Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 91

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَمَاتُواْ وَهُمۡ كُفَّارٞ فَلَن يُقۡبَلَ مِنۡ أَحَدِهِم مِّلۡءُ ٱلۡأَرۡضِ ذَهَبٗا وَلَوِ ٱفۡتَدَىٰ بِهِۦٓۗ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ وَمَا لَهُم مِّن نَّـٰصِرِينَ

Lalle waxanda suka kafirta, kuma suka mutu alhali suna kafirai, to ba za a tava karvar cikin qasa na zinare daga xayansu ba, ko da zai fanshi kansa da shi. Waxannan suna da wata azaba mai raxaxi kuma ba su da wasu mataimaka



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 92

لَن تَنَالُواْ ٱلۡبِرَّ حَتَّىٰ تُنفِقُواْ مِمَّا تُحِبُّونَۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِن شَيۡءٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٞ

Ba za ku tava dacewa da aiki na alheri ba har sai kun ciyar daga abin da kuke so, kuma abin da duk kuka ciyar kowane iri ne, to lalle Allah Yana sane da shi



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 93

۞كُلُّ ٱلطَّعَامِ كَانَ حِلّٗا لِّبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ إِلَّا مَا حَرَّمَ إِسۡرَـٰٓءِيلُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ مِن قَبۡلِ أَن تُنَزَّلَ ٱلتَّوۡرَىٰةُۚ قُلۡ فَأۡتُواْ بِٱلتَّوۡرَىٰةِ فَٱتۡلُوهَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Duk wani abinci ya kasance halal ne ga Banu Israila sai abin da shi Isra’ilu[1] ya haramta wa kansa tun kafin a saukar da Attaura. Ka ce: “To ku zo da Attaura, sai ku karanta ta in kun kasance masu gaskiya.”


1- Isra’ilu: shi ne Annabi Ya’aqub (). Ya haramta wa kansa ne cin naman raquma da shan nononsu. Sannan daga baya su ma ‘ya’yansa suka yi koyi da shi.


Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 94

فَمَنِ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ ٱلۡكَذِبَ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

To duk wanda ya qirqiri qarya ya jingina wa Allah bayan wannan, to waxannan su ne azzalumai



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 95

قُلۡ صَدَقَ ٱللَّهُۗ فَٱتَّبِعُواْ مِلَّةَ إِبۡرَٰهِيمَ حَنِيفٗاۖ وَمَا كَانَ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Ka ce: “Allah Ya yi gaskiya. Don haka ku bi addinin Ibrahimu, mai karkace wa varna, kuma bai tava zama xaya daga cikin mushirikai ba.”



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 96

إِنَّ أَوَّلَ بَيۡتٖ وُضِعَ لِلنَّاسِ لَلَّذِي بِبَكَّةَ مُبَارَكٗا وَهُدٗى لِّلۡعَٰلَمِينَ

Lalle farkon xaki da aka tanada don mutane (su yi ibada a cikinsa) shi ne wanda yake cikin Bakka[1], (xaki ne) mai albarka, kuma shiriya ne ga talikai


1- Watau Xakin Ka’aba da yake garin Makka mai alfarma.


Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 97

فِيهِ ءَايَٰتُۢ بَيِّنَٰتٞ مَّقَامُ إِبۡرَٰهِيمَۖ وَمَن دَخَلَهُۥ كَانَ ءَامِنٗاۗ وَلِلَّهِ عَلَى ٱلنَّاسِ حِجُّ ٱلۡبَيۡتِ مَنِ ٱسۡتَطَاعَ إِلَيۡهِ سَبِيلٗاۚ وَمَن كَفَرَ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَنِيٌّ عَنِ ٱلۡعَٰلَمِينَ

A cikinsa akwai ayoyi bayyanannu, (kuma akwai) Maqamu Ibrahimu; wanda duk ya shige shi ya zama amintacce. Kuma Allah Ya wajabta wa mutane ziyarar wannan xakin ga wanda ya sami iko[1]. Wanda kuwa ya kafirce, to lalle Allah Mawadaci ne ga barin talikai


1- Allah ya farlanta ziyarar wannan Xaki domin aikin hajji sau xaya a rayuwa ga duk wanda ya sami iko na lafiya da guzuri da abin hawa da amincin hanya.


Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 98

قُلۡ يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ لِمَ تَكۡفُرُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَٱللَّهُ شَهِيدٌ عَلَىٰ مَا تَعۡمَلُونَ

Ka ce: “Ya ku Ma’abota Littafi, don me kuke kafirce wa ayoyin Allah, kuma alhalin Allah Mai ba da shaida ne ga abin da kuke aikatawa?”



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 99

قُلۡ يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ لِمَ تَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ مَنۡ ءَامَنَ تَبۡغُونَهَا عِوَجٗا وَأَنتُمۡ شُهَدَآءُۗ وَمَا ٱللَّهُ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ

Ka ce: “Ya ku Ma’abota Littafi, don me kuke kange wanda ya yi imani daga hanyar Allah, kuna son ta zamo karkatacciya, kuma alhali ku da kanku masu shaida ne, kuma Allah ba gafalalle ne game da abin da kuke aikatawa ba?”



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 100

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تُطِيعُواْ فَرِيقٗا مِّنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ يَرُدُّوكُم بَعۡدَ إِيمَٰنِكُمۡ كَٰفِرِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka bi wani vangare na waxanda aka ba wa Littafi, to za su mayar da ku kafirai bayan imaninku



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 101

وَكَيۡفَ تَكۡفُرُونَ وَأَنتُمۡ تُتۡلَىٰ عَلَيۡكُمۡ ءَايَٰتُ ٱللَّهِ وَفِيكُمۡ رَسُولُهُۥۗ وَمَن يَعۡتَصِم بِٱللَّهِ فَقَدۡ هُدِيَ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Ta yaya kuma za ku kafirce, ga shi kuwa ana karanta muku ayoyin Allah, kuma Manzonsa yana tare da ku? Duk kuwa wanda ya riqi Allah, to haqiqa an shiryar da shi tafarki madaidaici



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 102

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ حَقَّ تُقَاتِهِۦ وَلَا تَمُوتُنَّ إِلَّا وَأَنتُم مُّسۡلِمُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi taqawa ga Allah haqiqanin taqawa, kuma lalle kada ku mutu face kuna Musulmi



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 103

وَٱعۡتَصِمُواْ بِحَبۡلِ ٱللَّهِ جَمِيعٗا وَلَا تَفَرَّقُواْۚ وَٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ إِذۡ كُنتُمۡ أَعۡدَآءٗ فَأَلَّفَ بَيۡنَ قُلُوبِكُمۡ فَأَصۡبَحۡتُم بِنِعۡمَتِهِۦٓ إِخۡوَٰنٗا وَكُنتُمۡ عَلَىٰ شَفَا حُفۡرَةٖ مِّنَ ٱلنَّارِ فَأَنقَذَكُم مِّنۡهَاۗ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمۡ ءَايَٰتِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ

Kuma ku yi riqo da igiyar Allah gaba xaya, kada kuma ku rarraba. Kuma ku tuna ni’imar Allah da Ya yi muku yayin da kuka zamo abokan gaban juna sai Ya haxa tsakanin zukatanku, sai kuka zamo ‘yan’uwan juna a sakamakon ni’imarsa, a da kuma kun kasance a kan gavar ramin wuta sai Ya tserar da ku daga gare ta. Kamar haka ne Allah Yake bayyana muku ayoyinsa don ku shiriya



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 104

وَلۡتَكُن مِّنكُمۡ أُمَّةٞ يَدۡعُونَ إِلَى ٱلۡخَيۡرِ وَيَأۡمُرُونَ بِٱلۡمَعۡرُوفِ وَيَنۡهَوۡنَ عَنِ ٱلۡمُنكَرِۚ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

A cikinku lalle a sami wata al’umma waxanda suke kira zuwa ga alheri, kuma suke umarni da kyakkyawa, kuma suke hana mummuna. Waxannan su ne masu rabauta



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 105

وَلَا تَكُونُواْ كَٱلَّذِينَ تَفَرَّقُواْ وَٱخۡتَلَفُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَهُمُ ٱلۡبَيِّنَٰتُۚ وَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٌ عَظِيمٞ

Kuma kada ku kasance kamar waxanda suka rarrabu, kuma suka sassava bayan hujjoji sun zo musu. Waxannan kuwa suna da azaba mai girma



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 106

يَوۡمَ تَبۡيَضُّ وُجُوهٞ وَتَسۡوَدُّ وُجُوهٞۚ فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ٱسۡوَدَّتۡ وُجُوهُهُمۡ أَكَفَرۡتُم بَعۡدَ إِيمَٰنِكُمۡ فَذُوقُواْ ٱلۡعَذَابَ بِمَا كُنتُمۡ تَكۡفُرُونَ

Ranar da waxansu fuskoki za su yi fari, waxansu fuskokin kuma za su yi baqi. Amma waxanda fuskokinsu suka yi baqi, (za a ce da su): “Shin ku ne kuka kafirce bayan imaninku? To ku xanxani azaba, saboda kafircin da kuka kasance kuna yi.”



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 107

وَأَمَّا ٱلَّذِينَ ٱبۡيَضَّتۡ وُجُوهُهُمۡ فَفِي رَحۡمَةِ ٱللَّهِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Amma waxanda fuskokinsu suka yi fari kuwa, to suna cikin rahamar Allah, suna masu dawwama a cikinta



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 108

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱللَّهِ نَتۡلُوهَا عَلَيۡكَ بِٱلۡحَقِّۗ وَمَا ٱللَّهُ يُرِيدُ ظُلۡمٗا لِّلۡعَٰلَمِينَ

Waxannan ayoyin Allah ne Muke karanta maka su da gaskiya. Kuma Allah ba Ya nufin zalunci ga talikai



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 109

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَإِلَى ٱللَّهِ تُرۡجَعُ ٱلۡأُمُورُ

Kuma duk abin da yake cikin sammai da qasa na Allah ne. Kuma zuwa ga Allah ne ake mayar da duk al’amura



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 110

كُنتُمۡ خَيۡرَ أُمَّةٍ أُخۡرِجَتۡ لِلنَّاسِ تَأۡمُرُونَ بِٱلۡمَعۡرُوفِ وَتَنۡهَوۡنَ عَنِ ٱلۡمُنكَرِ وَتُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِۗ وَلَوۡ ءَامَنَ أَهۡلُ ٱلۡكِتَٰبِ لَكَانَ خَيۡرٗا لَّهُمۚ مِّنۡهُمُ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَأَكۡثَرُهُمُ ٱلۡفَٰسِقُونَ

Ku ne mafi alherin al’umma waxanda aka fitar ga mutane, kuna umarni da kyakkyawan aiki, kuma kuna hana mummuna, kuma kuna yin imani da Allah. Da a ce kuwa Ma’abota Littafi za su yi imani da ya fi alheri a gare su. A cikinsu akwai muminai, amma mafiya yawansu fasiqai ne



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 111

لَن يَضُرُّوكُمۡ إِلَّآ أَذٗىۖ وَإِن يُقَٰتِلُوكُمۡ يُوَلُّوكُمُ ٱلۡأَدۡبَارَ ثُمَّ لَا يُنصَرُونَ

Ba za su tava iya cutar da ku ba sai dai cutarwa kaxan; kuma in da za su yaqe ku, sai sun juya muku baya, sannan ba za a taimake su ba



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 112

ضُرِبَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلذِّلَّةُ أَيۡنَ مَا ثُقِفُوٓاْ إِلَّا بِحَبۡلٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَحَبۡلٖ مِّنَ ٱلنَّاسِ وَبَآءُو بِغَضَبٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَضُرِبَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلۡمَسۡكَنَةُۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ كَانُواْ يَكۡفُرُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَيَقۡتُلُونَ ٱلۡأَنۢبِيَآءَ بِغَيۡرِ حَقّٖۚ ذَٰلِكَ بِمَا عَصَواْ وَّكَانُواْ يَعۡتَدُونَ

An haxa su da qasqanci a duk inda aka same su, sai dai waxanda suke riqe da wani alqawari daga Allah ko wani alqawari daga mutane, kuma sun dawo da wani fushi daga Allah, kuma an haxa su da talauci. Hakan kuwa saboda sun kasance suna kafirce wa ayoyin Allah, kuma suna kashe annabawa ba tare da wani haqqi ba, hakan yana faruwa ne saboda savo da suka yi, kuma sun kasance suna qetare iyaka



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 113

۞لَيۡسُواْ سَوَآءٗۗ مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ أُمَّةٞ قَآئِمَةٞ يَتۡلُونَ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ ءَانَآءَ ٱلَّيۡلِ وَهُمۡ يَسۡجُدُونَ

Ba dukansu ne suka zama xaya ba. Cikin Ma’abota Littafi akwai al’umma tsayayya, suna karanta Littafin Allah a cikin dare alhalin suna sujada



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 114

يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَيَأۡمُرُونَ بِٱلۡمَعۡرُوفِ وَيَنۡهَوۡنَ عَنِ ٱلۡمُنكَرِ وَيُسَٰرِعُونَ فِي ٱلۡخَيۡرَٰتِۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Suna yin imani da Allah da ranar qarshe, kuma suna umarni da kyakkyawan aiki, kuma suna hana mummuna, kuma suna hanzari wajen ayyukan alheri, waxannan kuwa suna cikin salihan bayi



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 115

وَمَا يَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَلَن يُكۡفَرُوهُۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلۡمُتَّقِينَ

Kuma duk abin da suka aikata na alheri, to ba za a hana musu ladansa ba. Kuma Allah Yana sane da masu taqawa



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 116

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَن تُغۡنِيَ عَنۡهُمۡ أَمۡوَٰلُهُمۡ وَلَآ أَوۡلَٰدُهُم مِّنَ ٱللَّهِ شَيۡـٔٗاۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Lalle waxanda suka kafirta, dukiyoyinsu da ‘ya’yansu ba za su wadatar da su komai ba a wurin Allah; kuma waxannan su ne ma’abota wuta; suna masu dawwama a cikinta



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 117

مَثَلُ مَا يُنفِقُونَ فِي هَٰذِهِ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا كَمَثَلِ رِيحٖ فِيهَا صِرٌّ أَصَابَتۡ حَرۡثَ قَوۡمٖ ظَلَمُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فَأَهۡلَكَتۡهُۚ وَمَا ظَلَمَهُمُ ٱللَّهُ وَلَٰكِنۡ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Misalin abin da suke ciyarwa a wannan rayuwa ta duniya kamar misalin iska ce mai tsananin sanyi, wadda ta auka kan shukar waxansu mutanen da suka zalunci kawunansu, sai ta lalata ta. Kuma Allah bai zalunce su ba, sai dai kawunansu suke zalunta



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 118

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ بِطَانَةٗ مِّن دُونِكُمۡ لَا يَأۡلُونَكُمۡ خَبَالٗا وَدُّواْ مَا عَنِتُّمۡ قَدۡ بَدَتِ ٱلۡبَغۡضَآءُ مِنۡ أَفۡوَٰهِهِمۡ وَمَا تُخۡفِي صُدُورُهُمۡ أَكۡبَرُۚ قَدۡ بَيَّنَّا لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi abokanan shawara waxanda ba a cikinku suke ba, ba za su sassauta muku mugunta ba, sun yi burin duk abin da zai quntata muku, haqiqa qiyayya ta bayyana daga bakunansu; amma abin da zukatansu suke voyewa ya fi girma. Haqiqa Mun bayyana muku ayoyi; in kun kasance kuna hankalta



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 119

هَـٰٓأَنتُمۡ أُوْلَآءِ تُحِبُّونَهُمۡ وَلَا يُحِبُّونَكُمۡ وَتُؤۡمِنُونَ بِٱلۡكِتَٰبِ كُلِّهِۦ وَإِذَا لَقُوكُمۡ قَالُوٓاْ ءَامَنَّا وَإِذَا خَلَوۡاْ عَضُّواْ عَلَيۡكُمُ ٱلۡأَنَامِلَ مِنَ ٱلۡغَيۡظِۚ قُلۡ مُوتُواْ بِغَيۡظِكُمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Sai ga shi ku xinnan kuna son su, su kuwa ba sa son ku, kuma ku kuna yin imani da Littattafai gaba xayansu, kuma idan sun gamu da ku, sai su ce: “Mun yi imani.” Idan kuma sun kevanta, sai su riqa cizon ‘yan yatsu a kanku saboda baqin ciki. Ka ce: “Sai dai ku mutu da baqin cikinku.” Lalle Allah Masanin abin da yake cikin qiraza ne



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 120

إِن تَمۡسَسۡكُمۡ حَسَنَةٞ تَسُؤۡهُمۡ وَإِن تُصِبۡكُمۡ سَيِّئَةٞ يَفۡرَحُواْ بِهَاۖ وَإِن تَصۡبِرُواْ وَتَتَّقُواْ لَا يَضُرُّكُمۡ كَيۡدُهُمۡ شَيۡـًٔاۗ إِنَّ ٱللَّهَ بِمَا يَعۡمَلُونَ مُحِيطٞ

Idan wani kyakkyawan abu ya same ku sai ya baqanta musu rai, amma idan wani mummunan abu ya same ku, sai su riqa farin ciki da shi; amma idan kuwa kuka yi haquri, kuma kuka yi taqawa, makircinsu ba zai cutar da ku komai ba. Lalle Allah Yana kewaye da sanin abin da suke aikatawa