Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 121

أُوْلَـٰٓئِكَ مَأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُ وَلَا يَجِدُونَ عَنۡهَا مَحِيصٗا

Waxannan makomarsu wutar Jahannama ce, kuma ba za su sami wurin kauce mata ba



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 122

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ سَنُدۡخِلُهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٗاۚ وَمَنۡ أَصۡدَقُ مِنَ ٱللَّهِ قِيلٗا

Kuma waxanda suka yi imani, kuma suka yi aiki nagari, za Mu shigar da su gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu har abada; kuma alqawarin Allah tabbatacce ne. Kuma wane ne ya fi Allah gaskiyar zance?



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 123

لَّيۡسَ بِأَمَانِيِّكُمۡ وَلَآ أَمَانِيِّ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِۗ مَن يَعۡمَلۡ سُوٓءٗا يُجۡزَ بِهِۦ وَلَا يَجِدۡ لَهُۥ مِن دُونِ ٱللَّهِ وَلِيّٗا وَلَا نَصِيرٗا

(Al’amarin) ba wai ya dangaci burace-buracenku ba ne, ba kuma burace-buracen Ma’abota Littafi ba ne. Duk wanda ya aikata mummunan aiki, to za a saka masa da shi, kuma ba zai sami wani masoyi ko mai taimako ba Allah ba



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 124

وَمَن يَعۡمَلۡ مِنَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ مِن ذَكَرٍ أَوۡ أُنثَىٰ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَدۡخُلُونَ ٱلۡجَنَّةَ وَلَا يُظۡلَمُونَ نَقِيرٗا

Kuma wanda ya yi wani aiki nagari, namiji ne ko mace, alhali yana mumini, to waxannan za su shiga Aljanna, kuma ba za a zalunce su gwargwadon xigon bayan qwallon dabino ba



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 125

وَمَنۡ أَحۡسَنُ دِينٗا مِّمَّنۡ أَسۡلَمَ وَجۡهَهُۥ لِلَّهِ وَهُوَ مُحۡسِنٞ وَٱتَّبَعَ مِلَّةَ إِبۡرَٰهِيمَ حَنِيفٗاۗ وَٱتَّخَذَ ٱللَّهُ إِبۡرَٰهِيمَ خَلِيلٗا

Kuma wane ne mafi kyawun addini fiye da wanda ya miqa fuskarsa ga Allah, yana kuma mai kaxaita Allah, sannan ya bi addinin Ibrahimu yana mai karkacewa duk wata varna? Allah kuwa Ya riqi Ibrahimu a matsayin badaxayi



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 126

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٖ مُّحِيطٗا

Kuma abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa duk na Allah ne. Kuma Allah Ya kasance Yana kewaye da (sanin) komai



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 127

وَيَسۡتَفۡتُونَكَ فِي ٱلنِّسَآءِۖ قُلِ ٱللَّهُ يُفۡتِيكُمۡ فِيهِنَّ وَمَا يُتۡلَىٰ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ فِي يَتَٰمَى ٱلنِّسَآءِ ٱلَّـٰتِي لَا تُؤۡتُونَهُنَّ مَا كُتِبَ لَهُنَّ وَتَرۡغَبُونَ أَن تَنكِحُوهُنَّ وَٱلۡمُسۡتَضۡعَفِينَ مِنَ ٱلۡوِلۡدَٰنِ وَأَن تَقُومُواْ لِلۡيَتَٰمَىٰ بِٱلۡقِسۡطِۚ وَمَا تَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِهِۦ عَلِيمٗا

Kuma suna neman fatawarka game da lamarin mata. Ka ce: “Allah ne Yake ba ku fatawa game da lamarinsu da kuma abin da ake karanta muku a cikin Littafi dangane da marayu mata waxanda ba kwa iya ba su sadakinsu cikakke, ga shi kuma kuna kwaxayin ku aure su; hakanan da kuma (dukiyar) yara masu rauni. Kuma ku tsaya wajen kula da (dukiyar) marayu ta hanyar adalci. Kuma duk abin da kuka aikata na alheri, to lalle Allah Yana sane da shi.”



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 128

وَإِنِ ٱمۡرَأَةٌ خَافَتۡ مِنۢ بَعۡلِهَا نُشُوزًا أَوۡ إِعۡرَاضٗا فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡهِمَآ أَن يُصۡلِحَا بَيۡنَهُمَا صُلۡحٗاۚ وَٱلصُّلۡحُ خَيۡرٞۗ وَأُحۡضِرَتِ ٱلۡأَنفُسُ ٱلشُّحَّۚ وَإِن تُحۡسِنُواْ وَتَتَّقُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٗا

Kuma idan wata mace ta ji tsoron burtsewa daga mijinta, ko bijirewa, to babu laifi su yi sulhu a tsakaninsu. Kuma yin sulhu shi ya fi alheri. Kuma an kimsa wa rayuka tsananin rowa. Idan kuka kyautata, kuma kuka yi taqawa, to lalle Allah Ya kasance Masanin abin da kuke aikatawa ne



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 129

وَلَن تَسۡتَطِيعُوٓاْ أَن تَعۡدِلُواْ بَيۡنَ ٱلنِّسَآءِ وَلَوۡ حَرَصۡتُمۡۖ فَلَا تَمِيلُواْ كُلَّ ٱلۡمَيۡلِ فَتَذَرُوهَا كَٱلۡمُعَلَّقَةِۚ وَإِن تُصۡلِحُواْ وَتَتَّقُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma ba za ku iya yin adalci (na soyayya) a tsakankanin mata ba, ko da kuna matuqar son yin hakan. To kada ku karkata, karkata ta gaba xaya, ta yadda za ku qyale xayar kamar ratayayya[1]. Amma idan za ku kyautata kuma ku yi taqawa, to lalle Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai


1- Watau su karkata ga xaya su qyale xayar a rataye, ita ba a sake ta ba ita kuma ba mai jin daxin aure ba.


Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 130

وَإِن يَتَفَرَّقَا يُغۡنِ ٱللَّهُ كُلّٗا مِّن سَعَتِهِۦۚ وَكَانَ ٱللَّهُ وَٰسِعًا حَكِيمٗا

Idan kuwa suka rabu, to Allah zai wadatar da kowannensu daga yalwarsa. Kuma Allah Ya kasance Mayalwaci ne, Mai yawan hikima



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 131

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۗ وَلَقَدۡ وَصَّيۡنَا ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ مِن قَبۡلِكُمۡ وَإِيَّاكُمۡ أَنِ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَۚ وَإِن تَكۡفُرُواْ فَإِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَنِيًّا حَمِيدٗا

Kuma duk abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne. Kuma haqiqa Mun yi wasiyya ga waxanda Muka bai wa Littafi gabaninku da ku kanku cewa, ku ji tsoron Allah. Idan kuwa kuka kafirce, to lalle abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa duka na Allah ne. Kuma Allah Ya kasance Mawadaci ne, Sha-yabo



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 132

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ وَكِيلًا

Kuma duk abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne. kuma Allah Ya isa Abin dogaro



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 133

إِن يَشَأۡ يُذۡهِبۡكُمۡ أَيُّهَا ٱلنَّاسُ وَيَأۡتِ بِـَٔاخَرِينَۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ ذَٰلِكَ قَدِيرٗا

Idan Ya ga dama sai Ya tafiyar da ku, ya ku mutane, kuma Ya kawo waxansu daban. Allah kuwa Ya kasance Mai iko ne a kan hakan



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 134

مَّن كَانَ يُرِيدُ ثَوَابَ ٱلدُّنۡيَا فَعِندَ ٱللَّهِ ثَوَابُ ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ سَمِيعَۢا بَصِيرٗا

Duk wanda ya kasance yana son ladan duniya, to ladan duniya da na lahira duk a hannun Allah suke. Kuma Allah Ya kasance Mai ji ne, Mai gani



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 135

۞يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُونُواْ قَوَّـٰمِينَ بِٱلۡقِسۡطِ شُهَدَآءَ لِلَّهِ وَلَوۡ عَلَىٰٓ أَنفُسِكُمۡ أَوِ ٱلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَۚ إِن يَكُنۡ غَنِيًّا أَوۡ فَقِيرٗا فَٱللَّهُ أَوۡلَىٰ بِهِمَاۖ فَلَا تَتَّبِعُواْ ٱلۡهَوَىٰٓ أَن تَعۡدِلُواْۚ وَإِن تَلۡوُۥٓاْ أَوۡ تُعۡرِضُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku zamo masu tsayawa da adalci, kuna masu ba da shaida don Allah, ko da kuwa a kan kawunanku ne ko a kan mahaifanku ko a kan dangi makusanta. Idan ya kasance mawadaci ne ko matalauci, to Allah Shi ne Ya fi sanin abin da ya fi cancanta gare su[1]; don haka kada ku bi son zuciyarku ku qi yin adalci. Idan kuwa kuka karkatar da shaida ko kuka qi ba da ita, to lalle Allah Ya kasance Mai cikakken sanin abin da kuke aikatawa ne


1- Watau da mai wadata da matalauci duk al'amuransu na ga Allah, ya fi kowa sanin abin da ya fi zama maslaha a gare su.


Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 136

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ ءَامِنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلَّذِي نَزَّلَ عَلَىٰ رَسُولِهِۦ وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ مِن قَبۡلُۚ وَمَن يَكۡفُرۡ بِٱللَّهِ وَمَلَـٰٓئِكَتِهِۦ وَكُتُبِهِۦ وَرُسُلِهِۦ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ فَقَدۡ ضَلَّ ضَلَٰلَۢا بَعِيدًا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi imani[1] da Allah da Manzonsa da Littafin da Ya saukar ga Manzonsa da Littafin da Ya saukar gabaninsa. Duk wanda kuwa ya kafirce wa Allah da mala’ikunsa da littattafansa da manzanninsa da ranar qarshe, to haqiqa ya vace vata mai nisa


1- Watau ku tsaya qyam a kan imaninsu da Allah da Annabinsa (), su riqe addininsu da kyau.


Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 137

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ثُمَّ كَفَرُواْ ثُمَّ ءَامَنُواْ ثُمَّ كَفَرُواْ ثُمَّ ٱزۡدَادُواْ كُفۡرٗا لَّمۡ يَكُنِ ٱللَّهُ لِيَغۡفِرَ لَهُمۡ وَلَا لِيَهۡدِيَهُمۡ سَبِيلَۢا

Lalle waxanda suka yi imani, sannan daga baya suka kafirce, sannan kuma suka qara yin imani, sannan suka kafirce, sannan suka qara kafirci, waxannan Allah ba zai yi musu gafara ba, ba kuma zai shiryar da su tafarki madaidaici ba



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 138

بَشِّرِ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ بِأَنَّ لَهُمۡ عَذَابًا أَلِيمًا

Ka yi albishir ga munafuqai cewa, suna da wata azaba mai raxaxi



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 139

ٱلَّذِينَ يَتَّخِذُونَ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۚ أَيَبۡتَغُونَ عِندَهُمُ ٱلۡعِزَّةَ فَإِنَّ ٱلۡعِزَّةَ لِلَّهِ جَمِيعٗا

Su ne waxanda suke riqar kafirai a matsayin masoya, su qyale muminai. Shin suna neman wata xaukaka ce a wurinsu? To lalle xaukaka gaba xaya ta Allah ce[1]


1- Watau shi ne yake bayar da girma, kuma ga muminai kaxai yake ba da shi, don haka munafukai ba za su same shi ba.


Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 140

وَقَدۡ نَزَّلَ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ أَنۡ إِذَا سَمِعۡتُمۡ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ يُكۡفَرُ بِهَا وَيُسۡتَهۡزَأُ بِهَا فَلَا تَقۡعُدُواْ مَعَهُمۡ حَتَّىٰ يَخُوضُواْ فِي حَدِيثٍ غَيۡرِهِۦٓ إِنَّكُمۡ إِذٗا مِّثۡلُهُمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ جَامِعُ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱلۡكَٰفِرِينَ فِي جَهَنَّمَ جَمِيعًا

Kuma haqiqa Ya saukar muku a cikin littafi[1] cewa, idan kuka ji ayoyin Allah ana kafirce musu, ana izgili da su, to kar ku zauna tare da su har sai sun shiga cikin wani zancen daban ba wannan ba. Lalle in har kuka zauna tare da su, to kun zama kamarsu. Lalle Allah Mai tattara munafuqai ne da kafirai cikin wutar Jahannama gaba xaya


1- Watau a cikin Alqur’ani a Suratul An’am, aya ta 68 inda Allah ya haramta wa muminai zama a inda ake yi wa shari’ar Allah izgili da rashin kunya.


Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 141

ٱلَّذِينَ يَتَرَبَّصُونَ بِكُمۡ فَإِن كَانَ لَكُمۡ فَتۡحٞ مِّنَ ٱللَّهِ قَالُوٓاْ أَلَمۡ نَكُن مَّعَكُمۡ وَإِن كَانَ لِلۡكَٰفِرِينَ نَصِيبٞ قَالُوٓاْ أَلَمۡ نَسۡتَحۡوِذۡ عَلَيۡكُمۡ وَنَمۡنَعۡكُم مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۚ فَٱللَّهُ يَحۡكُمُ بَيۡنَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۚ وَلَن يَجۡعَلَ ٱللَّهُ لِلۡكَٰفِرِينَ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ سَبِيلًا

Su ne waxanda suke fakon ku, idan kun sami wata nasara daga Allah sai su ce: “Shin ashe ba tare da ku muke ba?” Kuma idan kafirai ne suka samu wata nasara, sai su ce: “Ashe ba mu muka sami dama a kanku ba (amma muka qyale ku), kuma muka kare ku daga muminai?” To lalle Allah zai yi hukunci a tsakaninku ranar alqiyama, kuma Allah ba zai tava ba wa kafirai wata dama ba a kan muminai[1]


1- Watau ba zai tava ba su nasara a kan muminai gaba xaya ba, sai dai ta wani wuri ban da wani wuri. Hakanan a lahira ba zai ba su hujjar da za su rinjayi muminai da ita ba.


Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 142

إِنَّ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ يُخَٰدِعُونَ ٱللَّهَ وَهُوَ خَٰدِعُهُمۡ وَإِذَا قَامُوٓاْ إِلَى ٱلصَّلَوٰةِ قَامُواْ كُسَالَىٰ يُرَآءُونَ ٱلنَّاسَ وَلَا يَذۡكُرُونَ ٱللَّهَ إِلَّا قَلِيلٗا

Lalle munafuqai suna yaudarar Allah, alhali kuwa Shi Mai mayar musu da sakamakon yaudararsu ne; kuma idan sun tashi zuwa salla, za su tashi suna masu kasala ne, suna yin aiki don mutane su gani, kuma ba su ambaton Allah sai kaxan



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 143

مُّذَبۡذَبِينَ بَيۡنَ ذَٰلِكَ لَآ إِلَىٰ هَـٰٓؤُلَآءِ وَلَآ إِلَىٰ هَـٰٓؤُلَآءِۚ وَمَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَلَن تَجِدَ لَهُۥ سَبِيلٗا

Suna ta kai-kawo tsakanin haka (kafirci da imani), su ba sa tare da waxanan, kuma ba sa tare da waxancan. Duk wanda Allah Ya vatar da shi kuwa, to babu yadda za ka iya sama masa wani tafarki na shiriya



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 144

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۚ أَتُرِيدُونَ أَن تَجۡعَلُواْ لِلَّهِ عَلَيۡكُمۡ سُلۡطَٰنٗا مُّبِينًا

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi kafirai a matsayin masoya ku bar muminai. Shin kuna so ku ba wa Allah wata hujja mabayyaniya ne a kanku?



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 145

إِنَّ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ فِي ٱلدَّرۡكِ ٱلۡأَسۡفَلِ مِنَ ٱلنَّارِ وَلَن تَجِدَ لَهُمۡ نَصِيرًا

Lalle munafuqai suna cikin matakin qarshe na can qarqashin wuta, kuma ba za ka tava sama musu wani mataimaki ba



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 146

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ وَأَصۡلَحُواْ وَٱعۡتَصَمُواْ بِٱللَّهِ وَأَخۡلَصُواْ دِينَهُمۡ لِلَّهِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ مَعَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۖ وَسَوۡفَ يُؤۡتِ ٱللَّهُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ أَجۡرًا عَظِيمٗا

Sai fa waxanda suka tuba, kuma suka gyara aikinsu, kuma suka yi riqo ga igiyar Allah; kuma suka tsantsanta addininsu don Allah; to waxannan suna tare da muminai; kuma Allah zai bai wa muminai lada mai girma



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 147

مَّا يَفۡعَلُ ٱللَّهُ بِعَذَابِكُمۡ إِن شَكَرۡتُمۡ وَءَامَنتُمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ شَاكِرًا عَلِيمٗا

Me Allah zai yi da azabtar da ku idan har kun yi godiya kuma kun yi imani? Allah kuwa Ya kasance Mai godiya ne, Mai yawan sani



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 148

۞لَّا يُحِبُّ ٱللَّهُ ٱلۡجَهۡرَ بِٱلسُّوٓءِ مِنَ ٱلۡقَوۡلِ إِلَّا مَن ظُلِمَۚ وَكَانَ ٱللَّهُ سَمِيعًا عَلِيمًا

Allah ba Ya son bayyana mummunan zance, sai dai wanda aka zalunce shi. Kuma Allah Ya kasance Mai ji ne, Mai yawan sani



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 149

إِن تُبۡدُواْ خَيۡرًا أَوۡ تُخۡفُوهُ أَوۡ تَعۡفُواْ عَن سُوٓءٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَفُوّٗا قَدِيرًا

Idan har kuka bayyana wani alheri ko kuka voye shi ko kuma kuka yi afuwa game da wata cutarwa, to lalle Allah Ya kasance Mai yawan afuwa ne, Mai cikakken iko



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 150

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَكۡفُرُونَ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦ وَيُرِيدُونَ أَن يُفَرِّقُواْ بَيۡنَ ٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦ وَيَقُولُونَ نُؤۡمِنُ بِبَعۡضٖ وَنَكۡفُرُ بِبَعۡضٖ وَيُرِيدُونَ أَن يَتَّخِذُواْ بَيۡنَ ذَٰلِكَ سَبِيلًا

Lalle waxanda suke kafirce wa Allah da manzanninsa, kuma suke nufin su nuna bambanci tsakanin Allah da manzanninsa, kuma suna cewa: “Mun yi imani da wasu, mun kuma kafirce wa wasu,” kuma suna son su riqi wani tafarki tsakanin wannan (imani da kafirci)