Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 31

فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ

To bai ba da gaskiya ba bai kuma yi salla ba



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 32

وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ

Sai dai ya qaryata ya kuma ba da baya



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 33

ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ

Sannan ya tafi zuwa ga iyalinsa yana taqama



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 34

أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰ

(Azaba) ta doso ka, ta fa doso ka!



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 35

ثُمَّ أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰٓ

Sannan ta doso ka, ta fa doso ka!



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 36

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَن يُتۡرَكَ سُدًى

Yanzu mutum yana tsammanin za a bar shi haka sasaka[1]?


1- Watau za a qyale shi ya yi abin da ya ga dama ba tare da umarni ko hani ba?


Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 37

أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ

Shin bai kasance wani xigo na maniyyi da ake zuba shi (a mahaifa) ba?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 38

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ

Sannan ya zama gudan jini sannan (Allah) Ya halicce (shi) sai Ya daidaita (shi)?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 39

فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Sannan Ya halicci dangi biyu daga gare shi, namiji da mace?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 40

أَلَيۡسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحۡـِۧيَ ٱلۡمَوۡتَىٰ

Yanzu wannan bai zama Mai iko a kan ya raya matattu ba?