Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 31

قَالَ فَأۡتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

(Fir’auna) ya ce: “To ka zo da shi xin in ka kasance daga masu gaskiya.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 32

فَأَلۡقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعۡبَانٞ مُّبِينٞ

Sannan (Musa) ya jefa sandarsa sai ga ta (ta zama) kumurci quru-quru



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 33

وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِيَ بَيۡضَآءُ لِلنَّـٰظِرِينَ

Ya kuma zaro hannunsa (daga cikin rigarsa) sai ga shi fari fat ga masu gani



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 34

قَالَ لِلۡمَلَإِ حَوۡلَهُۥٓ إِنَّ هَٰذَا لَسَٰحِرٌ عَلِيمٞ

(Sai Fir’auna) ya ce da manyan mutanen da ke kewaye da shi: “Lalle wannan tabbas mai sihiri ne qwararre



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 35

يُرِيدُ أَن يُخۡرِجَكُم مِّنۡ أَرۡضِكُم بِسِحۡرِهِۦ فَمَاذَا تَأۡمُرُونَ

“Yana nufi ne ya fitar da ku daga qasarku da sihirinsa, to da me za ku yi umarni?”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 36

قَالُوٓاْ أَرۡجِهۡ وَأَخَاهُ وَٱبۡعَثۡ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Suka ce: “Ka dakatar da shi tare da xan’uwansa, kuma ka aika manzanni cikin birane su tattaro maka (masu sihiri)



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 37

يَأۡتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٖ

“Su zo maka da duk wani mai sihiri qwararre.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 38

فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَٰتِ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

Sai aka tattara masu sihirin (don su zo) a qayyadajjiyar rana sananniya[1]


1- Watau ranar bikin idinsu.


Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 39

وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلۡ أَنتُم مُّجۡتَمِعُونَ

Aka kuma ce da mutane: “Shin za ku tattaru



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 40

لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ

“Don mu goyi bayan masu sihiri idan har sun kasance su ne masu galaba?”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 41

فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُواْ لِفِرۡعَوۡنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجۡرًا إِن كُنَّا نَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبِينَ

Sannan lokacin da masu sihirin suka zo sai suka ce da Fir’auna: “Shin muna da wani lada (da za ka ba mu) in har mun zama mu ne masu galaba?”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 42

قَالَ نَعَمۡ وَإِنَّكُمۡ إِذٗا لَّمِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ

(Fir’auna) ya ce: “Na’am, kuma ma idan haka ya faru, to tabbas za ku zama daga makusanta.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 43

قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلۡقُواْ مَآ أَنتُم مُّلۡقُونَ

(Sai Musa) ya ce da su: “Ku jefa duk abin da za ku jefa.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 44

فَأَلۡقَوۡاْ حِبَالَهُمۡ وَعِصِيَّهُمۡ وَقَالُواْ بِعِزَّةِ فِرۡعَوۡنَ إِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبُونَ

Sai suka jefa igiyoyinsu da sandunansu suka kuma ce: “Lalle da izzar Fir’auna tabbas mu ne masu galaba.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 45

فَأَلۡقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلۡقَفُ مَا يَأۡفِكُونَ

Sai Musa ya jefa sandarsa, sai ga ta tana lanqwame duk abin da suke qagowa (na sihiri)



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 46

فَأُلۡقِيَ ٱلسَّحَرَةُ سَٰجِدِينَ

Sai aka durqusar da masu sihirin suna masu sujjada



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 47

قَالُوٓاْ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Suka ce: “Mun yi imani da Ubangijin talikai



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 48

رَبِّ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

“Ubangijin Musa da Haruna.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 49

قَالَ ءَامَنتُمۡ لَهُۥ قَبۡلَ أَنۡ ءَاذَنَ لَكُمۡۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِي عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحۡرَ فَلَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَرۡجُلَكُم مِّنۡ خِلَٰفٖ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمۡ أَجۡمَعِينَ

(Sai Fir’auna) ya ce: “Yanzu kwa yi imani da shi tun kafin in ba ku izini? Lalle tabbas shi ne babbanku wanda ya koya muku sihiri; to tabbas kuwa kwa sani. Lalle zan yanyanke hannayenku da qafafuwanku a tarnaqe, kuma tabbas zan gicciye ku gaba xaya!”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 50

قَالُواْ لَا ضَيۡرَۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ

Sai suka ce: “Ai ba damuwa; lalle mu masu komawa ne zuwa ga Ubangijinmu



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 51

إِنَّا نَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَٰيَٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Lalle mu muna kwaxayin Ubangijinmu Ya gafarta mana kurakuranmu saboda zamantowarmu farkon muminai.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 52

۞وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِيٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Muka kuma yi wa Musa wahayi cewa: “Ka tafi cikin dare tare da bayina, lalle ku za a biyo bayanku.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 53

فَأَرۡسَلَ فِرۡعَوۡنُ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Sai Fir’auna ya aika zuwa birane don a tattaro (mayaqa)



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 54

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرۡذِمَةٞ قَلِيلُونَ

(Fir’auna yana cewa): “Lalle waxannan tabbas ‘yan tsirarin jama’a ne



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 55

وَإِنَّهُمۡ لَنَا لَغَآئِظُونَ

“Kuma haqiqa su lalle suna fusata mu



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 56

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ

“Lalle kuma mu tabbas gaba xayanmu masu kwana cikin shiri ne.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 57

فَأَخۡرَجۡنَٰهُم مِّن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

(Allah Ya ce): Sai Muka fitar da su daga gonaki da kuma idandunan ruwa



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 58

وَكُنُوزٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ

Da taskoki da kuma mazauni na alfarma



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 59

كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Kamar haka ne Muka gadar da su ga Banu-Isra’ila



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 60

فَأَتۡبَعُوهُم مُّشۡرِقِينَ

Sai suka bi bayansu a lokacin fitowar rana