Sourate: Suratu Ibrahim

Verset : 48

يَوۡمَ تُبَدَّلُ ٱلۡأَرۡضُ غَيۡرَ ٱلۡأَرۡضِ وَٱلسَّمَٰوَٰتُۖ وَبَرَزُواْ لِلَّهِ ٱلۡوَٰحِدِ ٱلۡقَهَّارِ

(Ka tuna) ranar da za a sake qasa ba (wannan) qasar ba, da kuma sammai (ba waxannan samman ba. Halittu) kuma suka fito (daga cikin qasa) a gaban Allah Makaxaici, Mai rinjaye



Sourate: Suratul Kahf 

Verset : 47

وَيَوۡمَ نُسَيِّرُ ٱلۡجِبَالَ وَتَرَى ٱلۡأَرۡضَ بَارِزَةٗ وَحَشَرۡنَٰهُمۡ فَلَمۡ نُغَادِرۡ مِنۡهُمۡ أَحَدٗا

Kuma ka tuna ranar da za Mu tafiyar da duwatsu kuma ka ga qasa a baje (ba tudu ba rafi), Mu kuma tattara su (gaba xaya), ba Mu bar xaya daga cikinsu ba



Sourate: Suratu Maryam

Verset : 40

إِنَّا نَحۡنُ نَرِثُ ٱلۡأَرۡضَ وَمَنۡ عَلَيۡهَا وَإِلَيۡنَا يُرۡجَعُونَ

Lalle Mu ne za Mu gaje qasa da wanda yake bayanta kuma gare Mu ne za a komar da su



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 105

وَيَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلۡجِبَالِ فَقُلۡ يَنسِفُهَا رَبِّي نَسۡفٗا

Suna kuma tambayar ka game da duwatsu, to ka ce (da su): “Ubangijina zai niqe su tilis



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 106

فَيَذَرُهَا قَاعٗا صَفۡصَفٗا

“Sannan Ya bar ta (wato qasar) fili fetal



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 107

لَّا تَرَىٰ فِيهَا عِوَجٗا وَلَآ أَمۡتٗا

“Ba za ka ga wani kwari ko tudu a kanta ba.”



Sourate: Suratul Hajji

Verset : 65

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ سَخَّرَ لَكُم مَّا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَٱلۡفُلۡكَ تَجۡرِي فِي ٱلۡبَحۡرِ بِأَمۡرِهِۦ وَيُمۡسِكُ ٱلسَّمَآءَ أَن تَقَعَ عَلَى ٱلۡأَرۡضِ إِلَّا بِإِذۡنِهِۦٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِٱلنَّاسِ لَرَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Shin ba ka ga cewa Allah Ya hore muku abin da yake cikin qasa, da kuma jiragen ruwa da suke gudu a cikin kogi da umarninsa, kuma Yake riqe sama don kada ta faxo a kan qasa, sai da izininsa? Lalle Allah Mai tausayi ne, Mai rahama ga mutane



Sourate: Suratun Namli

Verset : 88

وَتَرَى ٱلۡجِبَالَ تَحۡسَبُهَا جَامِدَةٗ وَهِيَ تَمُرُّ مَرَّ ٱلسَّحَابِۚ صُنۡعَ ٱللَّهِ ٱلَّذِيٓ أَتۡقَنَ كُلَّ شَيۡءٍۚ إِنَّهُۥ خَبِيرُۢ بِمَا تَفۡعَلُونَ

Kuma za ka ga duwatsu ka zaci a tsaye suke cak, alhali kuwa su suna tafiya ne irin tafiyar gizagizai. Aikin Allah kenan wanda Ya kyautata halittar kowane irin abu. Lalle Shi Masanin abin da kuke aikatawa ne



Sourate: Suratuz Zumar

Verset : 67

وَمَا قَدَرُواْ ٱللَّهَ حَقَّ قَدۡرِهِۦ وَٱلۡأَرۡضُ جَمِيعٗا قَبۡضَتُهُۥ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ وَٱلسَّمَٰوَٰتُ مَطۡوِيَّـٰتُۢ بِيَمِينِهِۦۚ سُبۡحَٰنَهُۥ وَتَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Ba su kuma girmama Allah ba kamar yadda Ya cancanta a girmama Shi, alhali qasa ga baki xayanta tana cikin Damqarsa ranar alqiyama, sammai kuma suna nannaxe a Hannunsa na dama. Tsarki ya tabbata a gare Shi, Ya kuma xaukaka game da abin da suke yin shirka (da shi)



Sourate: Suratuz Zumar

Verset : 68

وَنُفِخَ فِي ٱلصُّورِ فَصَعِقَ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ إِلَّا مَن شَآءَ ٱللَّهُۖ ثُمَّ نُفِخَ فِيهِ أُخۡرَىٰ فَإِذَا هُمۡ قِيَامٞ يَنظُرُونَ

Aka kuma busa qaho, sai duk abin da yake cikin sammai da qasa ya halaka sai wanda Allah Ya ga dama; sannan aka sake yin wata busar, sai ga su a tsaye suna jiran tsammani



Sourate: Suratuz Zumar

Verset : 69

وَأَشۡرَقَتِ ٱلۡأَرۡضُ بِنُورِ رَبِّهَا وَوُضِعَ ٱلۡكِتَٰبُ وَجِاْيٓءَ بِٱلنَّبِيِّـۧنَ وَٱلشُّهَدَآءِ وَقُضِيَ بَيۡنَهُم بِٱلۡحَقِّ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Qasa kuma ta yi haske da hasken Ubangijinta, aka kuma ajiye takardu (na ayyuka), kuma aka zo da annabawa da masu shaida, kuma aka yi hukunci a tsakaninsu da gaskiya, ba kuma za a zalunce su ba



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 44

يَوۡمَ تَشَقَّقُ ٱلۡأَرۡضُ عَنۡهُمۡ سِرَاعٗاۚ ذَٰلِكَ حَشۡرٌ عَلَيۡنَا يَسِيرٞ

A ranar da qasa za ta tsattsage musu (su fito) da gaggawa. Wannan tattarawa ce mai sauqi a gare Mu



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 4

إِذَا رُجَّتِ ٱلۡأَرۡضُ رَجّٗا

Idan aka girgiza qasa girgizawa



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 5

وَبُسَّتِ ٱلۡجِبَالُ بَسّٗا

Aka kuma dandaqe duwatsu dandaqewa



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 6

فَكَانَتۡ هَبَآءٗ مُّنۢبَثّٗا

Suka zama qura abar sheqewa



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 14

وَحُمِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ وَٱلۡجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةٗ وَٰحِدَةٗ

Aka kuma xaga qasa da duwatsu sai aka dandaqe su dandaqewa baki xaya



Sourate: Suratul Muzzammil

Verset : 14

يَوۡمَ تَرۡجُفُ ٱلۡأَرۡضُ وَٱلۡجِبَالُ وَكَانَتِ ٱلۡجِبَالُ كَثِيبٗا مَّهِيلًا

A ranar da qasa da duwatsu za su girgiza, duwatsun kuma su kasance rairayi tilis



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 20

وَسُيِّرَتِ ٱلۡجِبَالُ فَكَانَتۡ سَرَابًا

Aka kuma tafiyar da duwatsu sai suka zama kawalwalniya



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 3

وَإِذَا ٱلۡأَرۡضُ مُدَّتۡ

Kuma idan qasa aka miqe ta



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 4

وَأَلۡقَتۡ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتۡ

Ta kuma jefar da abin da yake cikinta ta wofinta[1]


1- Watau cikinta ya koma fayau babu sauran wani abu.


Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 5

وَأَذِنَتۡ لِرَبِّهَا وَحُقَّتۡ

Ta kuma saurari Ubangijinta kuma ya wajaba (ta saurara)



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 2

وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا

Qasar kuma ta fitar da nauyaye-nauyayenta[1]


1- Watau ta fitar da mutanen da ke cikinta da sauran ma’adanan qarqashinta.


Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 3

وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا

Mutum kuma ya ce: “Me ya same ta?”



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 4

يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا

A wannan ranar ne za ta ba da labaranta[1]


1- Watau ayyukan da aka yi a kanta masu kyau da munana.


Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 5

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا

Don Ubangijinka Ya umarce ta (da yin haka)