Sourate: Suratus Saffat

Verset : 61

لِمِثۡلِ هَٰذَا فَلۡيَعۡمَلِ ٱلۡعَٰمِلُونَ

Don samun irin wannan lalle masu (kyakkyawan) aiki su yi aiki



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 62

أَذَٰلِكَ خَيۡرٞ نُّزُلًا أَمۡ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ

Shin wannan liyafa ita ce ta fi alheri ko kuwa bishiyar Zaqqum?



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 63

إِنَّا جَعَلۡنَٰهَا فِتۡنَةٗ لِّلظَّـٰلِمِينَ

Lalle Mu Mun sanya ta don ta zama fitina ga azzalumai



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 64

إِنَّهَا شَجَرَةٞ تَخۡرُجُ فِيٓ أَصۡلِ ٱلۡجَحِيمِ

Lalle ita wata bishiya ce da take fitowa a tsakiyar wutar Jahima



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 65

طَلۡعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَٰطِينِ

‘Ya’yanta kai ka ce kawunan shaixanu ne



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 66

فَإِنَّهُمۡ لَأٓكِلُونَ مِنۡهَا فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ

To su lalle za su ci daga gare ta, za su kuma cika cikkuna da ita



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 67

ثُمَّ إِنَّ لَهُمۡ عَلَيۡهَا لَشَوۡبٗا مِّنۡ حَمِيمٖ

Sannan kuma suna da wani gauraye na tafasasshen ruwa a kanta



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 68

ثُمَّ إِنَّ مَرۡجِعَهُمۡ لَإِلَى ٱلۡجَحِيمِ

Sannan kuma lalle makomarsu wutar Jahima ce



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 69

إِنَّهُمۡ أَلۡفَوۡاْ ءَابَآءَهُمۡ ضَآلِّينَ

Lalle su sun sami iyayensu vatattu



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 70

فَهُمۡ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمۡ يُهۡرَعُونَ

Sai suka riqa gaggawar bin sawunsu



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 71

وَلَقَدۡ ضَلَّ قَبۡلَهُمۡ أَكۡثَرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Haqiqa kafin su mafi yawan mutanen farko sun vata



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 72

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ

Kuma haqiqa Mun aiko masu gargaxi a cikinsu



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 73

فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُنذَرِينَ

To ka dubi yadda qarshen waxanda aka yi wa gargaxi ya kasance



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 74

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai dai bayin Allah waxanda aka tsarkake



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 75

وَلَقَدۡ نَادَىٰنَا نُوحٞ فَلَنِعۡمَ ٱلۡمُجِيبُونَ

Kuma haqiqa Nuhu ya roqe Mu, to madalla da Masu amsawa



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 76

وَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

Muka kuma tserar da shi tare da iyalinsa daga baqin ciki mai girma



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 77

وَجَعَلۡنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلۡبَاقِينَ

Muka kuma sanya zuriyarsa su ne suka wanzu



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 78

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare shi ga ‘yan baya



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 79

سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٖ فِي ٱلۡعَٰلَمِينَ

Aminci ya tabbata ga Nuhu a cikin talikai



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 80

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 81

إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle shi yana daga bayinmu muminai



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 82

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 83

۞وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبۡرَٰهِيمَ

Lalle kuma Ibrahimu yana daga mabiya addininsa



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 84

إِذۡ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلۡبٖ سَلِيمٍ

A yayin da ya zo wa Ubangijinsa da lafiyayyar zuciya



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 85

إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَاذَا تَعۡبُدُونَ

Lokacin da ya ce da babansa da kuma mutanensa: “Me kuke bauta wa ne?



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 86

أَئِفۡكًا ءَالِهَةٗ دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ

“Yanzu iyayen giji na qarya ba Allah ba kuke nufi?



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 87

فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“To mene ne tsammaninku game da Ubangijin talikai?”



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 88

فَنَظَرَ نَظۡرَةٗ فِي ٱلنُّجُومِ

Sai ya yi duba a cikin taurari, duba na tunani



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 89

فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٞ

Sannan ya ce: “Lalle ni fa ba ni da lafiya.”



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 90

فَتَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ مُدۡبِرِينَ

Sai suka juya daga wurinsa suna masu ba da baya