Sourate: Suratul Hijr

Verset : 61

فَلَمَّا جَآءَ ءَالَ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلُونَ

To lokacin da manzannin suka zo wa iyalin Luxu



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 62

قَالَ إِنَّكُمۡ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ

Ya ce: “Lalle ku wasu mutane ne da ba a san su ba.”



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 63

قَالُواْ بَلۡ جِئۡنَٰكَ بِمَا كَانُواْ فِيهِ يَمۡتَرُونَ

Suka ce: “A’a, mu mun zo maka ne da abin da (mutanenka) suke kokwanto game da shi



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 64

وَأَتَيۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ وَإِنَّا لَصَٰدِقُونَ

“Mun kuma zo maka da dahir, lalle kuma tabbas mu masu gaskiya ne



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 65

فَأَسۡرِ بِأَهۡلِكَ بِقِطۡعٖ مِّنَ ٱلَّيۡلِ وَٱتَّبِعۡ أَدۡبَٰرَهُمۡ وَلَا يَلۡتَفِتۡ مِنكُمۡ أَحَدٞ وَٱمۡضُواْ حَيۡثُ تُؤۡمَرُونَ

“Sai ka tafi da iyalinka cikin wani yankin dare ka kuma riqa bin su a baya, kada kuwa xaya daga cikinku ya waiwaya, kuma ku tafi inda aka umarce ku.”



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 66

وَقَضَيۡنَآ إِلَيۡهِ ذَٰلِكَ ٱلۡأَمۡرَ أَنَّ دَابِرَ هَـٰٓؤُلَآءِ مَقۡطُوعٞ مُّصۡبِحِينَ

Muka kuwa sanar da shi abin da Muka qaddara na wannan al’amari cewa, qarshen waxannan zai yanke ne da asuba



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 67

وَجَآءَ أَهۡلُ ٱلۡمَدِينَةِ يَسۡتَبۡشِرُونَ

Mutanen garin kuma suka zo suna murna (da ganin baqin)



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 68

قَالَ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ ضَيۡفِي فَلَا تَفۡضَحُونِ

Ya ce: “Lalle waxannan baqina ne, kada fa ku kunyata ni



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 69

وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَلَا تُخۡزُونِ

“Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kada ku tozarta ni[1].”


1- Annabi Luxu ya yi wannan maganar ne kafin ya san cewa waxannan baqi nasa mala’iku ne.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 70

قَالُوٓاْ أَوَلَمۡ نَنۡهَكَ عَنِ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Suka ce: “Ashe ba mu hana ka (ka saukar da) mutane (baqi ba)?”



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 71

قَالَ هَـٰٓؤُلَآءِ بَنَاتِيٓ إِن كُنتُمۡ فَٰعِلِينَ

Ya ce: “Ga ‘ya’yana nan (ku aura)[1] idan kun kasance masu aikata (haka)


1- Yana nufin matan al’ummarsa.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 72

لَعَمۡرُكَ إِنَّهُمۡ لَفِي سَكۡرَتِهِمۡ يَعۡمَهُونَ

“Na rantse da rayuwarka lalle su tabbas suna cikin mayensu suna ta ximuwa.”



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 73

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّيۡحَةُ مُشۡرِقِينَ

Sai tsawa ta auka musu lokacin hudowar rana



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 74

فَجَعَلۡنَا عَٰلِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِمۡ حِجَارَةٗ مِّن سِجِّيلٍ

Sai Muka mayar da samanta ya koma qasa, Muka kuma yi musu ruwan duwatsu soyayyu



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 75

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّلۡمُتَوَسِّمِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga masu hangen nesa



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 76

وَإِنَّهَا لَبِسَبِيلٖ مُّقِيمٍ

Lalle kuma ita (alqaryar) tabbas tana kan wani gwadabe ne miqaqqe



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 77

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai izina ga muminai



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 78

وَإِن كَانَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأَيۡكَةِ لَظَٰلِمِينَ

Lalle kuma mutanen (alqaryar) Mai duhuwa tabbas sun zamanto azzalumai



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 79

فَٱنتَقَمۡنَا مِنۡهُمۡ وَإِنَّهُمَا لَبِإِمَامٖ مُّبِينٖ

Sai Muka azabtar da su, lalle kuma su biyun suna kan wani gwadabe ne fitacce



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 80

وَلَقَدۡ كَذَّبَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡحِجۡرِ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Haqiqa kuma mutanen Hijiru (Samudawa) sun qaryata manzanni



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 81

وَءَاتَيۡنَٰهُمۡ ءَايَٰتِنَا فَكَانُواْ عَنۡهَا مُعۡرِضِينَ

Muka kuma kawo musu ayoyinmu, sai suka zamanto masu bijirewa daga gare su



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 82

وَكَانُواْ يَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتًا ءَامِنِينَ

Sun zamanto suna fafe duwatsu suna yin gidaje su zama cikin aminci



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 83

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّيۡحَةُ مُصۡبِحِينَ

Sai tsawa ta auka musu da asuba



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 84

فَمَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ

Sai abin da suka zamanto suna aikatawa bai amfane su ba



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 85

وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَآ إِلَّا بِٱلۡحَقِّۗ وَإِنَّ ٱلسَّاعَةَ لَأٓتِيَةٞۖ فَٱصۡفَحِ ٱلصَّفۡحَ ٱلۡجَمِيلَ

Ba Mu kuma halicci sammai da qasa ba sai da gaskiya. Kuma lalle alqiyama tabbas mai zuwa ce, sai ka yi afuwa kyakkyawar afuwa[1]


1- Watau afuwar da babu cutarwa a cikinta sai dai kyautatawa ga wanda ya munana.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 86

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ ٱلۡخَلَّـٰقُ ٱلۡعَلِيمُ

Lalle Ubangijinka Shi ne Mai halitta, Masani



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 87

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَٰكَ سَبۡعٗا مِّنَ ٱلۡمَثَانِي وَٱلۡقُرۡءَانَ ٱلۡعَظِيمَ

Haqiqa kuma Mun ba ka (ayoyi) bakwai waxanda ake ta nanatawa (wato Suratul Fatiha) da kuma Alqur’ani mai girma



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 88

لَا تَمُدَّنَّ عَيۡنَيۡكَ إِلَىٰ مَا مَتَّعۡنَا بِهِۦٓ أَزۡوَٰجٗا مِّنۡهُمۡ وَلَا تَحۡزَنۡ عَلَيۡهِمۡ وَٱخۡفِضۡ جَنَاحَكَ لِلۡمُؤۡمِنِينَ

Kada ka zura idanuwanka ga abubuwan jin daxi da Muka ba wa wasu dangogi daga cikinsu, kada kuma ka yi baqin ciki a kansu, kuma ka qasqantar da kanka ga muminai



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 89

وَقُلۡ إِنِّيٓ أَنَا ٱلنَّذِيرُ ٱلۡمُبِينُ

Ka kuma ce: “Lalle ni, ni ne mai gargaxi mabayyani»



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 90

كَمَآ أَنزَلۡنَا عَلَى ٱلۡمُقۡتَسِمِينَ

Kamar yadda Muka saukar wa masu rarrabawa (wato ma’abota littafi)