Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 31

وَقَالُواْ لَوۡلَا نُزِّلَ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانُ عَلَىٰ رَجُلٖ مِّنَ ٱلۡقَرۡيَتَيۡنِ عَظِيمٍ

Suka kuma ce: “Me ya hana a saukar da wannan Alqur’ani ga wani babban mutum, daga alqaryun nan guda biyu?”



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 32

أَهُمۡ يَقۡسِمُونَ رَحۡمَتَ رَبِّكَۚ نَحۡنُ قَسَمۡنَا بَيۡنَهُم مَّعِيشَتَهُمۡ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۚ وَرَفَعۡنَا بَعۡضَهُمۡ فَوۡقَ بَعۡضٖ دَرَجَٰتٖ لِّيَتَّخِذَ بَعۡضُهُم بَعۡضٗا سُخۡرِيّٗاۗ وَرَحۡمَتُ رَبِّكَ خَيۡرٞ مِّمَّا يَجۡمَعُونَ

Yanzu su ne suke raba rahamar Ubangijinka (ta annabci)? Mu ne Muka raba musu arzikinsu a rayuwar duniya. Muka kuma xaukaka darajojin sashinsu a kan sashi, don wani sashin ya riqi wani sashi mai yi masa hidima. Rahamar Ubangijinka kuma ita ta fi abin da suke tarawa (na duniya)



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 33

وَلَوۡلَآ أَن يَكُونَ ٱلنَّاسُ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ لَّجَعَلۡنَا لِمَن يَكۡفُرُ بِٱلرَّحۡمَٰنِ لِبُيُوتِهِمۡ سُقُفٗا مِّن فِضَّةٖ وَمَعَارِجَ عَلَيۡهَا يَظۡهَرُونَ

Ba don kuma kada mutane su zama iri xaya ba, da sai Mu sanya wa waxanda suke kafirce wa (Allah) Mai rahama rufi na azurfa a gidajensu, da kuma matattakala (irinta), da za su riqa hawa ta kansu



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 34

وَلِبُيُوتِهِمۡ أَبۡوَٰبٗا وَسُرُرًا عَلَيۡهَا يَتَّكِـُٔونَ

Kuma (Mu sanya wa) gidajen nasu qofofi da gadaje da za su riqa kishingixa a kansu



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 35

وَزُخۡرُفٗاۚ وَإِن كُلُّ ذَٰلِكَ لَمَّا مَتَٰعُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۚ وَٱلۡأٓخِرَةُ عِندَ رَبِّكَ لِلۡمُتَّقِينَ

Kuma (Mu sanya musu) zinariya. Duk waxannan ba komai ba ne sai xan jin daxin rayuwar duniya. Lahira kuma a wurin Ubangijinka ta masu taqawa ce



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 36

وَمَن يَعۡشُ عَن ذِكۡرِ ٱلرَّحۡمَٰنِ نُقَيِّضۡ لَهُۥ شَيۡطَٰنٗا فَهُوَ لَهُۥ قَرِينٞ

Wanda kuwa ya zama mai dundumi game da ambaton (Allah) Mai rahama, to za Mu haxa shi da Shaixan ya zama shi ne abokinsa



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 37

وَإِنَّهُمۡ لَيَصُدُّونَهُمۡ عَنِ ٱلسَّبِيلِ وَيَحۡسَبُونَ أَنَّهُم مُّهۡتَدُونَ

Lalle kuma su (shaixanun) tabbas suna kange su daga tafarki nagari, su kuma suna zato cewa lalle su shiryayyu ne



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 38

حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَنَا قَالَ يَٰلَيۡتَ بَيۡنِي وَبَيۡنَكَ بُعۡدَ ٱلۡمَشۡرِقَيۡنِ فَبِئۡسَ ٱلۡقَرِينُ

Har zuwa lokacin da suka zo mana (wato mutumin da shaixaninsa) sai ya ce: “Ina ma a ce tsakanina da kai akwai nisan gabas da yamma; to tir da aboki irinka.”



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 39

وَلَن يَنفَعَكُمُ ٱلۡيَوۡمَ إِذ ظَّلَمۡتُمۡ أَنَّكُمۡ فِي ٱلۡعَذَابِ مُشۡتَرِكُونَ

(Allah Ya ce da su): “A yau tun da kun riga kun yi zalunci zamantowarku tare a cikin azaba ba zai amfane ku ba



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 40

أَفَأَنتَ تُسۡمِعُ ٱلصُّمَّ أَوۡ تَهۡدِي ٱلۡعُمۡيَ وَمَن كَانَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Yanzu kai ka iya jiyar da kurame, ko kuma ka iya shiryar da makafi da wanda ya kasance cikin vata mabayyani?



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 41

فَإِمَّا نَذۡهَبَنَّ بِكَ فَإِنَّا مِنۡهُم مُّنتَقِمُونَ

To idan Muka karvi ranka, to lalle Mu Masu yi musu uquba ne



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 42

أَوۡ نُرِيَنَّكَ ٱلَّذِي وَعَدۡنَٰهُمۡ فَإِنَّا عَلَيۡهِم مُّقۡتَدِرُونَ

Ko kuma Muka nuna maka irin abin da muka yi musu alqawarin narko da shi, to lalle Mu Masu iko ne a kansu



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 43

فَٱسۡتَمۡسِكۡ بِٱلَّذِيٓ أُوحِيَ إِلَيۡكَۖ إِنَّكَ عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

To ka riqe abin da aka yi maka wahayinsa; lalle kai kana kan hanya madaidaiciya



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 44

وَإِنَّهُۥ لَذِكۡرٞ لَّكَ وَلِقَوۡمِكَۖ وَسَوۡفَ تُسۡـَٔلُونَ

Kuma lalle shi (Alqur’ani) xaukaka ce a gare ka da mutanenka; ba da daxewa ba kuma za a tambaye ku (game da haqqinsa)



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 45

وَسۡـَٔلۡ مَنۡ أَرۡسَلۡنَا مِن قَبۡلِكَ مِن رُّسُلِنَآ أَجَعَلۡنَا مِن دُونِ ٱلرَّحۡمَٰنِ ءَالِهَةٗ يُعۡبَدُونَ

Ka tambayi waxanda Muka aiko gabaninka daga manzanninmu, shin Mun sanya wasu ababen bauta da ake bauta musu ba (Allah) Mai rahama ba?



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 46

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا مُوسَىٰ بِـَٔايَٰتِنَآ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ وَمَلَإِيْهِۦ فَقَالَ إِنِّي رَسُولُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Haqiqa kuma Mun aiko Musa da ayoyinmu zuwa ga Fir’auna da manyan fadawansa, sai ya ce: “Lalle ni Manzo ne na Ubangijin talikai.”



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 47

فَلَمَّا جَآءَهُم بِـَٔايَٰتِنَآ إِذَا هُم مِّنۡهَا يَضۡحَكُونَ

To lokacin da ya zo musu da ayoyinmu sai ga su suna yi musu dariya



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 48

وَمَا نُرِيهِم مِّنۡ ءَايَةٍ إِلَّا هِيَ أَكۡبَرُ مِنۡ أُخۡتِهَاۖ وَأَخَذۡنَٰهُم بِٱلۡعَذَابِ لَعَلَّهُمۡ يَرۡجِعُونَ

Ba Mu kuma nuna musu wata aya ba sai wadda take ta fi `yar’uwarta girma; Muka kuma kama su da azaba don su dawo (kan hanya)



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 49

وَقَالُواْ يَـٰٓأَيُّهَ ٱلسَّاحِرُ ٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ بِمَا عَهِدَ عِندَكَ إِنَّنَا لَمُهۡتَدُونَ

Suka kuma ce: “Ya kai wannan mai sihiri, ka roqa mana Ubangijinka da abin da Ya yi maka wahayinsa (Ya yaye mana azaba), lalle mu tabbas za mu shiriya.”



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 50

فَلَمَّا كَشَفۡنَا عَنۡهُمُ ٱلۡعَذَابَ إِذَا هُمۡ يَنكُثُونَ

To lokacin da Muka yaye musu azabar sai ga su suna warware alqawari



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 51

وَنَادَىٰ فِرۡعَوۡنُ فِي قَوۡمِهِۦ قَالَ يَٰقَوۡمِ أَلَيۡسَ لِي مُلۡكُ مِصۡرَ وَهَٰذِهِ ٱلۡأَنۡهَٰرُ تَجۡرِي مِن تَحۡتِيٓۚ أَفَلَا تُبۡصِرُونَ

Fir’auna kuma ya yi shela a cikin mutanensa ya ce: “Ya ku mutanena, yanzu mulkin Misra ba nawa ba ne, kuma ga qoramu suna ta kwarara ta qarqashina, ko ba kwa gani ne?



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 52

أَمۡ أَنَا۠ خَيۡرٞ مِّنۡ هَٰذَا ٱلَّذِي هُوَ مَهِينٞ وَلَا يَكَادُ يُبِينُ

“A’a, ni na fi wannan wulaqantaccen wanda da qyar yake iya bayani



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 53

فَلَوۡلَآ أُلۡقِيَ عَلَيۡهِ أَسۡوِرَةٞ مِّن ذَهَبٍ أَوۡ جَآءَ مَعَهُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ مُقۡتَرِنِينَ

“To me ya hana a saukar masa da warawarai na zinare, ko kuma wasu mala’iku su zo tare da shi suna masu dafa masa baya?”



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 54

فَٱسۡتَخَفَّ قَوۡمَهُۥ فَأَطَاعُوهُۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ

Sai ya yi wasa da hankalin mutanensa sai suka bi shi. Lalle su sun kasance mutane ne fasiqai



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 55

فَلَمَّآ ءَاسَفُونَا ٱنتَقَمۡنَا مِنۡهُمۡ فَأَغۡرَقۡنَٰهُمۡ أَجۡمَعِينَ

To lokacin da suka fusata Mu sai Muka saukar musu da uquba, Muka nutsar da su ga baki xaya



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 56

فَجَعَلۡنَٰهُمۡ سَلَفٗا وَمَثَلٗا لِّلۡأٓخِرِينَ

Sai Muka sanya su ja-gaba (wajen hallakarwa), kuma wa’azi ga na baya



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 57

۞وَلَمَّا ضُرِبَ ٱبۡنُ مَرۡيَمَ مَثَلًا إِذَا قَوۡمُكَ مِنۡهُ يَصِدُّونَ

Lokacin da kuwa aka buga misali da (Isa) xan Maryamu, sai ga mutanenka suna ta annashawa game da shi[1]


1- Watau lokacin da Abdullahi xan Az-Ziba’ara ya ji faxar Allah cewa, waxanda aka bautawa ba Allah ba za su shiga wuta tare da masu bautarsu, sai ya ce, to idan haka ne Annabi Isa ma zai shiga wuta, wannan magana tasa ta faranta wa mushirikai rai sosai.


Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 58

وَقَالُوٓاْ ءَأَٰلِهَتُنَا خَيۡرٌ أَمۡ هُوَۚ مَا ضَرَبُوهُ لَكَ إِلَّا جَدَلَۢاۚ بَلۡ هُمۡ قَوۡمٌ خَصِمُونَ

Suka kuma ce: “Yanzu ababen bautar mu ne suka fi ko kuwa shi (Isa)?” Ba su buga maka misali da shi ba sai don son jayayya. Ba shakka su dai mutane ne masu tsananin jayayya



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 59

إِنۡ هُوَ إِلَّا عَبۡدٌ أَنۡعَمۡنَا عَلَيۡهِ وَجَعَلۡنَٰهُ مَثَلٗا لِّبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Shi (Isa) ba wani ba ne face bawa ne da Muka yi masa ni’ima, Muka kuma sanya shi abin buga misali ga Bani-Isra’ila



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 60

وَلَوۡ نَشَآءُ لَجَعَلۡنَا مِنكُم مَّلَـٰٓئِكَةٗ فِي ٱلۡأَرۡضِ يَخۡلُفُونَ

Da kuma za Mu ga dama tabbas da Mun sanya mala’iku ne za su maye gurbinku a bayan qasa