Sourate: Suratul Muzzammil

Verset : 20

۞إِنَّ رَبَّكَ يَعۡلَمُ أَنَّكَ تَقُومُ أَدۡنَىٰ مِن ثُلُثَيِ ٱلَّيۡلِ وَنِصۡفَهُۥ وَثُلُثَهُۥ وَطَآئِفَةٞ مِّنَ ٱلَّذِينَ مَعَكَۚ وَٱللَّهُ يُقَدِّرُ ٱلَّيۡلَ وَٱلنَّهَارَۚ عَلِمَ أَن لَّن تُحۡصُوهُ فَتَابَ عَلَيۡكُمۡۖ فَٱقۡرَءُواْ مَا تَيَسَّرَ مِنَ ٱلۡقُرۡءَانِۚ عَلِمَ أَن سَيَكُونُ مِنكُم مَّرۡضَىٰ وَءَاخَرُونَ يَضۡرِبُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ يَبۡتَغُونَ مِن فَضۡلِ ٱللَّهِ وَءَاخَرُونَ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ فَٱقۡرَءُواْ مَا تَيَسَّرَ مِنۡهُۚ وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَأَقۡرِضُواْ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗاۚ وَمَا تُقَدِّمُواْ لِأَنفُسِكُم مِّنۡ خَيۡرٖ تَجِدُوهُ عِندَ ٱللَّهِ هُوَ خَيۡرٗا وَأَعۡظَمَ أَجۡرٗاۚ وَٱسۡتَغۡفِرُواْ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمُۢ

Lalle Ubangijinka Yana sane da cewa kai kana tsayawa qasa da kashi biyu cikin uku na dare, da kuma rabinsa, da kuma xaya bisa ukunsa, kai da wata jama’ar da take tare da kai. Allah ne kuma Yake qaddara dare da rana. Ya san kuma cewa, ba za ku iya qididdige (sa’o’insa) ba, don haka sai Ya yafe muku; to sai ku karanta abin da ya sauqaqa daga Alqur’ani. Ya san cewa daga cikinku akwai waxanda za su kasance marasa lafiya, waxansu kuma suna tafiya a bayan qasa don fatauci suna neman falala daga Allah, waxansu kuma suna yin yaqi saboda Allah; to sai ku karanta abin da ya sauqaqa daga gare shi (Alqur’ani). Ku kuma tsayar da salla, ku kuma ba da zakka, kuma ku bai wa Allah rance kyakkyawa[1]. Kuma abin da kuka gabatar wa kanku na wani alheri, to za ku same shi wurin Allah, shi ya fi alheri ya kuma fi girman lada. Ku kuma nemi gafarar Allah; lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai


1- Watau su ciyar da dukiyoyinsu don Allah wuraren da suka dace.


Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 56

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ

Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 37

أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ

Shin bai kasance wani xigo na maniyyi da ake zuba shi (a mahaifa) ba?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 38

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ

Sannan ya zama gudan jini sannan (Allah) Ya halicce (shi) sai Ya daidaita (shi)?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 39

فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Sannan Ya halicci dangi biyu daga gare shi, namiji da mace?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 40

أَلَيۡسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحۡـِۧيَ ٱلۡمَوۡتَىٰ

Yanzu wannan bai zama Mai iko a kan ya raya matattu ba?



Sourate: Suratul Insan

Verset : 28

نَّحۡنُ خَلَقۡنَٰهُمۡ وَشَدَدۡنَآ أَسۡرَهُمۡۖ وَإِذَا شِئۡنَا بَدَّلۡنَآ أَمۡثَٰلَهُمۡ تَبۡدِيلًا

Mu Muka halicce su Muka kuma qarfafa gavovinsu; idan kuwa Muka ga dama sai Mu musanya irinsu (kyakkyawar) musanyawa



Sourate: Suratul Insan

Verset : 29

إِنَّ هَٰذِهِۦ تَذۡكِرَةٞۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ سَبِيلٗا

Lalle wannan wa’azi ne; saboda haka wanda ya ga dama sai ya riqi hanya zuwa ga Ubangijinsa



Sourate: Suratul Insan

Verset : 30

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Kuma ba ganin damarku ba ce sai abin da Allah ya ga dama. Lalle Allah Ya kasance Masani, Mai hikima



Sourate: Suratul Insan

Verset : 31

يُدۡخِلُ مَن يَشَآءُ فِي رَحۡمَتِهِۦۚ وَٱلظَّـٰلِمِينَ أَعَدَّ لَهُمۡ عَذَابًا أَلِيمَۢا

Yana shigar da wanda Ya ga dama cikin rahamarsa. Azzalumai kuwa Ya tanadar musu azaba mai raxaxi



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 27

ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا

Yanzu ku ne halittarku ta fi tsanani ko kuwa sama wadda Shi ne Ya gina ta?



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 28

رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Ya xaukaka rufinta Ya kuma daidaita ta[1]


1- Watau ya zama babu wata varaka ko tsagewa ko wani aibi tare da ita.


Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 29

وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Ya lulluve darenta da duhu Ya kuma fitar da hasken hantsinta



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 30

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Qasa kuma bayan haka Ya shimfixa ta



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 31

أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا

Ya fitar da ruwanta da makiyayarta daga gare ta



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 32

وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا

Duwatsu kuma Ya kafa su



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 33

مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ

Don jin daxinku da na dabbobinku



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 22

ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ

Sannan in Ya ga dama Ya tashe shi



Sourate: Suratut Takwir

Verset : 29

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ku kuma ba za ku iya ganin dama ba sai Allah Ubangijin talikai Ya ga dama



Sourate: Suratul Infixar

Verset : 7

ٱلَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ

Wanda Ya halicce ka Ya kuma daidaita ka Ya miqar da kai[1]?


1- Watau ya lura da girman ni’imar da ya yi masa yayin da bai yi masa irin halittar jaki ba ko ta biri ko ta kare.


Sourate: Suratul Infixar

Verset : 8

فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ

Ya harhaxa ka cikin irin surar da Ya ga dama?



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 14

إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ

Lalle ya yi zaton ba zai koma (ga Allah) ba



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 15

بَلَىٰٓۚ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرٗا

Haka yake, (zai koma), lalle Ubangijinsa Ya kasance Mai ganin sa ne



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 23

وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا يُوعُونَ

Allah kuwa (Shi) Ya fi sanin abin da suke voyewa (a zukatansu)



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 9

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Wanda Yake da mulkin sammai da qasa. Allah kuma Mai ganin komai ne



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 16

فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Mai aikata abin da Yake nufi