Sourate: Suratux Xur

Verset : 31

قُلۡ تَرَبَّصُواْ فَإِنِّي مَعَكُم مِّنَ ٱلۡمُتَرَبِّصِينَ

Ka ce, “To ku saurara, ni ma lalle ina cikin masu sauraron.”



Sourate: Suratux Xur

Verset : 32

أَمۡ تَأۡمُرُهُمۡ أَحۡلَٰمُهُم بِهَٰذَآۚ أَمۡ هُمۡ قَوۡمٞ طَاغُونَ

Ko kuwa hankullansu ne suke umartar su da wannan? A’a, su dai mutane ne masu tsaurin kai



Sourate: Suratux Xur

Verset : 33

أَمۡ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُۥۚ بَل لَّا يُؤۡمِنُونَ

Ko kuwa suna cewa: “Ya qago shi?” A’a, su dai ba sa yin imani ne kawai



Sourate: Suratux Xur

Verset : 34

فَلۡيَأۡتُواْ بِحَدِيثٖ مِّثۡلِهِۦٓ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ

To su zo da wani zance irinsa idan sun kasance masu gaskiya



Sourate: Suratux Xur

Verset : 35

أَمۡ خُلِقُواْ مِنۡ غَيۡرِ شَيۡءٍ أَمۡ هُمُ ٱلۡخَٰلِقُونَ

Ko kuwa an halicce su ne ba da wani mai halitta ba, ko kuwa su ne masu halittar (kansu)?



Sourate: Suratux Xur

Verset : 36

أَمۡ خَلَقُواْ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ

Ko kuwa su suka halicci sammai da qasa? A’a, ba sa dai sakankancewa ne



Sourate: Suratux Xur

Verset : 37

أَمۡ عِندَهُمۡ خَزَآئِنُ رَبِّكَ أَمۡ هُمُ ٱلۡمُصَۜيۡطِرُونَ

Ko kuwa taskokin Ubangijinka suna wurinsu ne, ko kuwa su ne masu iko?



Sourate: Suratux Xur

Verset : 38

أَمۡ لَهُمۡ سُلَّمٞ يَسۡتَمِعُونَ فِيهِۖ فَلۡيَأۡتِ مُسۡتَمِعُهُم بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٍ

Ko kuwa suna da wani tsani ne da suke jiyo (zancen Allah) ta kansa[1]? To mai jiyowar tasu ya zo da wata hujja mabayyaniya


1- Watau cewa su ne masu gaskiya, Annabi () maqaryaci ne?


Sourate: Suratux Xur

Verset : 39

أَمۡ لَهُ ٱلۡبَنَٰتُ وَلَكُمُ ٱلۡبَنُونَ

Ko kuwa Shi ne zai zama mai ‘ya’ya mata, ku kuwa ku zamanto da ‘ya’ya maza?



Sourate: Suratux Xur

Verset : 40

أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ

Ko kuwa kana tambayar su wani lada ne, saboda haka bashi ya yi musu nauyi?



Sourate: Suratux Xur

Verset : 41

أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko kuwa sun san gaibu ne, saboda haka su ne suke rubutawa



Sourate: Suratux Xur

Verset : 42

أَمۡ يُرِيدُونَ كَيۡدٗاۖ فَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ هُمُ ٱلۡمَكِيدُونَ

Ko kuwa suna nufin (yi maka) makirci ne? To waxanda suka kafirce su ne waxanda makircinsu zai kama su



Sourate: Suratux Xur

Verset : 43

أَمۡ لَهُمۡ إِلَٰهٌ غَيۡرُ ٱللَّهِۚ سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Ko kuwa suna da wani abin bauta ne ba Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke tara (Shi da shi)



Sourate: Suratux Xur

Verset : 44

وَإِن يَرَوۡاْ كِسۡفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ سَاقِطٗا يَقُولُواْ سَحَابٞ مَّرۡكُومٞ

Da kuwa za su ga wani yanki na azaba mai faxowa daga sama da sai su ce: “Hadari ne haxaxxe.”



Sourate: Suratux Xur

Verset : 45

فَذَرۡهُمۡ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي فِيهِ يُصۡعَقُونَ

To ka rabu da su har sai sun haxu da ranarsu wadda za a karvi rayukansu a cikinta



Sourate: Suratux Xur

Verset : 46

يَوۡمَ لَا يُغۡنِي عَنۡهُمۡ كَيۡدُهُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Ranar da makircinsu ba zai maganta musu komai ba, kuma su ba za a taimake su ba



Sourate: Suratux Xur

Verset : 47

وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ عَذَابٗا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Lalle kuma waxanda suka yi zalunci suna da wata azabar daban[1] ban da wannan (ta lahira), sai dai kuma mafi yawansu ba su sani ba


1- Watau a nan duniya ta hanyar kisa a wajen yaqi ko kamu a matsayin ribatattu ko kuma azabar qabari bayan sun mutu.


Sourate: Suratux Xur

Verset : 48

وَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعۡيُنِنَاۖ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ

Kuma ka yi haquri da hukuncin Ubangijika, don ko lalle kana qarqashin lurarmu; kuma ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka lokacin da za ka tashi (daga bacci)



Sourate: Suratux Xur

Verset : 49

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَسَبِّحۡهُ وَإِدۡبَٰرَ ٱلنُّجُومِ

Da daddare kuma sai ka tsarkake Shi da kuma lokacin da taurari suka ba da baya