Sourate: Suratur Rum

Verset : 49

وَإِن كَانُواْ مِن قَبۡلِ أَن يُنَزَّلَ عَلَيۡهِم مِّن قَبۡلِهِۦ لَمُبۡلِسِينَ

Ko da yake da can kafin a saukar musu shi tabbas sun kasance masu xebe qauna



Sourate: Suratur Rum

Verset : 50

فَٱنظُرۡ إِلَىٰٓ ءَاثَٰرِ رَحۡمَتِ ٱللَّهِ كَيۡفَ يُحۡيِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَآۚ إِنَّ ذَٰلِكَ لَمُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

To sai ka yi duba ga guraben rahamar Allah (ka ga) yadda Yake raya qasa bayan mutuwarta. Lalle wannan tabbas Mai raya matattu ne, kuma Mai iko ne a kan komai



Sourate: Suratu Luqman

Verset : 10

خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ بِغَيۡرِ عَمَدٖ تَرَوۡنَهَاۖ وَأَلۡقَىٰ فِي ٱلۡأَرۡضِ رَوَٰسِيَ أَن تَمِيدَ بِكُمۡ وَبَثَّ فِيهَا مِن كُلِّ دَآبَّةٖۚ وَأَنزَلۡنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجٖ كَرِيمٍ

Ya halicci sammai ba tare da wani ginshiqi da kuke ganin sa ba, Ya kuma kafa manya-manyan duwatsu a cikin qasa don kada ta riqa tangal-tangal da ku, Ya kuma yaxa kowace irin dabba a cikinta. Kuma Mun saukar da ruwa daga sama sai Muka tsirar da kowane irin dangin tsiro mai qayatarwa



Sourate: Suratus Sajda

Verset : 27

أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ أَنَّا نَسُوقُ ٱلۡمَآءَ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ ٱلۡجُرُزِ فَنُخۡرِجُ بِهِۦ زَرۡعٗا تَأۡكُلُ مِنۡهُ أَنۡعَٰمُهُمۡ وَأَنفُسُهُمۡۚ أَفَلَا يُبۡصِرُونَ

Ko kuwa ba sa gani cewa Mu Muke koro ruwa zuwa ga qeqasasshiyar qasa, sai Mu fitar da tsirrai da shi, waxanda dabbobinsu da su kansu suke ci daga gare shi? To me ya sa ba sa lura ne?



Sourate: Suratul Ahzab

Verset : 72

إِنَّا عَرَضۡنَا ٱلۡأَمَانَةَ عَلَى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱلۡجِبَالِ فَأَبَيۡنَ أَن يَحۡمِلۡنَهَا وَأَشۡفَقۡنَ مِنۡهَا وَحَمَلَهَا ٱلۡإِنسَٰنُۖ إِنَّهُۥ كَانَ ظَلُومٗا جَهُولٗا

Lalle Mun bijiro da amana[1] ga sammai da qasa da duwatsu sai suka qi xaukar ta suka ji tsoron ta, sai kuwa mutum ya xauke ta; lalle shi (mutum) ya kasance mai zaluntar kansa ne, mai jahilci


1- Amana a nan, su ne dokokin shari’a na umarni da hani.


Sourate: Suratu Faxir

Verset : 9

وَٱللَّهُ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ ٱلرِّيَٰحَ فَتُثِيرُ سَحَابٗا فَسُقۡنَٰهُ إِلَىٰ بَلَدٖ مَّيِّتٖ فَأَحۡيَيۡنَا بِهِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَاۚ كَذَٰلِكَ ٱلنُّشُورُ

Kuma Allah Shi ne wanda ya aiko da iska sai ta motsa hadari, sai Muka koro shi zuwa ga mataccen gari, sai Muka raya qasa da shi bayan mutuwarta. Kamar haka tayar da (matattu) yake



Sourate: Suratu Faxir

Verset : 27

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ أَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَخۡرَجۡنَا بِهِۦ ثَمَرَٰتٖ مُّخۡتَلِفًا أَلۡوَٰنُهَاۚ وَمِنَ ٱلۡجِبَالِ جُدَدُۢ بِيضٞ وَحُمۡرٞ مُّخۡتَلِفٌ أَلۡوَٰنُهَا وَغَرَابِيبُ سُودٞ

Ba ka ganin lalle Allah Ya saukar da ruwa daga sama sai Muka fitar da ‘ya’yan itace iri daban-daban da shi? Daga duwatsu kuma (Ya samar da) hanyoyi farare da jajaye masu launi daban-daban da kuma wasu baqaqe qirin



Sourate: Suratu Faxir

Verset : 28

وَمِنَ ٱلنَّاسِ وَٱلدَّوَآبِّ وَٱلۡأَنۡعَٰمِ مُخۡتَلِفٌ أَلۡوَٰنُهُۥ كَذَٰلِكَۗ إِنَّمَا يَخۡشَى ٱللَّهَ مِنۡ عِبَادِهِ ٱلۡعُلَمَـٰٓؤُاْۗ إِنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٌ غَفُورٌ

Daga mutane kuma da dabbobi da kuma dabbobin ni’ima su ma launinsu daban-daban ne kamar waxancan. Malamai ne kawai suke tsoron Allah daga bayinsa. Lalle Allah Mabuwayi ne Mai gafara



Sourate: Suratu Faxir

Verset : 41

۞إِنَّ ٱللَّهَ يُمۡسِكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ أَن تَزُولَاۚ وَلَئِن زَالَتَآ إِنۡ أَمۡسَكَهُمَا مِنۡ أَحَدٖ مِّنۢ بَعۡدِهِۦٓۚ إِنَّهُۥ كَانَ حَلِيمًا غَفُورٗا

Lalle Allah ne Yake riqe da sammai da qasa don kada su ruguje. Lallai kuwa idan da za su ruguje, to ba wani mai riqe su in ba Shi ba. Lalle Shi (Allah) Ya kasance Mai haquri ne, Mai gafara



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 33

وَءَايَةٞ لَّهُمُ ٱلۡأَرۡضُ ٱلۡمَيۡتَةُ أَحۡيَيۡنَٰهَا وَأَخۡرَجۡنَا مِنۡهَا حَبّٗا فَمِنۡهُ يَأۡكُلُونَ

Kuma wata aya ce a gare su (ganin) matacciyar qasar da Muka raya ta Muka fitar da qwaya daga gare ta, wadda kuma ita ce suke ci



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 34

وَجَعَلۡنَا فِيهَا جَنَّـٰتٖ مِّن نَّخِيلٖ وَأَعۡنَٰبٖ وَفَجَّرۡنَا فِيهَا مِنَ ٱلۡعُيُونِ

Muka kuma sanya gonaki na dabinai da na inabai a cikinta (qasar), Muka kuma vuvvugo da idanuwan ruwa daga gare ta



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 35

لِيَأۡكُلُواْ مِن ثَمَرِهِۦ وَمَا عَمِلَتۡهُ أَيۡدِيهِمۡۚ أَفَلَا يَشۡكُرُونَ

Don su ci daga ‘ya’yan (itacenta) da kuma abin da hannanyensu suka aikata. Me ya sa ba za su riqa godiya ba?



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 36

سُبۡحَٰنَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡأَزۡوَٰجَ كُلَّهَا مِمَّا تُنۢبِتُ ٱلۡأَرۡضُ وَمِنۡ أَنفُسِهِمۡ وَمِمَّا لَا يَعۡلَمُونَ

Tsarki ya tabbata ga wanda Ya halicci dangogin komai na maza da mata daga abin da qasa take tsirowa, kuma daga su kansu, da ma daga abin da ba su sani ba



Sourate: Suratuz Zumar

Verset : 21

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ أَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَسَلَكَهُۥ يَنَٰبِيعَ فِي ٱلۡأَرۡضِ ثُمَّ يُخۡرِجُ بِهِۦ زَرۡعٗا مُّخۡتَلِفًا أَلۡوَٰنُهُۥ ثُمَّ يَهِيجُ فَتَرَىٰهُ مُصۡفَرّٗا ثُمَّ يَجۡعَلُهُۥ حُطَٰمًاۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَذِكۡرَىٰ لِأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Yanzu ba ka gani cewa Allah ne Ya saukar da ruwa daga sama, sannan Ya shigar da shi cikin idanuwan ruwa a qasa, sannan Yana fitar da shukoki masu launi iri-iri da shi, sannan ya bushe sai ka gan shi fatsi-fatsi, sannan Ya mayar da shi dudduga? Lalle a game da wannan tabbas akwai wa’azi ga ma’abota hankula



Sourate: Suratu Ghafir

Verset : 64

ٱللَّهُ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ قَرَارٗا وَٱلسَّمَآءَ بِنَآءٗ وَصَوَّرَكُمۡ فَأَحۡسَنَ صُوَرَكُمۡ وَرَزَقَكُم مِّنَ ٱلطَّيِّبَٰتِۚ ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبُّكُمۡۖ فَتَبَارَكَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Allah ne wanda Ya sanya muku qasa ta zama wurin zama, sama kuma ta zama rufi, Ya kuma suranta ku, sai Ya kyautata surorinku, Ya kuma arzuta ku da daxaxan abubuwa. Wannan fa Shi ne Allah Ubangijinku. To Allah Ubangijin talikai albarkatunsa sun yawaita



Sourate: Suratu Fussilat

Verset : 39

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦٓ أَنَّكَ تَرَى ٱلۡأَرۡضَ خَٰشِعَةٗ فَإِذَآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡهَا ٱلۡمَآءَ ٱهۡتَزَّتۡ وَرَبَتۡۚ إِنَّ ٱلَّذِيٓ أَحۡيَاهَا لَمُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰٓۚ إِنَّهُۥ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Yana kuma daga ayoyinsa cewa lalle za ka ga qasa a qeqashe, to idan Mun saukar mata da ruwa sai ta girgiza ta kumbura (ta fitar da tsirrai). Lalle wanda Ya raya ta Shi ne Mai raya matattu. Lalle Shi Mai iko ne a kan komai



Sourate: Suratus Shura

Verset : 29

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦ خَلۡقُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَثَّ فِيهِمَا مِن دَآبَّةٖۚ وَهُوَ عَلَىٰ جَمۡعِهِمۡ إِذَا يَشَآءُ قَدِيرٞ

Yana kuma daga cikin ayoyinsa halittar sammai da qasa da kuma dabbobin da Ya yaxa a cikinsu. Kuma shi Mai iko ne a kan Ya tara su idan Ya ga dama



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 10

ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ مَهۡدٗا وَجَعَلَ لَكُمۡ فِيهَا سُبُلٗا لَّعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ

Wanda Ya sanya muku qasa ta zama shimfixa, Ya kuma sanya muku hanyoyi a cikinta don ku gane (inda za ku dosa)



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 11

وَٱلَّذِي نَزَّلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءَۢ بِقَدَرٖ فَأَنشَرۡنَا بِهِۦ بَلۡدَةٗ مَّيۡتٗاۚ كَذَٰلِكَ تُخۡرَجُونَ

Wanda kuma Ya saukar da ruwa daidai gwargwado daga sama sannan Muka raya mataccen gari da shi. Kamar haka ne za a fito da ku (daga qabarurruka)



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 4

وَفِي خَلۡقِكُمۡ وَمَا يَبُثُّ مِن دَآبَّةٍ ءَايَٰتٞ لِّقَوۡمٖ يُوقِنُونَ

A cikin halittarku ma da abin da Yake bazawa na dabbobi, akwai ayoyi ga mutane masu sakankancewa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 5

وَٱخۡتِلَٰفِ ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ وَمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مِن رِّزۡقٖ فَأَحۡيَا بِهِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَا وَتَصۡرِيفِ ٱلرِّيَٰحِ ءَايَٰتٞ لِّقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Da kuma sassavawar dare da yini da abin da Ya saukar daga sama na arziki, sai Ya raya qasa da shi bayan mutuwarta, da kuma jujjuyawar iska, akwai ayoyi ga mutanen da suke hankalta



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 7

وَٱلۡأَرۡضَ مَدَدۡنَٰهَا وَأَلۡقَيۡنَا فِيهَا رَوَٰسِيَ وَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجِۭ بَهِيجٖ

Qasa kuma Muka shimfixa ta, Muka kuma sanya turaku a cikinta, Muka kuma tsirar da kowane irin nau’in (tsiro) mai qayatarwa a cikinta



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 20

وَفِي ٱلۡأَرۡضِ ءَايَٰتٞ لِّلۡمُوقِنِينَ

A cikin qasa kuma akwai ayoyi ga masu sakankancewa



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 10

وَٱلۡأَرۡضَ وَضَعَهَا لِلۡأَنَامِ

Qasa kuma Ya yi ta saboda talikai



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 11

فِيهَا فَٰكِهَةٞ وَٱلنَّخۡلُ ذَاتُ ٱلۡأَكۡمَامِ

A cikinta akwai abin marmari da dabinai ma’abota kwasfa



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 12

وَٱلۡحَبُّ ذُو ٱلۡعَصۡفِ وَٱلرَّيۡحَانُ

Da qwayoyi ma’abota qaiqayi da kuma ganyaye masu qanshi



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 17

ٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ يُحۡيِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَاۚ قَدۡ بَيَّنَّا لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Ku sani cewa Allah Yana raya qasa bayan mutuwarta[1]. Haqiqa Mun bayyana muku ayoyi don ku hankalta


1- Watau hakanan Alqur’ani yake raya zukata bayan sun qeqashe.


Sourate: Suratul Hadid

Verset : 22

مَآ أَصَابَ مِن مُّصِيبَةٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فِيٓ أَنفُسِكُمۡ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مِّن قَبۡلِ أَن نَّبۡرَأَهَآۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Babu wani abu da ya samu na musiba a bayan qasa, ko kuma ga kawunanku face yana cikin Littafin (Lauhul Mahafuzu) tun kafin Mu halicce ta (watau halittar). Lalle wannan (a wurin Allah) mai sauqi ne



Sourate: Suratul Mulk

Verset : 15

هُوَ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ ذَلُولٗا فَٱمۡشُواْ فِي مَنَاكِبِهَا وَكُلُواْ مِن رِّزۡقِهِۦۖ وَإِلَيۡهِ ٱلنُّشُورُ

Shi ne wanda Ya sanya muku qasa horarriya[1], saboda haka ku yi tafiya a cikin sasanninta kuma ku ci daga arzikinta; makoma kuwa zuwa gare Shi take


1- Watau ta zamanto mai sauqin zama da rayuwa a kanta, ba tare da tana tangal-tangal da su ba.


Sourate: Suratu Nuh

Verset : 19

وَٱللَّهُ جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ بِسَاطٗا

“Kuma Allah Ya sanya muku qasa a shimfixe