Sourate: Suratun Najm

Verset : 31

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ لِيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَسَـٰٓـُٔواْ بِمَا عَمِلُواْ وَيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَحۡسَنُواْ بِٱلۡحُسۡنَى

Kuma abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne, don Ya saka wa waxanda suka munana da irin abin da suka aikata, Ya kuma saka wa waxanda suka kyautata da mafi kyan sakamako



Sourate: Suratun Najm

Verset : 32

ٱلَّذِينَ يَجۡتَنِبُونَ كَبَـٰٓئِرَ ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلۡمَغۡفِرَةِۚ هُوَ أَعۡلَمُ بِكُمۡ إِذۡ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ وَإِذۡ أَنتُمۡ أَجِنَّةٞ فِي بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمۡۖ فَلَا تُزَكُّوٓاْ أَنفُسَكُمۡۖ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ

(Su ne) waxanda suke nisantar manya-manyan zunubai da munanan ayyukan savo, sai dai ‘yan qananan zunubai. Lalle Ubangijinka Mayalwacin gafara ne. Shi ne Ya fi sanin ku, tun sanda Ya halicce ku daga qasa, sai ga ku kun zama ‘yan tayi a cikin cikin iyayenku mata; to kada ku tsarkake kanku; Shi ne Ya fi sanin wanda ya fi taqawa



Sourate: Suratun Najm

Verset : 33

أَفَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي تَوَلَّىٰ

Ka ba ni labarin wanda ya ba da baya



Sourate: Suratun Najm

Verset : 34

وَأَعۡطَىٰ قَلِيلٗا وَأَكۡدَىٰٓ

Ya kuma bayar da dukiya kaxan kuma ya yi rowa



Sourate: Suratun Najm

Verset : 35

أَعِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلۡغَيۡبِ فَهُوَ يَرَىٰٓ

Shin yana da ilimin gaibu ne don haka yana ganin (komai)?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 36

أَمۡ لَمۡ يُنَبَّأۡ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ

Ko ba a ba shi labarin abin da yake cikin takardun Musa ba ne?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 37

وَإِبۡرَٰهِيمَ ٱلَّذِي وَفَّىٰٓ

Da kuma Ibrahimu wanda ya cika alqawari?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 38

أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٞ وِزۡرَ أُخۡرَىٰ

Cewa: “Wani rai ba ya xaukar nauyin laifin wani



Sourate: Suratun Najm

Verset : 39

وَأَن لَّيۡسَ لِلۡإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ

“Kuma mutum bai mallaki wani sakamako ba sai na abin da ya aikata



Sourate: Suratun Najm

Verset : 40

وَأَنَّ سَعۡيَهُۥ سَوۡفَ يُرَىٰ

“Kuma lalle aikin nasa ba da daxewa ba za a gan shi



Sourate: Suratun Najm

Verset : 41

ثُمَّ يُجۡزَىٰهُ ٱلۡجَزَآءَ ٱلۡأَوۡفَىٰ

“Sannan a saka masa da cikakken sakamako



Sourate: Suratun Najm

Verset : 42

وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلۡمُنتَهَىٰ

“Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makoma



Sourate: Suratun Najm

Verset : 43

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضۡحَكَ وَأَبۡكَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya sa a yi dariya, kuma Ya sa a yi kuka



Sourate: Suratun Najm

Verset : 44

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَمَاتَ وَأَحۡيَا

“Kuma lalle Shi ne Ya kashe kuma Ya raya



Sourate: Suratun Najm

Verset : 45

وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya halicci dangi biyu namiji da mace



Sourate: Suratun Najm

Verset : 46

مِن نُّطۡفَةٍ إِذَا تُمۡنَىٰ

“Daga maniyyi yayin da ake zuba shi



Sourate: Suratun Najm

Verset : 47

وَأَنَّ عَلَيۡهِ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰ

“Kuma lalle Ya xora wa kansa sake tashin matattu



Sourate: Suratun Najm

Verset : 48

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغۡنَىٰ وَأَقۡنَىٰ

“Lalle kuma Shi ne Ya wadata, Ya kuma yalwata



Sourate: Suratun Najm

Verset : 49

وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعۡرَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ubangijin tauraron nan Shi’ira



Sourate: Suratun Najm

Verset : 50

وَأَنَّهُۥٓ أَهۡلَكَ عَادًا ٱلۡأُولَىٰ

“Lalle kuma Ya hallakar da Adawa na farko



Sourate: Suratun Najm

Verset : 51

وَثَمُودَاْ فَمَآ أَبۡقَىٰ

“Da kuma Samudawa, don haka bai bar saura ba



Sourate: Suratun Najm

Verset : 52

وَقَوۡمَ نُوحٖ مِّن قَبۡلُۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ هُمۡ أَظۡلَمَ وَأَطۡغَىٰ

“Da mutanen Nuhu tun kafin su; lalle su sun kasance su ne mafiya zalunci kuma mafiya xagawa



Sourate: Suratun Najm

Verset : 53

وَٱلۡمُؤۡتَفِكَةَ أَهۡوَىٰ

“Da waxanda aka kife (mutanen Luxu, Allah) ya qasqanta su



Sourate: Suratun Najm

Verset : 54

فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ

“Sannan abin da ya lulluve su (na azaba) ya lulluve su.”



Sourate: Suratun Najm

Verset : 55

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ

To (kai xan’adam) da waxanne ni’imomin Ubangijinka kake jayayya?



Sourate: Suratun Najm

Verset : 56

هَٰذَا نَذِيرٞ مِّنَ ٱلنُّذُرِ ٱلۡأُولَىٰٓ

Wannan mai gargaxi ne daga irin masu gargaxin farko



Sourate: Suratun Najm

Verset : 57

أَزِفَتِ ٱلۡأٓزِفَةُ

Mai kusantowa ta kusanto (watau alqiyama)



Sourate: Suratun Najm

Verset : 58

لَيۡسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ كَاشِفَةٌ

Ba wani mai bayyana lokacinta in ban da Allah



Sourate: Suratun Najm

Verset : 59

أَفَمِنۡ هَٰذَا ٱلۡحَدِيثِ تَعۡجَبُونَ

Yanzu game da wannan zancen ne[1] kuke mamaki?


1- Watau Alqur’ani mai girma.


Sourate: Suratun Najm

Verset : 60

وَتَضۡحَكُونَ وَلَا تَبۡكُونَ

Kuke kuma dariya ba kwa yin kuka?