinsu, amma idan kason da suka ware wa Allah ya shiga na gumakansu ba za su dawo da shi ba.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 137

وَكَذَٰلِكَ زَيَّنَ لِكَثِيرٖ مِّنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ قَتۡلَ أَوۡلَٰدِهِمۡ شُرَكَآؤُهُمۡ لِيُرۡدُوهُمۡ وَلِيَلۡبِسُواْ عَلَيۡهِمۡ دِينَهُمۡۖ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ مَا فَعَلُوهُۖ فَذَرۡهُمۡ وَمَا يَفۡتَرُونَ

Kuma kamar haka ne abokan tarayyarsu suka qawata wa yawancin mushirikai su dinga kashe ‘ya’yansu, don su hallakar da su, kuma don su rikita musu addininsu. Kuma da Allah Ya ga dama da ba su aikata haka ba. To ka qyale su da irin abin da suke qagawa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 138

وَقَالُواْ هَٰذِهِۦٓ أَنۡعَٰمٞ وَحَرۡثٌ حِجۡرٞ لَّا يَطۡعَمُهَآ إِلَّا مَن نَّشَآءُ بِزَعۡمِهِمۡ وَأَنۡعَٰمٌ حُرِّمَتۡ ظُهُورُهَا وَأَنۡعَٰمٞ لَّا يَذۡكُرُونَ ٱسۡمَ ٱللَّهِ عَلَيۡهَا ٱفۡتِرَآءً عَلَيۡهِۚ سَيَجۡزِيهِم بِمَا كَانُواْ يَفۡتَرُونَ

Kuma suka ce: “Waxannan dabbobi na gida da kuma amfanin gona haramtattu ne, ba wanda zai ci su sai wanda muka ga dama,” a riyawarsu. Waxansu dabbobin kuma an haramta hawansu, waxansu dabbobin kuma ba sa ambaton sunan Allah a kansu (yayin yankan su), don kawai su yi masa qage. Da sannu zai yi musu sakamakon abin da suka kasance suna qagawa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 139

وَقَالُواْ مَا فِي بُطُونِ هَٰذِهِ ٱلۡأَنۡعَٰمِ خَالِصَةٞ لِّذُكُورِنَا وَمُحَرَّمٌ عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِنَاۖ وَإِن يَكُن مَّيۡتَةٗ فَهُمۡ فِيهِ شُرَكَآءُۚ سَيَجۡزِيهِمۡ وَصۡفَهُمۡۚ إِنَّهُۥ حَكِيمٌ عَلِيمٞ

Kuma suka ce: “Abin da yake cikin waxannan dabbobi, a kevance yake ga mazajenmu, amma haramun ne ga matayenmu.” Idan kuma ya zamo mushe, to su duka sai su yi tarayya a kansa. Da sannu (Allah) zai yi musu sakayyar wannan abin da suka siffanta. Lalle Shi Mai hikima ne, Mai yawan sani



Sourate: Suratul An’am

Verset : 140

قَدۡ خَسِرَ ٱلَّذِينَ قَتَلُوٓاْ أَوۡلَٰدَهُمۡ سَفَهَۢا بِغَيۡرِ عِلۡمٖ وَحَرَّمُواْ مَا رَزَقَهُمُ ٱللَّهُ ٱفۡتِرَآءً عَلَى ٱللَّهِۚ قَدۡ ضَلُّواْ وَمَا كَانُواْ مُهۡتَدِينَ

Haqiqa waxannan da suka kashe ‘ya’yansu don wauta, ba tare da ilimi ba sun tave, kuma suka haramta wa kansu abin da Allah Ya arzuta su da shi, don qage ga Allah. Haqiqa sun vata, kuma ba su kasance shiryayyu ba



Sourate: Suratul An’am

Verset : 141

۞وَهُوَ ٱلَّذِيٓ أَنشَأَ جَنَّـٰتٖ مَّعۡرُوشَٰتٖ وَغَيۡرَ مَعۡرُوشَٰتٖ وَٱلنَّخۡلَ وَٱلزَّرۡعَ مُخۡتَلِفًا أُكُلُهُۥ وَٱلزَّيۡتُونَ وَٱلرُّمَّانَ مُتَشَٰبِهٗا وَغَيۡرَ مُتَشَٰبِهٖۚ كُلُواْ مِن ثَمَرِهِۦٓ إِذَآ أَثۡمَرَ وَءَاتُواْ حَقَّهُۥ يَوۡمَ حَصَادِهِۦۖ وَلَا تُسۡرِفُوٓاْۚ إِنَّهُۥ لَا يُحِبُّ ٱلۡمُسۡرِفِينَ

Kuma Shi ne Wanda Ya halicci lambuna waxanda suke da tsirrai masu yaxo da marasa yaxo da kuma dabino da shukoki waxanda suka sha bamban da juna wajen xanxanonsu, da kuma zaitun da ruman, mai kama da juna, da wanda ba ya kama da juna. Ku ci daga ‘ya’yansa, idan ya yi ‘ya’ya, kuma ku bayar da zakkarsa a ranar girbinsa, kuma kada ku yi almubazzaranci. Lalle Shi (Allah) ba Ya son masu almubazzaranci



Sourate: Suratul An’am

Verset : 142

وَمِنَ ٱلۡأَنۡعَٰمِ حَمُولَةٗ وَفَرۡشٗاۚ كُلُواْ مِمَّا رَزَقَكُمُ ٱللَّهُ وَلَا تَتَّبِعُواْ خُطُوَٰتِ ٱلشَّيۡطَٰنِۚ إِنَّهُۥ لَكُمۡ عَدُوّٞ مُّبِينٞ

Daga cikin dabbobin gida kuma akwai masu xaukan kaya da kuma qanana. Ku ci daga abin da Allah Ya arzuta ku da shi, kuma kada ku bi hanyoyin Shaixan. Lalle shi maqiyi ne mai bayyana qiyayya a gare ku



Sourate: Suratul An’am

Verset : 143

ثَمَٰنِيَةَ أَزۡوَٰجٖۖ مِّنَ ٱلضَّأۡنِ ٱثۡنَيۡنِ وَمِنَ ٱلۡمَعۡزِ ٱثۡنَيۡنِۗ قُلۡ ءَآلذَّكَرَيۡنِ حَرَّمَ أَمِ ٱلۡأُنثَيَيۡنِ أَمَّا ٱشۡتَمَلَتۡ عَلَيۡهِ أَرۡحَامُ ٱلۡأُنثَيَيۡنِۖ نَبِّـُٔونِي بِعِلۡمٍ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

(Dabbobin) nau’i takwas ne, daga tumaki akwai jinsi biyu, haka kuma daga awaki akwai jinsi biyu. Ka ce: “Shin mazan biyu ne Ya haramta ko kuma matan biyu ko kuma abin da yake cikin mahaifar matan biyu? Ku ba ni labari da ilimi in kun kasance ku masu gaskiya ne.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 144

وَمِنَ ٱلۡإِبِلِ ٱثۡنَيۡنِ وَمِنَ ٱلۡبَقَرِ ٱثۡنَيۡنِۗ قُلۡ ءَآلذَّكَرَيۡنِ حَرَّمَ أَمِ ٱلۡأُنثَيَيۡنِ أَمَّا ٱشۡتَمَلَتۡ عَلَيۡهِ أَرۡحَامُ ٱلۡأُنثَيَيۡنِۖ أَمۡ كُنتُمۡ شُهَدَآءَ إِذۡ وَصَّىٰكُمُ ٱللَّهُ بِهَٰذَاۚ فَمَنۡ أَظۡلَمُ مِمَّنِ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبٗا لِّيُضِلَّ ٱلنَّاسَ بِغَيۡرِ عِلۡمٍۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Haka kuma raquma akwai jinsi biyu, daga cikin shanu ma akwai jinsi biyu. Ka ce: “Shin mazan guda biyu Ya haramta ko matan biyu ko kuma abin da yake cikin mahaifar matan biyu ya haramta ko kuma kun zama shaidu yayin da Allah Ya yi muku wasicci da wannan abin?” To ba wanda ya fi zaluntar kansa fiye da wanda ya qirqiri qarya, ya jingina wa Allah don ya vatar da mutane ba tare da ilimi ba. Lalle Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 145

قُل لَّآ أَجِدُ فِي مَآ أُوحِيَ إِلَيَّ مُحَرَّمًا عَلَىٰ طَاعِمٖ يَطۡعَمُهُۥٓ إِلَّآ أَن يَكُونَ مَيۡتَةً أَوۡ دَمٗا مَّسۡفُوحًا أَوۡ لَحۡمَ خِنزِيرٖ فَإِنَّهُۥ رِجۡسٌ أَوۡ فِسۡقًا أُهِلَّ لِغَيۡرِ ٱللَّهِ بِهِۦۚ فَمَنِ ٱضۡطُرَّ غَيۡرَ بَاغٖ وَلَا عَادٖ فَإِنَّ رَبَّكَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ka ce: “Daga cikin abin da aka sauqar mini na manzanci ban samu wani abinci da aka haramta cinsa ba, sai fa idan ya zamo mushe ne ko jini mai kwarara, ko kuma naman alade, to lalle wannan qazanta ne, ko kuma abin da ya zamo fasiqanci ne wanda aka yanka shi ba da sunan Allah ba.” Sannan wanda ya matsu, ba tare da shisshigi ba, kuma ba yana mai qetare iyaka ba, to lalle Ubangijinka Mai gafara ne, Mai jin qai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 146

وَعَلَى ٱلَّذِينَ هَادُواْ حَرَّمۡنَا كُلَّ ذِي ظُفُرٖۖ وَمِنَ ٱلۡبَقَرِ وَٱلۡغَنَمِ حَرَّمۡنَا عَلَيۡهِمۡ شُحُومَهُمَآ إِلَّا مَا حَمَلَتۡ ظُهُورُهُمَآ أَوِ ٱلۡحَوَايَآ أَوۡ مَا ٱخۡتَلَطَ بِعَظۡمٖۚ ذَٰلِكَ جَزَيۡنَٰهُم بِبَغۡيِهِمۡۖ وَإِنَّا لَصَٰدِقُونَ

Kuma Mun haramta wa Yahudawa duk wata dabba mai kofato; daga shanu da tumaki kuwa Mun haramta musu kitsensu, sai abin da gadon bayansu yake xauke da shi ko kayan cikinsu ko abin da ya cakuxu da qashi[1]. Wannan Mun Yi musu sakamako da shi ne saboda zaluncinsu; kuma lalle Mu tabbas Masu gaskiya ne


1- Watau an haramta musu kitsen shanu da tumaki sai dai kitsen da ke gadon bayan waxannan dabbobi ko wanda yake tare da kayan ciki ko wanda ya haxe da qashi.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 147

فَإِن كَذَّبُوكَ فَقُل رَّبُّكُمۡ ذُو رَحۡمَةٖ وَٰسِعَةٖ وَلَا يُرَدُّ بَأۡسُهُۥ عَنِ ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Sannan idan sun qaryata ka, to ka ce: “Ubangijinku Ma’abocin rahama mayalwaciya ne. Kuma ba a iya mayar da azabarsa daga mutanen da suke masu laifi.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 148

سَيَقُولُ ٱلَّذِينَ أَشۡرَكُواْ لَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ مَآ أَشۡرَكۡنَا وَلَآ ءَابَآؤُنَا وَلَا حَرَّمۡنَا مِن شَيۡءٖۚ كَذَٰلِكَ كَذَّبَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ حَتَّىٰ ذَاقُواْ بَأۡسَنَاۗ قُلۡ هَلۡ عِندَكُم مِّنۡ عِلۡمٖ فَتُخۡرِجُوهُ لَنَآۖ إِن تَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَإِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا تَخۡرُصُونَ

Waxanda suke yin shirka za su ce: “Da Allah Ya ga dama, da ba mu yi shirka ba, haka iyayenmu ma da ba su yi ba, kuma da ba mu haramta wani abu ba.” Kamar haka ne waxanda suka gabace su suka qaryata (manzanni), har sai da suka xanxani azabarmu. Ka ce: “Shin kuna da wata hujja ce da za ku fito mana da ita? Ba fa abin da kuke bi sai zato, kuma ku (ba a kan komai kuke ba) face shaci-faxi.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 149

قُلۡ فَلِلَّهِ ٱلۡحُجَّةُ ٱلۡبَٰلِغَةُۖ فَلَوۡ شَآءَ لَهَدَىٰكُمۡ أَجۡمَعِينَ

Ka ce: “To a wurin Allah ne cikakkiyar hujja take; kuma da Ya ga dama, tabbas da Ya shiryar da ku gaba xaya.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 150

قُلۡ هَلُمَّ شُهَدَآءَكُمُ ٱلَّذِينَ يَشۡهَدُونَ أَنَّ ٱللَّهَ حَرَّمَ هَٰذَاۖ فَإِن شَهِدُواْ فَلَا تَشۡهَدۡ مَعَهُمۡۚ وَلَا تَتَّبِعۡ أَهۡوَآءَ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا وَٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ وَهُم بِرَبِّهِمۡ يَعۡدِلُونَ

Ka ce: “Ku kawo shaidunku waxanda za su ba da shaidar cewa, Allah Shi Ya haramta wannan.” Sannan idan har sun ba da shaidar, to kai kada ka bayar da shaida tare da su. Kuma kada ka bi soye-soyen zukatan waxanda suka qaryata ayoyinmu, waxanda kuma ba sa yin imani da ranar lahira, su ne kuwa masu daidaita Ubangijinsu (da wani abu)