Sourate: Suratu Yasin

Verset : 31

أَلَمۡ يَرَوۡاْ كَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّنَ ٱلۡقُرُونِ أَنَّهُمۡ إِلَيۡهِمۡ لَا يَرۡجِعُونَ

Shin ba sa gani ne, al’ummu nawa ne Muka hallaka kafin su, cewa lalle kuwa ba sa dawowa zuwa gare su?



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 32

وَإِن كُلّٞ لَّمَّا جَمِيعٞ لَّدَيۡنَا مُحۡضَرُونَ

Kuma duk gaba xayansu wurinmu za a tattara su



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 33

وَءَايَةٞ لَّهُمُ ٱلۡأَرۡضُ ٱلۡمَيۡتَةُ أَحۡيَيۡنَٰهَا وَأَخۡرَجۡنَا مِنۡهَا حَبّٗا فَمِنۡهُ يَأۡكُلُونَ

Kuma wata aya ce a gare su (ganin) matacciyar qasar da Muka raya ta Muka fitar da qwaya daga gare ta, wadda kuma ita ce suke ci



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 34

وَجَعَلۡنَا فِيهَا جَنَّـٰتٖ مِّن نَّخِيلٖ وَأَعۡنَٰبٖ وَفَجَّرۡنَا فِيهَا مِنَ ٱلۡعُيُونِ

Muka kuma sanya gonaki na dabinai da na inabai a cikinta (qasar), Muka kuma vuvvugo da idanuwan ruwa daga gare ta



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 35

لِيَأۡكُلُواْ مِن ثَمَرِهِۦ وَمَا عَمِلَتۡهُ أَيۡدِيهِمۡۚ أَفَلَا يَشۡكُرُونَ

Don su ci daga ‘ya’yan (itacenta) da kuma abin da hannanyensu suka aikata. Me ya sa ba za su riqa godiya ba?



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 36

سُبۡحَٰنَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡأَزۡوَٰجَ كُلَّهَا مِمَّا تُنۢبِتُ ٱلۡأَرۡضُ وَمِنۡ أَنفُسِهِمۡ وَمِمَّا لَا يَعۡلَمُونَ

Tsarki ya tabbata ga wanda Ya halicci dangogin komai na maza da mata daga abin da qasa take tsirowa, kuma daga su kansu, da ma daga abin da ba su sani ba



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 37

وَءَايَةٞ لَّهُمُ ٱلَّيۡلُ نَسۡلَخُ مِنۡهُ ٱلنَّهَارَ فَإِذَا هُم مُّظۡلِمُونَ

Dare ma aya ne a gare su, wanda Muka savule yini daga gare shi[1], sai ga su cikin duhu


1- Watau Allah () yana gusar da rana daga dare sai kawai mutane su gan su cikin duhu.


Sourate: Suratu Yasin

Verset : 38

وَٱلشَّمۡسُ تَجۡرِي لِمُسۡتَقَرّٖ لَّهَاۚ ذَٰلِكَ تَقۡدِيرُ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡعَلِيمِ

Rana kuma tana gudu zuwa wurin da aka iyakance mata. Wannan tsari ne na (Allah) Mabuwayi, Masani



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 39

وَٱلۡقَمَرَ قَدَّرۡنَٰهُ مَنَازِلَ حَتَّىٰ عَادَ كَٱلۡعُرۡجُونِ ٱلۡقَدِيمِ

Wata kuma Mun qaddara masa masaukai, har ya koma kamar tsohuwar zarbar dabino



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 40

لَا ٱلشَّمۡسُ يَنۢبَغِي لَهَآ أَن تُدۡرِكَ ٱلۡقَمَرَ وَلَا ٱلَّيۡلُ سَابِقُ ٱلنَّهَارِۚ وَكُلّٞ فِي فَلَكٖ يَسۡبَحُونَ

Ba zai yiwu rana ta riski wata ba, dare kuma ba zai riga yini ba. Kowanne kuwa yana iyo ne a cikin falaki



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 41

وَءَايَةٞ لَّهُمۡ أَنَّا حَمَلۡنَا ذُرِّيَّتَهُمۡ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ

Kuma wata aya ce a gare su cewa Mu Muka xauki iyayensu a cikin jirgin ruwa wanda aka maqare[1]


1- Watau wanda Allah ya tserar da zuriyar Annabi Adamu () a cikinsa a zamanin Annabi Nuhu () bayan varkewar ruwan Xufana.


Sourate: Suratu Yasin

Verset : 42

وَخَلَقۡنَا لَهُم مِّن مِّثۡلِهِۦ مَا يَرۡكَبُونَ

Muka kuma halitta musu abin da suke hawa kwatankwacinsa



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 43

وَإِن نَّشَأۡ نُغۡرِقۡهُمۡ فَلَا صَرِيخَ لَهُمۡ وَلَا هُمۡ يُنقَذُونَ

Idan kuwa da Mun ga dama, sai Mu nutsar da su, don haka babu wani mai taimakon su, ba kuma za a kuvutar da su ba



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 44

إِلَّا رَحۡمَةٗ مِّنَّا وَمَتَٰعًا إِلَىٰ حِينٖ

Sai dai rahama daga gare Mu da kuma jin daxi zuwa wani lokaci



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 45

وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ ٱتَّقُواْ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيكُمۡ وَمَا خَلۡفَكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تُرۡحَمُونَ

Idan kuwa aka ce da su: “Ku kiyayi abin da yake gabanku da abin da yake bayanku[1], don a ji qan ku”, (sai su bijire)


1- Watau ranar lahira da suke fuskanta da abubuwan ban tsoron cikinta, da kuma duniya wadda suke ba ta baya.


Sourate: Suratu Yasin

Verset : 46

وَمَا تَأۡتِيهِم مِّنۡ ءَايَةٖ مِّنۡ ءَايَٰتِ رَبِّهِمۡ إِلَّا كَانُواْ عَنۡهَا مُعۡرِضِينَ

Babu wata aya daga ayoyin Ubangijinsu da za ta zo musu sai sun kasance masu bijire mata



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 47

وَإِذَا قِيلَ لَهُمۡ أَنفِقُواْ مِمَّا رَزَقَكُمُ ٱللَّهُ قَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَنُطۡعِمُ مَن لَّوۡ يَشَآءُ ٱللَّهُ أَطۡعَمَهُۥٓ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Idan kuma aka ce da su: “Ku ciyar daga abin da Allah Ya arzuta ku,” sai waxanda suka kafirta su ce wa waxanda suka yi imani: “Yanzu ma ciyar da wanda, da Allah Ya ga dama da ya ciyar da shi? Ba abin da kuke ciki in ban da vata mabayyani.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 48

وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا ٱلۡوَعۡدُ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Suna kuma cewa: “Yaushe ne wannan alqawarin, idan kun kasance masu gaskiya?”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 49

مَا يَنظُرُونَ إِلَّا صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ تَأۡخُذُهُمۡ وَهُمۡ يَخِصِّمُونَ

Ba abin da suke sauraro sai tsawa guda xaya da za ta far musu, a yayin da suke cikin hayaniyar rayuwa



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 50

فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ تَوۡصِيَةٗ وَلَآ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِمۡ يَرۡجِعُونَ

Don haka ba za su sami damar yin wata wasiyya ba, kuma ba za su iya koma wa wajen iyalinsu ba



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 51

وَنُفِخَ فِي ٱلصُّورِ فَإِذَا هُم مِّنَ ٱلۡأَجۡدَاثِ إِلَىٰ رَبِّهِمۡ يَنسِلُونَ

Aka kuma busa qaho[1], sai ga su suna fitowa daga qaburbura zuwa wurin Ubangijinsu


1- Watau busa ta biyu domin tashi.


Sourate: Suratu Yasin

Verset : 52

قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَا مَنۢ بَعَثَنَا مِن مَّرۡقَدِنَاۜۗ هَٰذَا مَا وَعَدَ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَصَدَقَ ٱلۡمُرۡسَلُونَ

Suka ce: “Kaiconmu, wane ne ya tashe mu daga makwancinmu?” (Sai a ce da su): “Ai wannnan shi ne abin da (Allah) Mai rahama Ya yi alqawarinsa, manzanni kuma sun yi gaskiya.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 53

إِن كَانَتۡ إِلَّا صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ فَإِذَا هُمۡ جَمِيعٞ لَّدَيۡنَا مُحۡضَرُونَ

Ba abin da zai kasance sai tsawa guda xaya, sai ga su gaba xaya an tattaro su gabanmu



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 54

فَٱلۡيَوۡمَ لَا تُظۡلَمُ نَفۡسٞ شَيۡـٔٗا وَلَا تُجۡزَوۡنَ إِلَّا مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

To a yau fa ba za a zalunci wani rai da komai ba, ba kuma za a saka muku ba sai da irin abin da kuka zamanto kuna aikatawa



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 55

إِنَّ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ ٱلۡيَوۡمَ فِي شُغُلٖ فَٰكِهُونَ

Lalle ‘yan Aljanna a yau suna cikin shagali, suna masu farin ciki



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 56

هُمۡ وَأَزۡوَٰجُهُمۡ فِي ظِلَٰلٍ عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِ مُتَّكِـُٔونَ

Su da matansu suna cikin inuwoyi kishingixe a kan gadaje



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 57

لَهُمۡ فِيهَا فَٰكِهَةٞ وَلَهُم مَّا يَدَّعُونَ

Suna da kayan marmari a cikinta, suna kuma da duk irin abin da suke nema



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 58

سَلَٰمٞ قَوۡلٗا مِّن رَّبّٖ رَّحِيمٖ

Sallama (za a riqa yi musu), magana ce daga Ubangiji Mai rahama



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 59

وَٱمۡتَٰزُواْ ٱلۡيَوۡمَ أَيُّهَا ٱلۡمُجۡرِمُونَ

Kuma (za a ce): “Ku ware a yau, ya ku waxannan masu manyan laifuka.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 60

۞أَلَمۡ أَعۡهَدۡ إِلَيۡكُمۡ يَٰبَنِيٓ ءَادَمَ أَن لَّا تَعۡبُدُواْ ٱلشَّيۡطَٰنَۖ إِنَّهُۥ لَكُمۡ عَدُوّٞ مُّبِينٞ

Yanzu ban umarce ku ba, ya ku ‘yan’adam, da cewa kada ku bauta wa Shaixan; lalle shi maqiyi ne mai bayyana (qiyayya)?