Sourate: Suratu Yasin

Verset : 1

يسٓ

YA SIN[1]


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


Sourate: Suratu Yasin

Verset : 2

وَٱلۡقُرۡءَانِ ٱلۡحَكِيمِ

Na rantse da Alqur’ani mai hikima



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 3

إِنَّكَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Lalle kai (Manzon Allah) tabbas kana daga cikin manzanni



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 4

عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

(Kana) a kan tafarki madaidaici



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 5

تَنزِيلَ ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

(Alqur’ani) saukarwar (Allah) Mabuwayi Mai jin qai ne



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 6

لِتُنذِرَ قَوۡمٗا مَّآ أُنذِرَ ءَابَآؤُهُمۡ فَهُمۡ غَٰفِلُونَ

Don ka gargaxi mutanen da ba a yi wa iyayensu gargaxi ba[1], don haka kuwa suna cikin gafala


1- Su ne al’ummar Larabawa waxanda wani annabi bai zo musu ba.


Sourate: Suratu Yasin

Verset : 7

لَقَدۡ حَقَّ ٱلۡقَوۡلُ عَلَىٰٓ أَكۡثَرِهِمۡ فَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Haqiqa hukuncin Allah (na azaba) ya wajaba a kan mafiya yawansu, don ba za su yi imani ba



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 8

إِنَّا جَعَلۡنَا فِيٓ أَعۡنَٰقِهِمۡ أَغۡلَٰلٗا فَهِيَ إِلَى ٱلۡأَذۡقَانِ فَهُم مُّقۡمَحُونَ

Lalle Mun sanya ququmai a wuyoyinsu har zuwa havovinsu, don haka kawunansu a xage suke



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 9

وَجَعَلۡنَا مِنۢ بَيۡنِ أَيۡدِيهِمۡ سَدّٗا وَمِنۡ خَلۡفِهِمۡ سَدّٗا فَأَغۡشَيۡنَٰهُمۡ فَهُمۡ لَا يُبۡصِرُونَ

Muka kuma sanya wani shamaki a gabansu da kuma shamaki a bayansu, sai Muka lulluve musu (idanuwa), don haka ba sa gani



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 10

وَسَوَآءٌ عَلَيۡهِمۡ ءَأَنذَرۡتَهُمۡ أَمۡ لَمۡ تُنذِرۡهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Kuma duk xaya ne a wurinsu ko ka yi musu gargaxi ko ba ka yi musu gargaxi ba, ba za su yi imani ba



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 11

إِنَّمَا تُنذِرُ مَنِ ٱتَّبَعَ ٱلذِّكۡرَ وَخَشِيَ ٱلرَّحۡمَٰنَ بِٱلۡغَيۡبِۖ فَبَشِّرۡهُ بِمَغۡفِرَةٖ وَأَجۡرٖ كَرِيمٍ

Kana yin gargaxi ne kawai ga wanda ya bi umarnin Alqur’ani, ya kuma ji tsoron Allah ba tare da ya gan Shi ba; sai ka yi masa albishir da samun gafara da lada na karamci



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 12

إِنَّا نَحۡنُ نُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰ وَنَكۡتُبُ مَا قَدَّمُواْ وَءَاثَٰرَهُمۡۚ وَكُلَّ شَيۡءٍ أَحۡصَيۡنَٰهُ فِيٓ إِمَامٖ مُّبِينٖ

Lalle Mu ne za Mu raya matattu, Muke kuma rubuta irin abubuwan da suka gabatar (a rayuwarsu) da kuma abin da suka bari a bayansu (bayan mutuwa). Kowane abu kuma Mun qididdige shi a cikin Lauhul-Mahafuzu



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 13

وَٱضۡرِبۡ لَهُم مَّثَلًا أَصۡحَٰبَ ٱلۡقَرۡيَةِ إِذۡ جَآءَهَا ٱلۡمُرۡسَلُونَ

Kuma ka ba su misali da mutanen wata alqarya lokacin da manzannin suka zo mata



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 14

إِذۡ أَرۡسَلۡنَآ إِلَيۡهِمُ ٱثۡنَيۡنِ فَكَذَّبُوهُمَا فَعَزَّزۡنَا بِثَالِثٖ فَقَالُوٓاْ إِنَّآ إِلَيۡكُم مُّرۡسَلُونَ

A yayin da Muka aika musu (manzanni) biyu sai suka qaryata su, sannan Muka qarfafe su da na uku, sai suka ce: “Lalle mu manzanni ne zuwa gare ku.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 15

قَالُواْ مَآ أَنتُمۡ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا وَمَآ أَنزَلَ ٱلرَّحۡمَٰنُ مِن شَيۡءٍ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا تَكۡذِبُونَ

Suka ce: “Ku ai ba kowa ba ne face mutane kamarmu, kuma (Allah) Mai rahama bai saukar da komai ba, ku dai ba abin da kuke yi sai qarya.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 16

قَالُواْ رَبُّنَا يَعۡلَمُ إِنَّآ إِلَيۡكُمۡ لَمُرۡسَلُونَ

Suka ce: “Ubangijinmu Yana sane da cewa mu lalle tabbas manzanni ne zuwa gare ku



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 17

وَمَا عَلَيۡنَآ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُ ٱلۡمُبِينُ

“Kuma babu wani abu a kanmu sai isar da aike bayyananne.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 18

قَالُوٓاْ إِنَّا تَطَيَّرۡنَا بِكُمۡۖ لَئِن لَّمۡ تَنتَهُواْ لَنَرۡجُمَنَّكُمۡ وَلَيَمَسَّنَّكُم مِّنَّا عَذَابٌ أَلِيمٞ

Suka ce: “Mu dai lalle mun camfa ku, tabbas idan ba ku bari ba to za mu jefe ku, kuma tabbas za ku gamu da azaba mai raxaxi daga gare mu.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 19

قَالُواْ طَـٰٓئِرُكُم مَّعَكُمۡ أَئِن ذُكِّرۡتُمۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ مُّسۡرِفُونَ

Suka ce: “Camfinku ya qare a kanku. Yanzu don an yi muku gargaxi ne (za ku faxi haka?) A’a, ku dai mutane ne mavarnata.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 20

وَجَآءَ مِنۡ أَقۡصَا ٱلۡمَدِينَةِ رَجُلٞ يَسۡعَىٰ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱتَّبِعُواْ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Wani mutum kuma ya zo daga can qarshen gari yana sauri ya ce: “Ya ku mutanena, ku bi waxannan manzannin



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 21

ٱتَّبِعُواْ مَن لَّا يَسۡـَٔلُكُمۡ أَجۡرٗا وَهُم مُّهۡتَدُونَ

“Ku bi waxanda ba sa tambayar ku wani lada, ga su kuma shiryayyu



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 22

وَمَالِيَ لَآ أَعۡبُدُ ٱلَّذِي فَطَرَنِي وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

“Ni kuma me zai hana ni in bauta wa wanda Ya halicce ni, kuma gare Shi ne za a komar da ku?



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 23

ءَأَتَّخِذُ مِن دُونِهِۦٓ ءَالِهَةً إِن يُرِدۡنِ ٱلرَّحۡمَٰنُ بِضُرّٖ لَّا تُغۡنِ عَنِّي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَا يُنقِذُونِ

“Yanzu na riqi wasu ababen bauta ba Shi ba, alhali kuwa idan (Allah) Mai rahama Ya nufe ni da wata cuta, cetonsu ba zai amfana min komai ba, kuma ba za su iya tsamo ni ba?



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 24

إِنِّيٓ إِذٗا لَّفِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٍ

“Lalle ni idan na yi haka to tabbas na zama cikin vata mabayyani



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 25

إِنِّيٓ ءَامَنتُ بِرَبِّكُمۡ فَٱسۡمَعُونِ

“Lalle ni na yi imani da Ubangijinku, sai ku saurare ni.”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 26

قِيلَ ٱدۡخُلِ ٱلۡجَنَّةَۖ قَالَ يَٰلَيۡتَ قَوۡمِي يَعۡلَمُونَ

Aka ce (da shi): “Shiga Aljanna.” Ya ce: “Kaicon mutanena, ina ma da suna sane?



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 27

بِمَا غَفَرَ لِي رَبِّي وَجَعَلَنِي مِنَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ

“Da gafarar da Ubangijina Ya yi min, Ya kuma sanya ni cikin waxanda aka karrama?”



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 28

۞وَمَآ أَنزَلۡنَا عَلَىٰ قَوۡمِهِۦ مِنۢ بَعۡدِهِۦ مِن جُندٖ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا كُنَّا مُنزِلِينَ

Ba Mu kuma saukar da wata runduna (ta mala’iku) a kan mutanensa daga sama ba a bayansa, ba Mu kuma saba saukarwa ba



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 29

إِن كَانَتۡ إِلَّا صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ فَإِذَا هُمۡ خَٰمِدُونَ

Ba abin da ya kasance sai tsawa guda xaya, sai ga su matattu



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 30

يَٰحَسۡرَةً عَلَى ٱلۡعِبَادِۚ مَا يَأۡتِيهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

Nadama ta tabbata ga bayi (masu qaryatawa), ba wani manzo da zai zo musu sai sun zamanto suna yi masa izgili