Sourate: Suratut Tauba

Verset : 120

مَا كَانَ لِأَهۡلِ ٱلۡمَدِينَةِ وَمَنۡ حَوۡلَهُم مِّنَ ٱلۡأَعۡرَابِ أَن يَتَخَلَّفُواْ عَن رَّسُولِ ٱللَّهِ وَلَا يَرۡغَبُواْ بِأَنفُسِهِمۡ عَن نَّفۡسِهِۦۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ لَا يُصِيبُهُمۡ ظَمَأٞ وَلَا نَصَبٞ وَلَا مَخۡمَصَةٞ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلَا يَطَـُٔونَ مَوۡطِئٗا يَغِيظُ ٱلۡكُفَّارَ وَلَا يَنَالُونَ مِنۡ عَدُوّٖ نَّيۡلًا إِلَّا كُتِبَ لَهُم بِهِۦ عَمَلٞ صَٰلِحٌۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُضِيعُ أَجۡرَ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Bai kamata ba ga mutanen Madina da waxanda suke kewaye da su daga mazauna qauye su noqe su qi bin Manzon Allah, ko kuma su zavi kansu fiye da shi. Wannan kuwa saboda ba wata qishirwa ko wahala ko yunwa da za ta same su a kan hanyar Allah, kuma ba za su taka wani wuri ba da zai vata wa kafirai rai, kuma ba za su tafka wa abokan gaba wata hasara ba sai an rubuta musu lada saboda shi (wato kowane xaya daga abubuwan da aka zana). Lalle Allah ba Ya tozarta ladan masu kyautatawa



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 121

وَلَا يُنفِقُونَ نَفَقَةٗ صَغِيرَةٗ وَلَا كَبِيرَةٗ وَلَا يَقۡطَعُونَ وَادِيًا إِلَّا كُتِبَ لَهُمۡ لِيَجۡزِيَهُمُ ٱللَّهُ أَحۡسَنَ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Ba kuma za su bayar da wata sadaka ba, qarama ko kuma babba, kuma ba wani kwazazzabo da za su keta sai an rubuta musu ladansu don Allah Ya saka musu da mafi kyawun abin da suka zamanto suna aikatawa



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 122

۞وَمَا كَانَ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ لِيَنفِرُواْ كَآفَّةٗۚ فَلَوۡلَا نَفَرَ مِن كُلِّ فِرۡقَةٖ مِّنۡهُمۡ طَآئِفَةٞ لِّيَتَفَقَّهُواْ فِي ٱلدِّينِ وَلِيُنذِرُواْ قَوۡمَهُمۡ إِذَا رَجَعُوٓاْ إِلَيۡهِمۡ لَعَلَّهُمۡ يَحۡذَرُونَ

Bai kamata muminai su fita yaqi gaba xaya ba. Me zai hana wasu jama’a daga kowace qabila (su zauna) don su koyi ilimin addini, su kuma yi wa mutanensu gargaxi idan sun dawo musu don su kiyaye (dokokin Allah)?



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 123

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قَٰتِلُواْ ٱلَّذِينَ يَلُونَكُم مِّنَ ٱلۡكُفَّارِ وَلۡيَجِدُواْ فِيكُمۡ غِلۡظَةٗۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلۡمُتَّقِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yaqi kafirai waxanda suke maqota da ku, kuma su sami kausasawa daga wajenku. Ku kuma sani cewa Allah Yana tare da masu taqawa



Sourate: Suratul Hajji

Verset : 39

أُذِنَ لِلَّذِينَ يُقَٰتَلُونَ بِأَنَّهُمۡ ظُلِمُواْۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ نَصۡرِهِمۡ لَقَدِيرٌ

An yi izini (na yin yaqi) ga waxanda ake yaqa[1] don ko lalle an zalunce su. Lalle kuma Allah Mai iko ne bisa taimakon su


1- Watau sahabban Annabi () waxanda kafirai a lokacin suke yaqar su.


Sourate: Suratul Hajji

Verset : 40

ٱلَّذِينَ أُخۡرِجُواْ مِن دِيَٰرِهِم بِغَيۡرِ حَقٍّ إِلَّآ أَن يَقُولُواْ رَبُّنَا ٱللَّهُۗ وَلَوۡلَا دَفۡعُ ٱللَّهِ ٱلنَّاسَ بَعۡضَهُم بِبَعۡضٖ لَّهُدِّمَتۡ صَوَٰمِعُ وَبِيَعٞ وَصَلَوَٰتٞ وَمَسَٰجِدُ يُذۡكَرُ فِيهَا ٱسۡمُ ٱللَّهِ كَثِيرٗاۗ وَلَيَنصُرَنَّ ٱللَّهُ مَن يَنصُرُهُۥٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَقَوِيٌّ عَزِيزٌ

(Su ne) waxanda aka fitar da su daga gidajensu ba da wani laifi ba, sai don kawai sun ce: “Allah ne Ubangijinmu”. Kuma ba don kariyar Allah ga wasu mutane ta hanyar wasu ba, to da lalle an rusa wuraren bauta (na Nasara da suka qaurace wa ‘yan’uwansu), da coci-coci da wuraren bautar Yahudawa da masallatai (na Musulmi) waxanda ake ambaton sunan Allah da yawa a cikinsu. Kuma tabbas Allah zai taimaki mai taimakon Sa. Lalle Allah Mai qarfi ne, Mabuwayi



Sourate: Suratul Hajji

Verset : 58

وَٱلَّذِينَ هَاجَرُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ثُمَّ قُتِلُوٓاْ أَوۡ مَاتُواْ لَيَرۡزُقَنَّهُمُ ٱللَّهُ رِزۡقًا حَسَنٗاۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ لَهُوَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰزِقِينَ

Waxanda kuwa suka yi hijira saboda Allah sannan aka kashe su ko kuma suka mutu, to lalle Allah tabbas zai arzuta su da kyakkyawan arziki. Kuma lalle Allah tabbas Shi ne Fiyayyen masu arzutawa



Sourate: Suratul Hajji

Verset : 59

لَيُدۡخِلَنَّهُم مُّدۡخَلٗا يَرۡضَوۡنَهُۥۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ لَعَلِيمٌ حَلِيمٞ

Lalle tabbas Zai shigar da su wata mashiga da za su yarda da ita. Kuma lalle Allah tabbas Masani ne, Mai hakuri



Sourate: Suratul Hajji

Verset : 78

وَجَٰهِدُواْ فِي ٱللَّهِ حَقَّ جِهَادِهِۦۚ هُوَ ٱجۡتَبَىٰكُمۡ وَمَا جَعَلَ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلدِّينِ مِنۡ حَرَجٖۚ مِّلَّةَ أَبِيكُمۡ إِبۡرَٰهِيمَۚ هُوَ سَمَّىٰكُمُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ مِن قَبۡلُ وَفِي هَٰذَا لِيَكُونَ ٱلرَّسُولُ شَهِيدًا عَلَيۡكُمۡ وَتَكُونُواْ شُهَدَآءَ عَلَى ٱلنَّاسِۚ فَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَٱعۡتَصِمُواْ بِٱللَّهِ هُوَ مَوۡلَىٰكُمۡۖ فَنِعۡمَ ٱلۡمَوۡلَىٰ وَنِعۡمَ ٱلنَّصِيرُ

Kuma ku yi jihadi wajen (xaukaka addinin) Allah iyakar iyawarku. Shi ne Ya zave ku, bai kuma sanya muku wani qunci ba cikin addini. Addinin Babanku ne Ibrahimu. (Allah) Shi ne Ya kira ku Musulmi tuntuni, da kuma cikin wannan (Alqur’ani) don Manzo ya zama shaida a gare ku, ku kuma ku zama shaida ga (sauran) mutane. To sai ku tsai da salla kuma ku ba da zakka, ku kuma yi riqo da (addinin) Allah, Shi ne Majivincin al’amarinku; to madalla da Majivinci, kuma madalla da Mataimaki



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 6

وَمَن جَٰهَدَ فَإِنَّمَا يُجَٰهِدُ لِنَفۡسِهِۦٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَغَنِيٌّ عَنِ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Duk wanda kuwa ya yi jihadi, to yana jihadin ne don kansa. Lalle Allah tabbas Mawadaci ne daga talikai



Sourate: Suratul Ankabut

Verset : 69

وَٱلَّذِينَ جَٰهَدُواْ فِينَا لَنَهۡدِيَنَّهُمۡ سُبُلَنَاۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ لَمَعَ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Waxanda kuma suka yi jihadi saboda Mu to tabbas za Mu shiryar da su hanyoyinmu[1], kuma lalle Allah Yana tare da masu kyautatawa


1- Watau hanyoyin Allah na alheri, su samu dacewa da bin tafarki madaidaici.


Sourate: Suratul Ahzab

Verset : 23

مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ رِجَالٞ صَدَقُواْ مَا عَٰهَدُواْ ٱللَّهَ عَلَيۡهِۖ فَمِنۡهُم مَّن قَضَىٰ نَحۡبَهُۥ وَمِنۡهُم مَّن يَنتَظِرُۖ وَمَا بَدَّلُواْ تَبۡدِيلٗا

Akwai wasu mazaje daga muminai da suka cika abin da suka yi wa Allah alqawari da shi; akwai daga cikinsu wanda ya haxu da ajalinsa, akwai kuma daga cikinsu wanda yake sauraron (ajalin); kuma ba su yi kowace irin savawa ba (game da alqawarin)



Sourate: Suratu Muhammad

Verset : 4

فَإِذَا لَقِيتُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَضَرۡبَ ٱلرِّقَابِ حَتَّىٰٓ إِذَآ أَثۡخَنتُمُوهُمۡ فَشُدُّواْ ٱلۡوَثَاقَ فَإِمَّا مَنَّۢا بَعۡدُ وَإِمَّا فِدَآءً حَتَّىٰ تَضَعَ ٱلۡحَرۡبُ أَوۡزَارَهَاۚ ذَٰلِكَۖ وَلَوۡ يَشَآءُ ٱللَّهُ لَٱنتَصَرَ مِنۡهُمۡ وَلَٰكِن لِّيَبۡلُوَاْ بَعۡضَكُم بِبَعۡضٖۗ وَٱلَّذِينَ قُتِلُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَلَن يُضِلَّ أَعۡمَٰلَهُمۡ

To idan kuka haxu da waxanda suka kafirta sai ku sare wuyoyinsu har lokacin da kuka yi musu jina-jina, sai ku tsananta xauri[1]; to bayan nan ko dai yafewa su tafi bayan (kun ribace su), ko kuma karvar fansa har sai yaqi ya lafa. Wannan abu haka yake, da kuma Allah Ya ga dama da Ya yi nasara a kansu (ko da ba yaqi), sai dai kuma (Ya yi haka ne) don Ya jarrabi shashinku da shashi. Waxanda kuwa aka kashe su a hanyar Allah, to ba zai tava lalata ayyukansa ba


1- Watau Musulmi su kama su a matsayin ribatattun yaqi.


Sourate: Suratu Muhammad

Verset : 5

سَيَهۡدِيهِمۡ وَيُصۡلِحُ بَالَهُمۡ

Zai shirye su Ya kuma kyautata halinsu



Sourate: Suratu Muhammad

Verset : 6

وَيُدۡخِلُهُمُ ٱلۡجَنَّةَ عَرَّفَهَا لَهُمۡ

Ya kuma shigar da su Aljannar da Ya sanar da ita gare su



Sourate: Suratu Muhammad

Verset : 7

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تَنصُرُواْ ٱللَّهَ يَنصُرۡكُمۡ وَيُثَبِّتۡ أَقۡدَامَكُمۡ

Ya ku waxanda suka yi imani idan kuka taimaki Allah, to zai taimake ku, Ya kuma tabbatar da dugaduganku



Sourate: Suratu Muhammad

Verset : 35

فَلَا تَهِنُواْ وَتَدۡعُوٓاْ إِلَى ٱلسَّلۡمِ وَأَنتُمُ ٱلۡأَعۡلَوۡنَ وَٱللَّهُ مَعَكُمۡ وَلَن يَتِرَكُمۡ أَعۡمَٰلَكُمۡ

To kada ku raunana, kuma kada ku kirawo su zuwa sulhu[1], alhali ku ne a sama, Allah kuwa Yana tare da ku, kuma ba zai tauye muku ayyukanku ba


1- Watau gabanin su kafiran su nuna suna son sulhu.


Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 16

قُل لِّلۡمُخَلَّفِينَ مِنَ ٱلۡأَعۡرَابِ سَتُدۡعَوۡنَ إِلَىٰ قَوۡمٍ أُوْلِي بَأۡسٖ شَدِيدٖ تُقَٰتِلُونَهُمۡ أَوۡ يُسۡلِمُونَۖ فَإِن تُطِيعُواْ يُؤۡتِكُمُ ٱللَّهُ أَجۡرًا حَسَنٗاۖ وَإِن تَتَوَلَّوۡاْ كَمَا تَوَلَّيۡتُم مِّن قَبۡلُ يُعَذِّبۡكُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا

Ka ce da waxanda suka qi fita tare da kai[1] daga mutanen qauye: “Ba da daxewa ba za a kirawo ku zuwa wurin wasu mutane masu tsananin yaqi don ku yaqe su ko su musulunta. To idan kuka bi (wannan umarni), Allah zai ba ku lada kyakkyawa, idan kuwa kuka ba da baya kamar yadda kuka ba da baya a da can, zai azabtar da ku azaba mai raxaxi.”


1- Watau zuwa Makka.


Sourate: Suratul Hujurat

Verset : 15

إِنَّمَا ٱلۡمُؤۡمِنُونَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ ثُمَّ لَمۡ يَرۡتَابُواْ وَجَٰهَدُواْ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلصَّـٰدِقُونَ

Muminai kawai su ne waxanda suka yi imani da Allah da Manzonsa, sannan ba su yi kokwanto ba, suka kuma yi yaqi da dukiyoyinsu da rayukansu a hanyar Allah, Waxannan su ne masu gaskiya



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 10

وَمَا لَكُمۡ أَلَّا تُنفِقُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلِلَّهِ مِيرَٰثُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَا يَسۡتَوِي مِنكُم مَّنۡ أَنفَقَ مِن قَبۡلِ ٱلۡفَتۡحِ وَقَٰتَلَۚ أُوْلَـٰٓئِكَ أَعۡظَمُ دَرَجَةٗ مِّنَ ٱلَّذِينَ أَنفَقُواْ مِنۢ بَعۡدُ وَقَٰتَلُواْۚ وَكُلّٗا وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلۡحُسۡنَىٰۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٞ

Kuma me ya same ku ne da ba za ku ciyar saboda Allah ba, alhali kuwa gadon sammai da qasa na Allah ne? Wanda ya ciyar daga cikinku tun kafin buxe (Makka)[1] ya kuma yi yaqi, ba zai zama daidai (da wanda bai yi) ba. Waxannan su suka fi girman daraja a kan waxanda suka ciyar daga bisani, suka kuma yi yaqi. Amma kuma kowannensu Allah Ya yi masa alqawarin Aljanna. Allah kuma Masanin abin da kuke aikatawa ne


1- Wasu daga cikin malamai sun fassara Fat’hu a wannan ayar da cewa ana nufin Sulhul Hudaibiyya.


Sourate: Suratul Hadid

Verset : 25

لَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا رُسُلَنَا بِٱلۡبَيِّنَٰتِ وَأَنزَلۡنَا مَعَهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمِيزَانَ لِيَقُومَ ٱلنَّاسُ بِٱلۡقِسۡطِۖ وَأَنزَلۡنَا ٱلۡحَدِيدَ فِيهِ بَأۡسٞ شَدِيدٞ وَمَنَٰفِعُ لِلنَّاسِ وَلِيَعۡلَمَ ٱللَّهُ مَن يَنصُرُهُۥ وَرُسُلَهُۥ بِٱلۡغَيۡبِۚ إِنَّ ٱللَّهَ قَوِيٌّ عَزِيزٞ

Haqiqa Mun aiko manzanninmu da (ayoyi) mabayyana, Muka kuma saukar da littafi da ma’auni a tare da su (manzannin) don mutane su tsaya da adalci; Muka kuma saukar da baqin qarfe wanda a tare da shi akwai tsananin qarfi da kuma amfani ga mutane, don kuma Allah Ya bayyanar da wanda yake taimakon Sa da manzanninsa a voye. Lalle Allah Mai qarfi ne, Mabuwayi



Sourate: Suratul Hashr

Verset : 2

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَخۡرَجَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ مِن دِيَٰرِهِمۡ لِأَوَّلِ ٱلۡحَشۡرِۚ مَا ظَنَنتُمۡ أَن يَخۡرُجُواْۖ وَظَنُّوٓاْ أَنَّهُم مَّانِعَتُهُمۡ حُصُونُهُم مِّنَ ٱللَّهِ فَأَتَىٰهُمُ ٱللَّهُ مِنۡ حَيۡثُ لَمۡ يَحۡتَسِبُواْۖ وَقَذَفَ فِي قُلُوبِهِمُ ٱلرُّعۡبَۚ يُخۡرِبُونَ بُيُوتَهُم بِأَيۡدِيهِمۡ وَأَيۡدِي ٱلۡمُؤۡمِنِينَ فَٱعۡتَبِرُواْ يَـٰٓأُوْلِي ٱلۡأَبۡصَٰرِ

Shi ne wanda Ya fitar da waxanda suka kafirce daga ma’abota littafi[1] daga gidajensu a fitarwa ta farko. Ba ku yi tsammanin cewa za su fita ba, su kuma sun zaci ganuwoyinsu za su kare su daga Allah, sai Allah Ya zo musu ta inda ba su yi tsammani ba; Ya kuma jefa tsoro a cikin zukatansu. Suka riqa rushe gidajensu da hannayensu da kuma hannayen muminai, to sai ku luru da kyau ya ku ma’abota basira


1- Su ne Yahudawan Banun Nadhir waxanda Annabi () ya kore su daga Madina bayan sun yi yunqurin kashe shi.


Sourate: Suratul Hashr

Verset : 3

وَلَوۡلَآ أَن كَتَبَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمُ ٱلۡجَلَآءَ لَعَذَّبَهُمۡ فِي ٱلدُّنۡيَاۖ وَلَهُمۡ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ عَذَابُ ٱلنَّارِ

Ba don Allah Ya qaddara musu ficewa ba, lalle da Ya azabtar da su a duniya, a lahira kuma suna da azabar wuta



Sourate: Suratul Hashr

Verset : 4

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ شَآقُّواْ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥۖ وَمَن يُشَآقِّ ٱللَّهَ فَإِنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Wannan kuwa saboda cewa sun sava wa Allah da Manzonsa ne, duk kuwa wanda ya sava wa Allah da Manzonsa, to lalle Allah Mai tsananin uquba ne



Sourate: Suratul Hashr

Verset : 5

مَا قَطَعۡتُم مِّن لِّينَةٍ أَوۡ تَرَكۡتُمُوهَا قَآئِمَةً عَلَىٰٓ أُصُولِهَا فَبِإِذۡنِ ٱللَّهِ وَلِيُخۡزِيَ ٱلۡفَٰسِقِينَ

Duk abin da kuka sare na wata bishiyar dabino ko kuka bar ta a tsaye a kan tushiyoyinta, to da izinin Allah ne, don kuma Ya kunyata fasiqai



Sourate: Suratul Hashr

Verset : 6

وَمَآ أَفَآءَ ٱللَّهُ عَلَىٰ رَسُولِهِۦ مِنۡهُمۡ فَمَآ أَوۡجَفۡتُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ خَيۡلٖ وَلَا رِكَابٖ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يُسَلِّطُ رُسُلَهُۥ عَلَىٰ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Kuma duk abin da Allah Ya bai wa Manzonsa na wata dukiya tasu (don falalarsa), to ba wani hari kuka kai na dawaki ko raquma[1] ba saboda shi, sai dai kuma Allah Shi ne Yake xora manzanninsa a kan wanda Ya ga dama. Allah kuwa Mai iko ne a kan komai


1- Watau ku sami dukiya ba tare da yaqi ba.


Sourate: Suratul Hashr

Verset : 7

مَّآ أَفَآءَ ٱللَّهُ عَلَىٰ رَسُولِهِۦ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡقُرَىٰ فَلِلَّهِ وَلِلرَّسُولِ وَلِذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِ كَيۡ لَا يَكُونَ دُولَةَۢ بَيۡنَ ٱلۡأَغۡنِيَآءِ مِنكُمۡۚ وَمَآ ءَاتَىٰكُمُ ٱلرَّسُولُ فَخُذُوهُ وَمَا نَهَىٰكُمۡ عَنۡهُ فَٱنتَهُواْۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Abin da Allah ya bai wa Manzonsa na wata dukiya daga mutanen alqaryu, to na Allah ne da Manzonsa da kuma danginsa na kusa[1] da marayu da miskinai da matafiyin (da guzuri ya yanke wa), don kada ya zama mai juyawa tsakanin mawadata daga cikinku. Kuma abin da Manzo ya ba ku sai ku karve shi, abin kuma da ya hana ku sai ku hanu. Ku kuma kiyaye dokokin Allah; lalle Allah Mai tsananin uquba ne


1- Watau Banu Hashim da Banul Muxxalib, waxanda aka haramta musu karvar sadaka ko zakka.


Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ عَدُوِّي وَعَدُوَّكُمۡ أَوۡلِيَآءَ تُلۡقُونَ إِلَيۡهِم بِٱلۡمَوَدَّةِ وَقَدۡ كَفَرُواْ بِمَا جَآءَكُم مِّنَ ٱلۡحَقِّ يُخۡرِجُونَ ٱلرَّسُولَ وَإِيَّاكُمۡ أَن تُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ رَبِّكُمۡ إِن كُنتُمۡ خَرَجۡتُمۡ جِهَٰدٗا فِي سَبِيلِي وَٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِيۚ تُسِرُّونَ إِلَيۡهِم بِٱلۡمَوَدَّةِ وَأَنَا۠ أَعۡلَمُ بِمَآ أَخۡفَيۡتُمۡ وَمَآ أَعۡلَنتُمۡۚ وَمَن يَفۡعَلۡهُ مِنكُمۡ فَقَدۡ ضَلَّ سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi maqiyana kuma maqiyanku masoya, kuna nuna musu soyayya, alhali kuwa sun kafirce wa abin da ya zo muku na gaskiya, suna fitar da Manzo har da ku kanku don kun yi imani da Allah Ubangijinku, idan har kun zamanto kun fito don yin jihadi saboda Ni da kuma neman yardata. Kuna voye qaunarku gare su, alhali kuwa Ina sane da abin da kuka voye da kuma abin da kuka bayyana. Duk kuwa wanda ya aikata haka daga cikinku, to haqiqa ya vace wa hanya madaidaiciya



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 2

إِن يَثۡقَفُوكُمۡ يَكُونُواْ لَكُمۡ أَعۡدَآءٗ وَيَبۡسُطُوٓاْ إِلَيۡكُمۡ أَيۡدِيَهُمۡ وَأَلۡسِنَتَهُم بِٱلسُّوٓءِ وَوَدُّواْ لَوۡ تَكۡفُرُونَ

Idan suka samu nasara a kanku za su zama abokan gabanku, kuma za su miqa hannayensu da harsunansu zuwa gare ku don munanawa, sun kuma yi burin ina ma da za ku kafirta



Sourate: Suratus Saff 

Verset : 4

إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلَّذِينَ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِهِۦ صَفّٗا كَأَنَّهُم بُنۡيَٰنٞ مَّرۡصُوصٞ

Lalle Allah Yana son waxanda suke yin yaqi dominsa sahu-sahu kai ka ce su gini ne wanda yake xamfare da juna