Sourate: Suratul Hijr

Verset : 1

الٓرۚ تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ وَقُرۡءَانٖ مُّبِينٖ

ALIF LAM RA[1]. Waxannan ayoyin Littafi ne, kuma abin karatu ne mabayyani


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 2

رُّبَمَا يَوَدُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَوۡ كَانُواْ مُسۡلِمِينَ

Waxanda suka kafirta za su riqa burin ina ma da sun zama Musulmai[1]


1- Watau a ranar alqiyama ko kuma lokacin mutuwarsa.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 3

ذَرۡهُمۡ يَأۡكُلُواْ وَيَتَمَتَّعُواْ وَيُلۡهِهِمُ ٱلۡأَمَلُۖ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ

Bar su su ci kuma su ji daxi, buri kuma ya shagaltar da su ; sai dai ba da daxewa ba za su sani



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 4

وَمَآ أَهۡلَكۡنَا مِن قَرۡيَةٍ إِلَّا وَلَهَا كِتَابٞ مَّعۡلُومٞ

Ba wata alqarya da Muka hallakar face tana da wani sanannen lokaci (a wurin Allah)



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 5

مَّا تَسۡبِقُ مِنۡ أُمَّةٍ أَجَلَهَا وَمَا يَسۡتَـٔۡخِرُونَ

Ba wata al’umma da za ta riga lokacin da aka iyakance mata ko su jinkirta bayansa



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 6

وَقَالُواْ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِي نُزِّلَ عَلَيۡهِ ٱلذِّكۡرُ إِنَّكَ لَمَجۡنُونٞ

Suka kuma ce: “Ya kai wanda aka saukar wa da Alqur’ani, lalle kai tabbas mahaukaci ne



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 7

لَّوۡمَا تَأۡتِينَا بِٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Me zai hana ka zo mana da mala’iku idan kana daga cikin masu gaskiya?”



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 8

مَا نُنَزِّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ إِلَّا بِٱلۡحَقِّ وَمَا كَانُوٓاْ إِذٗا مُّنظَرِينَ

(Allah ya ce): “Ba ma saukar da mala’iku sai da gaskiya[1]; inda kuwa haka ya faru, to ba za a saurara musu ba.”


1- Watau sai idan lokacin da za a hallaka su ya zo.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 9

إِنَّا نَحۡنُ نَزَّلۡنَا ٱلذِّكۡرَ وَإِنَّا لَهُۥ لَحَٰفِظُونَ

Lalle Mu Muka saukar da Alqur’ani, lalle kuma tabbas Mu za Mu kiyaye shi



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 10

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا مِن قَبۡلِكَ فِي شِيَعِ ٱلۡأَوَّلِينَ

Haqiqa kuma Mun aiko (manzanni) a gabaninka cikin al’ummun farko



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 11

وَمَا يَأۡتِيهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

Ba kuwa wani manzo da zai zo musu sai sun zamanto suna yi masa izgili



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 12

كَذَٰلِكَ نَسۡلُكُهُۥ فِي قُلُوبِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Kamar haka ne Muke shigar da shi cikin zukatan kafirai



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 13

لَا يُؤۡمِنُونَ بِهِۦ وَقَدۡ خَلَتۡ سُنَّةُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Ba za su yi imani da shi ba; haqiqa kuma hanyar (sakamakon) mutanen farko ta gabata (wato hallakarwa)



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 14

وَلَوۡ فَتَحۡنَا عَلَيۡهِم بَابٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ فَظَلُّواْ فِيهِ يَعۡرُجُونَ

Idan da Mun buxe musu qofar sama har suka dinga hawa ta cikinta



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 15

لَقَالُوٓاْ إِنَّمَا سُكِّرَتۡ أَبۡصَٰرُنَا بَلۡ نَحۡنُ قَوۡمٞ مَّسۡحُورُونَ

Tabbas da sun ce: “Ai an yi mana rufa-ido ne kawai; a’a, kai mu dai mutane ne da aka sihirce.”



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 16

وَلَقَدۡ جَعَلۡنَا فِي ٱلسَّمَآءِ بُرُوجٗا وَزَيَّنَّـٰهَا لِلنَّـٰظِرِينَ

Haqiqa kuma Mun sanya taurari a sama, Muka kuma qawata ta ga masu gani



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 17

وَحَفِظۡنَٰهَا مِن كُلِّ شَيۡطَٰنٖ رَّجِيمٍ

Kuma Muka kiyaye ta daga duk wani shaixani la’ananne



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 18

إِلَّا مَنِ ٱسۡتَرَقَ ٱلسَّمۡعَ فَأَتۡبَعَهُۥ شِهَابٞ مُّبِينٞ

Sai dai wanda ya yi satar sauraro, sannan sai tauraro mai harshen wuta ya biyo shi



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 19

وَٱلۡأَرۡضَ مَدَدۡنَٰهَا وَأَلۡقَيۡنَا فِيهَا رَوَٰسِيَ وَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ شَيۡءٖ مَّوۡزُونٖ

Qasa kuma Mun shimfixa ta Muka sanya manyan duwatsu a cikinta, Muka kuma tsiro da kowane abu a cikinta qayyadajje



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 20

وَجَعَلۡنَا لَكُمۡ فِيهَا مَعَٰيِشَ وَمَن لَّسۡتُمۡ لَهُۥ بِرَٰزِقِينَ

Muka kuma sanya muku kayan rayuwa a cikinta, da kuma wanda ba ku ne kuke arzuta shi ba (wato bayi da dabbobi)



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 21

وَإِن مِّن شَيۡءٍ إِلَّا عِندَنَا خَزَآئِنُهُۥ وَمَا نُنَزِّلُهُۥٓ إِلَّا بِقَدَرٖ مَّعۡلُومٖ

Babu wani abu wanda taskokinsa ba a wurinmu suke ba, kuma ba ma saukar da shi sai daidai wani gwargwado sananne



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 22

وَأَرۡسَلۡنَا ٱلرِّيَٰحَ لَوَٰقِحَ فَأَنزَلۡنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَسۡقَيۡنَٰكُمُوهُ وَمَآ أَنتُمۡ لَهُۥ بِخَٰزِنِينَ

Muka kuma aiko da iska mai yin barbara (ga giza-gizai), sai Muka saukar da ruwa daga sama Muka shayar da ku da shi, ba kuma ku ne masu taskance shi ba



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 23

وَإِنَّا لَنَحۡنُ نُحۡيِۦ وَنُمِيتُ وَنَحۡنُ ٱلۡوَٰرِثُونَ

Lalle kuma tabbas Mu Muke rayawa kuma Muke kashewa, Mu ne kuma Masu gaje (komai)



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 24

وَلَقَدۡ عَلِمۡنَا ٱلۡمُسۡتَقۡدِمِينَ مِنكُمۡ وَلَقَدۡ عَلِمۡنَا ٱلۡمُسۡتَـٔۡخِرِينَ

Haqiqa kuma Mun san marigaya daga cikinku kuma haqiqa Mun san masu biyowa baya[1]


1- Watau Allah () ya san waxanda za a riga haihuwarsu su riga mutuwa, ya san kuma waxanda za a haife su, daga baya su mutu.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 25

وَإِنَّ رَبَّكَ هُوَ يَحۡشُرُهُمۡۚ إِنَّهُۥ حَكِيمٌ عَلِيمٞ

Lalle Ubangijinka kuma Shi zai tattara su. Lalle shi Mai hikima ne, Masani



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 26

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِن صَلۡصَٰلٖ مِّنۡ حَمَإٖ مَّسۡنُونٖ

Kuma haqiqa Mun halicci mutum daga busasshen tavo mai amo na wani yumvu mai wari



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 27

وَٱلۡجَآنَّ خَلَقۡنَٰهُ مِن قَبۡلُ مِن نَّارِ ٱلسَّمُومِ

Aljani kuwa Mun halicce shi ne gabanin (halittar mutum) daga wuta mai tsananin zafi



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 28

وَإِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي خَٰلِقُۢ بَشَرٗا مِّن صَلۡصَٰلٖ مِّنۡ حَمَإٖ مَّسۡنُونٖ

Kuma (ka tuna) lokacin da Ubangijinka ya ce da mala’iku: “Lalle Ni zan halicci mutum daga busasshen tavo mai amo na wani yumvu mai wari



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 29

فَإِذَا سَوَّيۡتُهُۥ وَنَفَخۡتُ فِيهِ مِن رُّوحِي فَقَعُواْ لَهُۥ سَٰجِدِينَ

“To idan Na daidaita shi Na kuma busa masa daga ruhina, to ku faxi kuna masu sujjada a gare shi.”



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 30

فَسَجَدَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ كُلُّهُمۡ أَجۡمَعُونَ

Sai mala’iku dukkaninsu suka yi sujjada gaba xaya