Sourate: Suratul An’am

Verset : 31

قَدۡ خَسِرَ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِلِقَآءِ ٱللَّهِۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَتۡهُمُ ٱلسَّاعَةُ بَغۡتَةٗ قَالُواْ يَٰحَسۡرَتَنَا عَلَىٰ مَا فَرَّطۡنَا فِيهَا وَهُمۡ يَحۡمِلُونَ أَوۡزَارَهُمۡ عَلَىٰ ظُهُورِهِمۡۚ أَلَا سَآءَ مَا يَزِرُونَ

Haqiqa waxanda suka qaryata haxuwa da Allah sun yi hasara; har sai lokacin da alqiyama ta zo musu ba zato ba tsammani, sai su ce: “Kaiconmu kan irin sakacin da muka yi a cikinta (duniya),” alhalin kuwa suna xauke da kayan laifukansu a bayansu. Ku saurara, abin da suka xauka na laifi ya munana matuqa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 32

وَمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَآ إِلَّا لَعِبٞ وَلَهۡوٞۖ وَلَلدَّارُ ٱلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لِّلَّذِينَ يَتَّقُونَۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Kuma rayuwar duniya ba komai ba ce face wasa da sharholiya; kuma lalle gidan lahira shi ne mafi alheri ga waxanda suke kiyaye dokokin (Allah). Shin ba za ku hankalta ba?



Sourate: Suratul An’am

Verset : 33

قَدۡ نَعۡلَمُ إِنَّهُۥ لَيَحۡزُنُكَ ٱلَّذِي يَقُولُونَۖ فَإِنَّهُمۡ لَا يُكَذِّبُونَكَ وَلَٰكِنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ يَجۡحَدُونَ

Haqiqa Muna da cikakkiyar masaniyar cewa, lalle irin abin da suke faxa yakan baqanta maka rai; to a gaskiya su ba kai suke qaryatawa ba, sai dai azzalumai suna jayayya ne da ayoyin Allah



Sourate: Suratul An’am

Verset : 34

وَلَقَدۡ كُذِّبَتۡ رُسُلٞ مِّن قَبۡلِكَ فَصَبَرُواْ عَلَىٰ مَا كُذِّبُواْ وَأُوذُواْ حَتَّىٰٓ أَتَىٰهُمۡ نَصۡرُنَاۚ وَلَا مُبَدِّلَ لِكَلِمَٰتِ ٱللَّهِۚ وَلَقَدۡ جَآءَكَ مِن نَّبَإِيْ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma lalle haqiqa an qaryata waxansu manzanni a gabaninka, sai suka yi haquri a kan qaryata su da aka yi, kuma an cutar da su, har sai da taimakonmu ya zo musu. Kuma babu wanda ya isa ya musanya kalmomin Allah. Kuma lalle haqiqa wani sashi na labarin manzanni ya zo maka



Sourate: Suratul An’am

Verset : 35

وَإِن كَانَ كَبُرَ عَلَيۡكَ إِعۡرَاضُهُمۡ فَإِنِ ٱسۡتَطَعۡتَ أَن تَبۡتَغِيَ نَفَقٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ أَوۡ سُلَّمٗا فِي ٱلسَّمَآءِ فَتَأۡتِيَهُم بِـَٔايَةٖۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَجَمَعَهُمۡ عَلَى ٱلۡهُدَىٰۚ فَلَا تَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡجَٰهِلِينَ

Kuma idan bijirewarsu ta dame ka, to idan har kana iya haqa rami a cikin qasa, ko kuma (ka samu) wani tsani ka hau sama, don ka zo musu da wata aya, (to ka yi hakan). Kuma in da Allah Ya ga dama, tabbas da Ya tara su gaba xaya a kan shiriya. Don haka kada ka kasance cikin jahilai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 36

۞إِنَّمَا يَسۡتَجِيبُ ٱلَّذِينَ يَسۡمَعُونَۘ وَٱلۡمَوۡتَىٰ يَبۡعَثُهُمُ ٱللَّهُ ثُمَّ إِلَيۡهِ يُرۡجَعُونَ

Lalle masu ji su ne kawai suke amsa (kiranka). Matattu kuwa Allah zai tashe su (ranar alqiyama), sannan zuwa gare Shi za a mayar da su



Sourate: Suratul An’am

Verset : 37

وَقَالُواْ لَوۡلَا نُزِّلَ عَلَيۡهِ ءَايَةٞ مِّن رَّبِّهِۦۚ قُلۡ إِنَّ ٱللَّهَ قَادِرٌ عَلَىٰٓ أَن يُنَزِّلَ ءَايَةٗ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Kuma suka ce: “Ina ma da an saukar masa da wata aya daga Ubangijinsa ?” Ka ce: “Lalle Allah Mai iko ne a kan Ya saukar da kowace irin aya, sai dai yawancinsu ba sa sanin (haka).”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 38

وَمَا مِن دَآبَّةٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا طَـٰٓئِرٖ يَطِيرُ بِجَنَاحَيۡهِ إِلَّآ أُمَمٌ أَمۡثَالُكُمۚ مَّا فَرَّطۡنَا فِي ٱلۡكِتَٰبِ مِن شَيۡءٖۚ ثُمَّ إِلَىٰ رَبِّهِمۡ يُحۡشَرُونَ

Kuma babu wata dabba da take tafiya a bayan qasa, kuma babu wani tsuntsu da yake tashi da fukafukansa, face (su ma) al’ummomi ne irinku. Ba Mu yi sakacin barin wani abu ba a cikin littafi, sannan kuma zuwa ga Ubangijinsu ne za a tara su



Sourate: Suratul An’am

Verset : 39

وَٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا صُمّٞ وَبُكۡمٞ فِي ٱلظُّلُمَٰتِۗ مَن يَشَإِ ٱللَّهُ يُضۡلِلۡهُ وَمَن يَشَأۡ يَجۡعَلۡهُ عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Waxanda suka qaryata ayoyinmu su kurame ne, kuma bebaye ne, suna cikin duffai. Wanda Allah Ya ga dama sai Ya vatar da shi, wanda kuwa Ya ga dama sai Ya xora shi a kan tafarki madaidaici



Sourate: Suratul An’am

Verset : 40

قُلۡ أَرَءَيۡتَكُمۡ إِنۡ أَتَىٰكُمۡ عَذَابُ ٱللَّهِ أَوۡ أَتَتۡكُمُ ٱلسَّاعَةُ أَغَيۡرَ ٱللَّهِ تَدۡعُونَ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Ka ce; “Ku ba ni labari, idan da a ce azabar Allah za ta zo muku ko alqiyama ta zo muku, shin wanin Allah za ku kira, in har kun kasance masu gaskiya?”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 41

بَلۡ إِيَّاهُ تَدۡعُونَ فَيَكۡشِفُ مَا تَدۡعُونَ إِلَيۡهِ إِن شَآءَ وَتَنسَوۡنَ مَا تُشۡرِكُونَ

Ba haka ba ne, (Allah) Shi kaxai za ku kira, sai Ya yaye abin da kuke roqonsa a kai idan Ya ga dama, kuma za ku manta abin da kuke haxa Allah da shi wajen bauta



Sourate: Suratul An’am

Verset : 42

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَآ إِلَىٰٓ أُمَمٖ مِّن قَبۡلِكَ فَأَخَذۡنَٰهُم بِٱلۡبَأۡسَآءِ وَٱلضَّرَّآءِ لَعَلَّهُمۡ يَتَضَرَّعُونَ

Kuma lalle Mun aika da (manzanni) zuwa ga al’ummomin da suka gabace ka, sai Muka xora musu tsananin talauci da cutuka ko sa qasqantar da kai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 43

فَلَوۡلَآ إِذۡ جَآءَهُم بَأۡسُنَا تَضَرَّعُواْ وَلَٰكِن قَسَتۡ قُلُوبُهُمۡ وَزَيَّنَ لَهُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

To me ya hana lokacin da musibarmu ta zo musu, su qasqantar da kai? Sai dai kuma zukatansu ne suka qeqashe, Shaixan kuma ya qawata musu abin da suka kasance suna aikatawa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 44

فَلَمَّا نَسُواْ مَا ذُكِّرُواْ بِهِۦ فَتَحۡنَا عَلَيۡهِمۡ أَبۡوَٰبَ كُلِّ شَيۡءٍ حَتَّىٰٓ إِذَا فَرِحُواْ بِمَآ أُوتُوٓاْ أَخَذۡنَٰهُم بَغۡتَةٗ فَإِذَا هُم مُّبۡلِسُونَ

To yayin da suka yi watsi da abin da aka yi musu wa’azi da shi, sai Muka buxe musu qofofin kowane irin abu, har zuwa lokacin da suka yi fariya da abin da aka ba su, sai Muka damqe su ba zato ba tsammani, sai ga su suna masu yanke qauna (daga kowane alheri)



Sourate: Suratul An’am

Verset : 45

فَقُطِعَ دَابِرُ ٱلۡقَوۡمِ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْۚ وَٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Da haka ne aka tumvuke tushen waxanda suka yi zalunci. Kuma yabo da kirari sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 46

قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَخَذَ ٱللَّهُ سَمۡعَكُمۡ وَأَبۡصَٰرَكُمۡ وَخَتَمَ عَلَىٰ قُلُوبِكُم مَّنۡ إِلَٰهٌ غَيۡرُ ٱللَّهِ يَأۡتِيكُم بِهِۗ ٱنظُرۡ كَيۡفَ نُصَرِّفُ ٱلۡأٓيَٰتِ ثُمَّ هُمۡ يَصۡدِفُونَ

Ka ce: “Ku ba ni labari, yanzu idan Allah zai xauke jinku da ganinku, kuma Ya xora murfi a zukatanku, wane abin bauta ne wanda ba Allah ba, da zai dawo muku da shi?” Duba ka ga yadda Muke sarrafa ayoyi, amma duk da haka suna bijirewa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 47

قُلۡ أَرَءَيۡتَكُمۡ إِنۡ أَتَىٰكُمۡ عَذَابُ ٱللَّهِ بَغۡتَةً أَوۡ جَهۡرَةً هَلۡ يُهۡلَكُ إِلَّا ٱلۡقَوۡمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Ka ce: “Ku ba ni labari, idan da azabar Allah za ta zo muku ba zato ba tsammani ko kuma cikin sani, to shin za a hallakar da (wasu) ba azzaluman mutane ba?”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 48

وَمَا نُرۡسِلُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ إِلَّا مُبَشِّرِينَ وَمُنذِرِينَۖ فَمَنۡ ءَامَنَ وَأَصۡلَحَ فَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Kuma ba ma aiko da manzanni sai suna masu bushara masu gargaxi; sannan duk wanda ya yi imani kuma ya kyautata aiki, to babu tsoro a tattare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



Sourate: Suratul An’am

Verset : 49

وَٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يَمَسُّهُمُ ٱلۡعَذَابُ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

Waxanda kuwa suka qaryata ayoyinmu, azaba za ta shafe su saboda abin da suka kasance suna yi na fasiqanci



Sourate: Suratul An’am

Verset : 50

قُل لَّآ أَقُولُ لَكُمۡ عِندِي خَزَآئِنُ ٱللَّهِ وَلَآ أَعۡلَمُ ٱلۡغَيۡبَ وَلَآ أَقُولُ لَكُمۡ إِنِّي مَلَكٌۖ إِنۡ أَتَّبِعُ إِلَّا مَا يُوحَىٰٓ إِلَيَّۚ قُلۡ هَلۡ يَسۡتَوِي ٱلۡأَعۡمَىٰ وَٱلۡبَصِيرُۚ أَفَلَا تَتَفَكَّرُونَ

Ka ce: “Ni ba zan ce da ku a wajena taskokin Allah suke ba, kuma ni ban san gaibu ba, kuma ni ba zan ce da ku ni mala’ika ne ba; ni ba abin da nake bi sai abin da aka yi mini wahayinsa.” Ka ce: “Yanzu makaho da mai gani za su yi daidai? To me ya sa ba za ku yi tunani ba?”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 51

وَأَنذِرۡ بِهِ ٱلَّذِينَ يَخَافُونَ أَن يُحۡشَرُوٓاْ إِلَىٰ رَبِّهِمۡ لَيۡسَ لَهُم مِّن دُونِهِۦ وَلِيّٞ وَلَا شَفِيعٞ لَّعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ

Kuma ka yi gargaxi da shi (Alqur’ani) ga waxanda suke jin tsoron a tattara su a gaban Ubangijinsu, ba su da wani majivincin lamari in ba Shi ba, kuma ba su da wani mai ceto, don su kiyaye dokokin Allah



Sourate: Suratul An’am

Verset : 52

وَلَا تَطۡرُدِ ٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ رَبَّهُم بِٱلۡغَدَوٰةِ وَٱلۡعَشِيِّ يُرِيدُونَ وَجۡهَهُۥۖ مَا عَلَيۡكَ مِنۡ حِسَابِهِم مِّن شَيۡءٖ وَمَا مِنۡ حِسَابِكَ عَلَيۡهِم مِّن شَيۡءٖ فَتَطۡرُدَهُمۡ فَتَكُونَ مِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma kada ka kori waxannan da suke bauta wa Ubangijinsu safe da yamma, suna nufin Fuskarsa (watau suna yi don Shi kaxai); ba wani abu na haqqinsu a kanka, kuma babu wani abu na haqqinka a kansu, balle ka kore su, sai ka kasance cikin azzalumai.[1]


1- Daga nan zuwa aya ta 54 suna magana ne game da mushirikan Larabawa da suka nuna wa Manzon Allah () cewa za su musulunta amma da sharaxin zai kori Musulmi talakawa daga majalisarsa don kada su riqa yi musu rashin kunya. Sai Allah () ya hana shi aikata hakan.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 53

وَكَذَٰلِكَ فَتَنَّا بَعۡضَهُم بِبَعۡضٖ لِّيَقُولُوٓاْ أَهَـٰٓؤُلَآءِ مَنَّ ٱللَّهُ عَلَيۡهِم مِّنۢ بَيۡنِنَآۗ أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَعۡلَمَ بِٱلشَّـٰكِرِينَ

Kuma kamar haka ne Muka jarrabi sashinsu da sashi, domin su ce: “Yanzu waxannan su ne Allah Ya yi wa baiwa daga cikinmu?” Ashe Allah ba Shi ne Mafi sanin masu godiya (gare Shi) ba?



Sourate: Suratul An’am

Verset : 54

وَإِذَا جَآءَكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِـَٔايَٰتِنَا فَقُلۡ سَلَٰمٌ عَلَيۡكُمۡۖ كَتَبَ رَبُّكُمۡ عَلَىٰ نَفۡسِهِ ٱلرَّحۡمَةَ أَنَّهُۥ مَنۡ عَمِلَ مِنكُمۡ سُوٓءَۢا بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ تَابَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَصۡلَحَ فَأَنَّهُۥ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Kuma idan waxanda suke yin imani da ayoyinmu sun zo wurinka, to ka ce: “Sallama a gare ku;” Ubangijinku Ya wajabta wa kansa yin rahama cewa, lalle cikinku duk wanda ya aikata wani mummunan aiki bisa ga jahilci, sannan daga baya ya tuba kuma ya kyautata aiki, to Shi Mai gafara ne, Mai jin qai.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 55

وَكَذَٰلِكَ نُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ وَلِتَسۡتَبِينَ سَبِيلُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Kuma kamar haka ne Muke rarrabe ayoyi domin tafarkin masu laifuka ya bayyana



Sourate: Suratul An’am

Verset : 56

قُلۡ إِنِّي نُهِيتُ أَنۡ أَعۡبُدَ ٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِۚ قُل لَّآ أَتَّبِعُ أَهۡوَآءَكُمۡ قَدۡ ضَلَلۡتُ إِذٗا وَمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُهۡتَدِينَ

Ka ce: “Lalle ni an hana ni in bauta wa abubuwan da kuke bauta wa ba Allah ba.” Ka ce: “Ba zan bi soye-soyen zukatanku ba, (idan har zan bi son zuciyarku), to haqiqa na vata, kuma da ban zama cikin shiryayyu ba kenan”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 57

قُلۡ إِنِّي عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّي وَكَذَّبۡتُم بِهِۦۚ مَا عِندِي مَا تَسۡتَعۡجِلُونَ بِهِۦٓۚ إِنِ ٱلۡحُكۡمُ إِلَّا لِلَّهِۖ يَقُصُّ ٱلۡحَقَّۖ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلۡفَٰصِلِينَ

Ka ce: “Lalle ni ina kan hujja mai qarfi daga Ubangijina, ku kuma kun qaryata ta. Abin da kuke so in gaggauto muku da shi, ba a hannuna yake ba. Hukunci yana hannun Allah ne Shi kaxai; Shi ne Yake bayar da labarin gaskiya, kuma Shi ne Fiyayyen masu rarrabewa (tsakanin qarya da gaskiya)”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 58

قُل لَّوۡ أَنَّ عِندِي مَا تَسۡتَعۡجِلُونَ بِهِۦ لَقُضِيَ ٱلۡأَمۡرُ بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡۗ وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِٱلظَّـٰلِمِينَ

Ka ce: “Da a ce abin da kuke nema a gaggauto muku da shi a wurina yake, to tabbas da ta faru ta qare tsakanina da ku. Kuma Allah Shi ne Mafi sanin su wane ne azzalumai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 59

۞وَعِندَهُۥ مَفَاتِحُ ٱلۡغَيۡبِ لَا يَعۡلَمُهَآ إِلَّا هُوَۚ وَيَعۡلَمُ مَا فِي ٱلۡبَرِّ وَٱلۡبَحۡرِۚ وَمَا تَسۡقُطُ مِن وَرَقَةٍ إِلَّا يَعۡلَمُهَا وَلَا حَبَّةٖ فِي ظُلُمَٰتِ ٱلۡأَرۡضِ وَلَا رَطۡبٖ وَلَا يَابِسٍ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

“Kuma mabuxan gaibu a wurinsa suke Shi kaxai[1], babu wanda ya san su sai Shi. Kuma Ya san qididdigar abin da yake kan tudu da na ruwa. Kuma babu wani ganyen itace da zai faxo, face sai Ya san da shi, kuma ba wata qwaya da take cikin duhun qasa, kuma ba wani xanyen abu ko busasshe, face (bayaninsa) yana cikin Littafi mabayyani


1- Mabuxan gaibu biyar ne babu wanda ya san su sai Allah. Su ne suka zo a qarshen Suratu Luqman aya ta 34.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 60

وَهُوَ ٱلَّذِي يَتَوَفَّىٰكُم بِٱلَّيۡلِ وَيَعۡلَمُ مَا جَرَحۡتُم بِٱلنَّهَارِ ثُمَّ يَبۡعَثُكُمۡ فِيهِ لِيُقۡضَىٰٓ أَجَلٞ مُّسَمّٗىۖ ثُمَّ إِلَيۡهِ مَرۡجِعُكُمۡ ثُمَّ يُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

“Kuma Shi ne Yake karvar rayukanku da daddare[1], kuma Ya san abin da kuka aikata da rana, sannan Ya tayar da ku a cikinta (ranar), har zuwa lokacin da zai zartar da wani ajali sananne, sannan zuwa gare Shi ne makomarku take, sannan zai ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa


1- Watau lokacin barcinku; ya riqe ran da ya hukunta masa mutuwa, ya sako wanda lokacin mutuwarsa bai zo ba. duba Suratuz Zumar aya ta 42.