Sourate: Suratul Qalam

Verset : 31

قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ

Suka ce: “Kaiconmu, lalle mu mun kasance masu shisshigi



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 32

عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبۡدِلَنَا خَيۡرٗا مِّنۡهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ

“Tsammanin Ubangijinmu zai musanya mana wadda ta fi ta, lalle mu masu kwaxayi ne a wurin Ubangijinmu[1].”


1- Watau zai ba su wata gonar da ta fi tasu, suna kuma fatan zai yi musu afuwa ya yafe musu kurakuransu.


Sourate: Suratul Qalam

Verset : 33

كَذَٰلِكَ ٱلۡعَذَابُۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Kamar haka ne azaba take tabbata; kuma tabbas azabar lahira ta fi girma. Da sun kasance sun san haka



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 34

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Lalle masu taqawa suna da gidajen Aljannar ni’ima a wurin Ubangijinsu



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 35

أَفَنَجۡعَلُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ كَٱلۡمُجۡرِمِينَ

Yanzu za Mu sanya Musulmi kamar kangararru?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 36

مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ

Me ya same ku ne, yaya kuke irin wannan hukuncin?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 37

أَمۡ لَكُمۡ كِتَٰبٞ فِيهِ تَدۡرُسُونَ

Ko kuna da wani littafi ne wanda a cikinsa kuke karantawa?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 38

إِنَّ لَكُمۡ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ

(Cewa) a cikinsa lalle kuna da abin da kuke zava?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 39

أَمۡ لَكُمۡ أَيۡمَٰنٌ عَلَيۡنَا بَٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ إِنَّ لَكُمۡ لَمَا تَحۡكُمُونَ

Ko kuwa kuna da wasu alqawura na rantsuwa ne (tabbatattu) a kanmu har zuwa ranar alqiyama cewa, lalle kuna da abin da kuke hukunta wa (kanku)?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 40

سَلۡهُمۡ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ

Ka tambaye su wane ne a cikinsu ya yi lamuni game da wannan?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 41

أَمۡ لَهُمۡ شُرَكَآءُ فَلۡيَأۡتُواْ بِشُرَكَآئِهِمۡ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ

Ko kuwa suna da wasu ababan tarayya ne? To su kawo ababan tarayyar tasu idan sun kasance masu gaskiya



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 42

يَوۡمَ يُكۡشَفُ عَن سَاقٖ وَيُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ

(Ka tuna) ranar da za a yaye qwauri[1] a kuma kirawo su zuwa yin sujjada sannan su rasa ikon yi


1- Watau ranar da Allah () zai kware qwaurinsa mai daraja wanda bai yi kama da wani abu na halittarsa ba.


Sourate: Suratul Qalam

Verset : 43

خَٰشِعَةً أَبۡصَٰرُهُمۡ تَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۖ وَقَدۡ كَانُواْ يُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمۡ سَٰلِمُونَ

Idanuwansu a qasqance, wulaqanci ya lulluve su. Haqiqa kuwa a duniya sun kasance ana kiran su zuwa yin sujjada alhali suna lafiyayyu



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 44

فَذَرۡنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِۖ سَنَسۡتَدۡرِجُهُم مِّنۡ حَيۡثُ لَا يَعۡلَمُونَ

Saboda haka ka bar Ni da wanda yake qaryata wannan Alqur’ani; ba da daxewa ba za Mu yi musu talala ta inda ba za su sani ba



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 45

وَأُمۡلِي لَهُمۡۚ إِنَّ كَيۡدِي مَتِينٌ

Kuma zan saurara musu. Lalle kaidina mai qarfi ne



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 46

أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ

Ko kuwa kana tambayar su wani lada ne, saboda haka biyan (wannan lada) ya yi musu nauyi?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 47

أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko kuwa sanin gaibu a wurinsu yake, saboda haka suke rubuto shi?



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 48

فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلۡحُوتِ إِذۡ نَادَىٰ وَهُوَ مَكۡظُومٞ

To ka yi haquri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar ma’abocin kifi (Yunus) a yayin da ya yi kira, alhali shi yana cike da baqin ciki



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 49

لَّوۡلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعۡمَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ مَذۡمُومٞ

Ba don wata rahama daga Ubangijinsa ta riske shi ba, da an jefar da shi a qungurmin daji alhali shi yana abin suka



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 50

فَٱجۡتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Sai Ubangijinsa Ya zave shi Ya sanya shi daga (bayi) nagari



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 51

وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَيُزۡلِقُونَكَ بِأَبۡصَٰرِهِمۡ لَمَّا سَمِعُواْ ٱلذِّكۡرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجۡنُونٞ

Lalle kuma waxanda suka kafirta sun yi kusa su kayar da kai da kallonsu yayin da suka ji Alqur’ani, suka kuma riqa cewa: “Lalle shi tabbas mahaukaci ne!”



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 52

وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ

Shi kuwa (Alqur’ani) ba wani abu ba ne face gargaxi ga talikai