Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 61

وَلَئِن سَأَلۡتَهُم مَّنۡ خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَسَخَّرَ ٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَ لَيَقُولُنَّ ٱللَّهُۖ فَأَنَّىٰ يُؤۡفَكُونَ

Tabbas da za ka tambaye su: “Wane ne ya halicci sammai da qasa, ya kuma hore rana da wata?” To tabbas za su ce: “Allah ne.” To ta yaya ake karkatar da su (daga kaxaita Shi)?



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 62

ٱللَّهُ يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦ وَيَقۡدِرُ لَهُۥٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Allah Yana shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama daga bayinsa, Ya kuma quntata masa. Lalle Allah Masanin komai ne



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 63

وَلَئِن سَأَلۡتَهُم مَّن نَّزَّلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَحۡيَا بِهِ ٱلۡأَرۡضَ مِنۢ بَعۡدِ مَوۡتِهَا لَيَقُولُنَّ ٱللَّهُۚ قُلِ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يَعۡقِلُونَ

Kuma tabbas da za ka tambaye su: “Wane ne ya saukar da ruwa daga sama, sai ya raya qasa da shi bayan mutuwarta?” Lalle za su ce: “Allah ne.” Ka ce (da su): “Alhamdu Lillahi.” A’a, yawancinsu dai ba sa hankalta



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 64

وَمَا هَٰذِهِ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَآ إِلَّا لَهۡوٞ وَلَعِبٞۚ وَإِنَّ ٱلدَّارَ ٱلۡأٓخِرَةَ لَهِيَ ٱلۡحَيَوَانُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Kuma wannan rayuwar duniya ba komai ba ce face sharholiya da wasa. Kuma lalle (rayuwar) gidan lahira ita ce rayuwa, in da sun kasance sun sani



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 65

فَإِذَا رَكِبُواْ فِي ٱلۡفُلۡكِ دَعَوُاْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ فَلَمَّا نَجَّىٰهُمۡ إِلَى ٱلۡبَرِّ إِذَا هُمۡ يُشۡرِكُونَ

To idan suka hau jiragen ruwa sukan roqi Allah suna masu tsantsanta addini a gare Shi; to lokacin da Ya tserar da su zuwa tudu sai ga su suna yin shirka



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 66

لِيَكۡفُرُواْ بِمَآ ءَاتَيۡنَٰهُمۡ وَلِيَتَمَتَّعُواْۚ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ

Don su kafirce wa abin da Muka ba su, kuma don su ji daxi; to da sannu za su sani



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 67

أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ أَنَّا جَعَلۡنَا حَرَمًا ءَامِنٗا وَيُتَخَطَّفُ ٱلنَّاسُ مِنۡ حَوۡلِهِمۡۚ أَفَبِٱلۡبَٰطِلِ يُؤۡمِنُونَ وَبِنِعۡمَةِ ٱللَّهِ يَكۡفُرُونَ

Yanzu ba su ga cewa, Mu Muka sanya musu Harami amintacce ba, alhali kuwa ana ta fauce mutane a kewayensu[1]? Shin yanzu sa riqa yin imani da qarya su kuma riqa kafirce wa ni’imar Allah?


1- Watau ana ta kai musu hare-hare ana kashe su, ana kama su ribatattun yaqi, a mayar da su bayi.


Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 68

وَمَنۡ أَظۡلَمُ مِمَّنِ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبًا أَوۡ كَذَّبَ بِٱلۡحَقِّ لَمَّا جَآءَهُۥٓۚ أَلَيۡسَ فِي جَهَنَّمَ مَثۡوٗى لِّلۡكَٰفِرِينَ

Wane ne ya fi zalunci kamar wanda ya qaga wa Allah qarya ko kuma ya qaryata gaskiya lokacin da ta zo masa? Yanzu ashe babu mazaunar kafirai a cikin Jahannama?



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 69

وَٱلَّذِينَ جَٰهَدُواْ فِينَا لَنَهۡدِيَنَّهُمۡ سُبُلَنَاۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ لَمَعَ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Waxanda kuma suka yi jihadi saboda Mu to tabbas za Mu shiryar da su hanyoyinmu[1], kuma lalle Allah Yana tare da masu kyautatawa


1- Watau hanyoyin Allah na alheri, su samu dacewa da bin tafarki madaidaici.