Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 61

قَالَ لَهُم مُّوسَىٰ وَيۡلَكُمۡ لَا تَفۡتَرُواْ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبٗا فَيُسۡحِتَكُم بِعَذَابٖۖ وَقَدۡ خَابَ مَنِ ٱفۡتَرَىٰ

Musa ya ce da su: “Kaiconku! Kada fa ku qirqira wa Allah qarya, sai Ya hallaka ku da azaba; haqiqa kuwa wanda ya qirqira (masa qarya) to ya tave.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 62

فَتَنَٰزَعُوٓاْ أَمۡرَهُم بَيۡنَهُمۡ وَأَسَرُّواْ ٱلنَّجۡوَىٰ

Sai suka tattauna al’amarinsu a tsakaninsu, suka kuma gana a asirce



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 63

قَالُوٓاْ إِنۡ هَٰذَٰنِ لَسَٰحِرَٰنِ يُرِيدَانِ أَن يُخۡرِجَاكُم مِّنۡ أَرۡضِكُم بِسِحۡرِهِمَا وَيَذۡهَبَا بِطَرِيقَتِكُمُ ٱلۡمُثۡلَىٰ

Suka ce: “Lalle waxannan biyun (Musa da Haruna) tabbas matsafa ne, suna so ne su fitar da ku daga qasarku da tsafinsu, su kuma tafiyar da kyakkyawar hanyarku (ta rayuwa)



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 64

فَأَجۡمِعُواْ كَيۡدَكُمۡ ثُمَّ ٱئۡتُواْ صَفّٗاۚ وَقَدۡ أَفۡلَحَ ٱلۡيَوۡمَ مَنِ ٱسۡتَعۡلَىٰ

“Sai ku yiwo shiri haxaxxe sannan ku zo sahu-sahu. Haqiqa yau kam wanda ya yi nasara ya rabauta!”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 65

قَالُواْ يَٰمُوسَىٰٓ إِمَّآ أَن تُلۡقِيَ وَإِمَّآ أَن نَّكُونَ أَوَّلَ مَنۡ أَلۡقَىٰ

Suka ce: “Ya Musa, ko dai ka jefa (naka) ko kuma mu mu fara jefa (namu).”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 66

قَالَ بَلۡ أَلۡقُواْۖ فَإِذَا حِبَالُهُمۡ وَعِصِيُّهُمۡ يُخَيَّلُ إِلَيۡهِ مِن سِحۡرِهِمۡ أَنَّهَا تَسۡعَىٰ

Ya ce: “A’a, ku (fara) jefawa.” To saboda sihirinsu sai ga igiyoyinsu da sandunansu ana suranta masa cewa su (macizai ne) suna sauri



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 67

فَأَوۡجَسَ فِي نَفۡسِهِۦ خِيفَةٗ مُّوسَىٰ

Sai Musa ya voye (wani abu) na tsoro a ransa



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 68

قُلۡنَا لَا تَخَفۡ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Muka ce: “Kada ka ji tsoro, lalle kai kake da rinjaye



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 69

وَأَلۡقِ مَا فِي يَمِينِكَ تَلۡقَفۡ مَا صَنَعُوٓاْۖ إِنَّمَا صَنَعُواْ كَيۡدُ سَٰحِرٖۖ وَلَا يُفۡلِحُ ٱلسَّاحِرُ حَيۡثُ أَتَىٰ

“Kuma ka jefar da abin da yake hannunka na dama, za ta haxiye abin da suka aikata; lalle abin da suka aikata makircin matsafi ne; matsafi kuwa ba ya rabauta duk ta inda ya zo.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 70

فَأُلۡقِيَ ٱلسَّحَرَةُ سُجَّدٗا قَالُوٓاْ ءَامَنَّا بِرَبِّ هَٰرُونَ وَمُوسَىٰ

Sai matsafan suka faxi suna sujjada[1] suka ce: “Mun yi imani da Ubangijin Haruna da Musa!”


1- Watau bayan sun fahimci cewa abin da Musa () ya zo da shi ba tsafi ba ne, wani abu ne daga Allah.


Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 71

قَالَ ءَامَنتُمۡ لَهُۥ قَبۡلَ أَنۡ ءَاذَنَ لَكُمۡۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِي عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحۡرَۖ فَلَأُقَطِّعَنَّ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَرۡجُلَكُم مِّنۡ خِلَٰفٖ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمۡ فِي جُذُوعِ ٱلنَّخۡلِ وَلَتَعۡلَمُنَّ أَيُّنَآ أَشَدُّ عَذَابٗا وَأَبۡقَىٰ

(Fir’auna) ya ce: “Yanzu kwa yi imani da shi tun kafin in yi muku izini? Lalle shi ne babbanku wanda ya koya muku tsafi; to lalle zan yayyanke hannayenku da qafafuwanku a tarnaqe (wato hannun dama da qafar hagu), kuma tabbas zan gicciye ku a kan kututturen dabino, lalle kuma tabbas za ku san wane ne tsakanin ni da shi wanda ya fi tsananin azaba kuma ta fi xorewa



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 72

قَالُواْ لَن نُّؤۡثِرَكَ عَلَىٰ مَا جَآءَنَا مِنَ ٱلۡبَيِّنَٰتِ وَٱلَّذِي فَطَرَنَاۖ فَٱقۡضِ مَآ أَنتَ قَاضٍۖ إِنَّمَا تَقۡضِي هَٰذِهِ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَآ

Suka ce: “Ba za mu fifita ka ba a kan abin da ya zo mana na (ayoyi) mabayyana, da kuma a kan wanda Ya halicce mu. Sai ka hukunta duk abin da za ka hukunta; za ka yi hukunci ne kawai a wannnan rayuwar ta duniya



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 73

إِنَّآ ءَامَنَّا بِرَبِّنَا لِيَغۡفِرَ لَنَا خَطَٰيَٰنَا وَمَآ أَكۡرَهۡتَنَا عَلَيۡهِ مِنَ ٱلسِّحۡرِۗ وَٱللَّهُ خَيۡرٞ وَأَبۡقَىٰٓ

“Lalle mu kam mun yi imani da Ubangijinmu don Ya gafarta mana laifukanmu da kuma abin da ka tilasta mu a kansa na tsafi. Allah kuwa Shi ne Mafi alherin (sakamako), kuma Shi ne Mafi dawwamar (azaba).”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 74

إِنَّهُۥ مَن يَأۡتِ رَبَّهُۥ مُجۡرِمٗا فَإِنَّ لَهُۥ جَهَنَّمَ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحۡيَىٰ

Lalle duk wanda ya zo wa Ubangijinsa yana mai babban laifi[1] to lalle yana da (sakamakon) Jahannama, ba zai mutu a cikinta ba, ba kuma zai rayu ba (rayuwa mai daxi)


1- Watau kafirce wa Allah da haxa wani da shi a wajen bauta.


Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 75

وَمَن يَأۡتِهِۦ مُؤۡمِنٗا قَدۡ عَمِلَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمُ ٱلدَّرَجَٰتُ ٱلۡعُلَىٰ

Wanda kuwa ya zo masa yana mumini ya zamana ya yi aiki na gari, to waxannan suna da (sakamakon samun) darajoji maxaukaka



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 76

جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ وَذَٰلِكَ جَزَآءُ مَن تَزَكَّىٰ

(Watau) gidajen Aljanna na dawwama waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, masu dawwama ne a cikinsu. Wannan kuwa shi ne sakamakon wanda ya tsarkaka (daga savo)



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 77

وَلَقَدۡ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِي فَٱضۡرِبۡ لَهُمۡ طَرِيقٗا فِي ٱلۡبَحۡرِ يَبَسٗا لَّا تَخَٰفُ دَرَكٗا وَلَا تَخۡشَىٰ

Haqiqa kuma Mun yi wa Musa wahayi cewa: “Ka tafi da bayina cikin dare sannan ka keta musu hanya qeqasasshiya a cikin kogi, ba za ka ji tsoron riskar (Fir’auna da jama’arsa) ba, kuma ba za ka ji tsoron (nutsewa) ba.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 78

فَأَتۡبَعَهُمۡ فِرۡعَوۡنُ بِجُنُودِهِۦ فَغَشِيَهُم مِّنَ ٱلۡيَمِّ مَا غَشِيَهُمۡ

Sai Fir’auna ya bi su shi da rundunarsa sai abin da ya haxe su na ruwan kogi ya haxiye su (suka hallaka kakaf)!



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 79

وَأَضَلَّ فِرۡعَوۡنُ قَوۡمَهُۥ وَمَا هَدَىٰ

Fir’auna kuma ya vatar da mutanensa bai kuma shiryar (da su) ba



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 80

يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ قَدۡ أَنجَيۡنَٰكُم مِّنۡ عَدُوِّكُمۡ وَوَٰعَدۡنَٰكُمۡ جَانِبَ ٱلطُّورِ ٱلۡأَيۡمَنَ وَنَزَّلۡنَا عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَنَّ وَٱلسَّلۡوَىٰ

Ya ku Banu-Isra’ila, haqiqa Mun tserar da ku daga maqiyinku, (watau Fir’auna) Muka kuma yi muku alqawarin (ganawa) a varin dama na dutsen Xuri[1], Muka kuma saukar muku da darva da kuma (gasassun tsuntsayen) salwa


1- Watau Allah () ya yi musu alqawarin ganawa da Annabi Musa (), domin yin magana da shi da ba shi littafin Attaura mai qunshe da shiriya a gare su.


Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 81

كُلُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا رَزَقۡنَٰكُمۡ وَلَا تَطۡغَوۡاْ فِيهِ فَيَحِلَّ عَلَيۡكُمۡ غَضَبِيۖ وَمَن يَحۡلِلۡ عَلَيۡهِ غَضَبِي فَقَدۡ هَوَىٰ

Ku ci daga daxaxan abin da Muka arzuta ku da shi (na halal), kada kuwa ku qetare shi (zuwa haramun), sai fushina ya faxa muku; wanda kuwa fushina ya faxa masa, to haqiqa ya hallaka



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 82

وَإِنِّي لَغَفَّارٞ لِّمَن تَابَ وَءَامَنَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا ثُمَّ ٱهۡتَدَىٰ

Lalle Ni kuma Mai yawan gafara ne ga wanda ya tuba kuma ya yi aiki na gari sannan ya (tabbata bisa) shiriya



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 83

۞وَمَآ أَعۡجَلَكَ عَن قَوۡمِكَ يَٰمُوسَىٰ

Kuma me ya sa ka gaggawar barin mutanenka, ya Musa?



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 84

قَالَ هُمۡ أُوْلَآءِ عَلَىٰٓ أَثَرِي وَعَجِلۡتُ إِلَيۡكَ رَبِّ لِتَرۡضَىٰ

(Musa) ya ce: “Su waxannan (mutane nawa) ai za su biyo bayana ne (ba da jimawa ba), na kuwa yi gaggawa ne zuwa gare Ka ya Ubangijina don neman yardarka.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 85

قَالَ فَإِنَّا قَدۡ فَتَنَّا قَوۡمَكَ مِنۢ بَعۡدِكَ وَأَضَلَّهُمُ ٱلسَّامِرِيُّ

(Allah) ya ce: “To lalle Mun jarrabi mutanenka a bayanka, Samiri kuma ya vatar da su[1].”


1- Samiri, wani munafuki ne a cikin Banu Isra’ila wanda ya ja su zuwa ga bautar xan maraqi.


Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 86

فَرَجَعَ مُوسَىٰٓ إِلَىٰ قَوۡمِهِۦ غَضۡبَٰنَ أَسِفٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ أَلَمۡ يَعِدۡكُمۡ رَبُّكُمۡ وَعۡدًا حَسَنًاۚ أَفَطَالَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡعَهۡدُ أَمۡ أَرَدتُّمۡ أَن يَحِلَّ عَلَيۡكُمۡ غَضَبٞ مِّن رَّبِّكُمۡ فَأَخۡلَفۡتُم مَّوۡعِدِي

Sai Musa ya komo zuwa ga mutanensa cike da fushi da baqin ciki. Ya ce: “Ya ku mutanena, yanzu Ubangijinku bai yi muku kyakkyawan alqawari ba[1]? Ko kuwa lokacin alqawarin ne ya yi muku tsawo? Ko kuwa kuna so ne fushin Ubangijinku ya saukar muku, shi ne sai kuka sava alqawarin (da muka yi na ku tabbata bisa imani)?”


1- Alqawari na cewa zai saukar musu da littafin Attaura, ya kuma shigar da su Aljjanna idan sun mutu.


Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 87

قَالُواْ مَآ أَخۡلَفۡنَا مَوۡعِدَكَ بِمَلۡكِنَا وَلَٰكِنَّا حُمِّلۡنَآ أَوۡزَارٗا مِّن زِينَةِ ٱلۡقَوۡمِ فَقَذَفۡنَٰهَا فَكَذَٰلِكَ أَلۡقَى ٱلسَّامِرِيُّ

Suka ce: “Ba mu sava alqawarinka da zavin kanmu ba, sai dai mu an xora mana kayayyakin nauyi ne na ababan adon mutane (Qibxawa), sai muka jefa su (a cikin wuta), sannan Samiri ya jefa (nasa) kamar yadda (muka yi).”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 88

فَأَخۡرَجَ لَهُمۡ عِجۡلٗا جَسَدٗا لَّهُۥ خُوَارٞ فَقَالُواْ هَٰذَآ إِلَٰهُكُمۡ وَإِلَٰهُ مُوسَىٰ فَنَسِيَ

To sai ya fitar musu da xan maraqi jika-jika mai kuka, sai suka ce[1]: “Wannan ubangijinku ne kuma ubangijin Musa, amma sai ya manta (da yana nan).”


1- Watau wasu fitinannu daga cikin Banu Isra’ila suka faxi wannan magana.


Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 89

أَفَلَا يَرَوۡنَ أَلَّا يَرۡجِعُ إِلَيۡهِمۡ قَوۡلٗا وَلَا يَمۡلِكُ لَهُمۡ ضَرّٗا وَلَا نَفۡعٗا

Yanzu ba sa gani cewa (maraqin) ba ya mayar musu da magana, kuma ba ya mallakar wata cuta ko amfani gare su?



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 90

وَلَقَدۡ قَالَ لَهُمۡ هَٰرُونُ مِن قَبۡلُ يَٰقَوۡمِ إِنَّمَا فُتِنتُم بِهِۦۖ وَإِنَّ رَبَّكُمُ ٱلرَّحۡمَٰنُ فَٱتَّبِعُونِي وَأَطِيعُوٓاْ أَمۡرِي

Alhali kuwa haqiqa Haruna ya faxa musu tun da wuri cewa: “Ya ku mutanena, an jarrabe ku da shi ne kawai, kuma lalle Ubangijinku (na gaskiya) Shi ne Arrahamanu, sai ku bi ni kuma ku bi umarnina.”