Sourate: Suratul Baqara

Verset : 124

۞وَإِذِ ٱبۡتَلَىٰٓ إِبۡرَٰهِـۧمَ رَبُّهُۥ بِكَلِمَٰتٖ فَأَتَمَّهُنَّۖ قَالَ إِنِّي جَاعِلُكَ لِلنَّاسِ إِمَامٗاۖ قَالَ وَمِن ذُرِّيَّتِيۖ قَالَ لَا يَنَالُ عَهۡدِي ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Ubangijin Ibrahimu Ya jarrabe shi da wasu kalmomi, sai ya cika su, sai Ya ce: “Ni zan naxa ka shugaba ga mutane”. Sai (Ibrahimu) ya ce: “Har da kuma zurriyata”; Sai (Allah) Ya ce: “Alqawarina ba zai shafi azzalumai ba.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 125

وَإِذۡ جَعَلۡنَا ٱلۡبَيۡتَ مَثَابَةٗ لِّلنَّاسِ وَأَمۡنٗا وَٱتَّخِذُواْ مِن مَّقَامِ إِبۡرَٰهِـۧمَ مُصَلّٗىۖ وَعَهِدۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِـۧمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ أَن طَهِّرَا بَيۡتِيَ لِلطَّآئِفِينَ وَٱلۡعَٰكِفِينَ وَٱلرُّكَّعِ ٱلسُّجُودِ

Kuma ka tuna lokacin da Muka sanya wannan Xaki ya zama matattara ga mutane da kuma aminci; kuma ku mayar da Maqamu Ibrahim wajen salla; kuma Muka yi umarni ga Ibrahim da Isma’ila da cewa: “Ku tsarkake Xakina don masu xawafi da masu i’itikafi da masu ruku’u da sujjada”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 126

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ رَبِّ ٱجۡعَلۡ هَٰذَا بَلَدًا ءَامِنٗا وَٱرۡزُقۡ أَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلثَّمَرَٰتِ مَنۡ ءَامَنَ مِنۡهُم بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۚ قَالَ وَمَن كَفَرَ فَأُمَتِّعُهُۥ قَلِيلٗا ثُمَّ أَضۡطَرُّهُۥٓ إِلَىٰ عَذَابِ ٱلنَّارِۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu ya ce: “Ya Ubangijina, Ka sanya wannan (wuri) ya zama gari mai aminci, kuma Ka arzuta mutanensa da kayan marmari, (amma) wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira daga cikinsu”. Sai (Allah) Ya ce: “Har ma wanda ya kafirta, zan jiyar da shi daxi kaxan, sannan in tilasa masa shiga azabar wuta, tir da wannan makoma.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 127

وَإِذۡ يَرۡفَعُ إِبۡرَٰهِـۧمُ ٱلۡقَوَاعِدَ مِنَ ٱلۡبَيۡتِ وَإِسۡمَٰعِيلُ رَبَّنَا تَقَبَّلۡ مِنَّآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu yake xaga harsashen ginin Xakin Ka’aba tare da Isma’ila, suna cewa: “Ya Ubangijinmu Ka karva mana; lalle Kai Mai ji ne Mai gani.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 128

رَبَّنَا وَٱجۡعَلۡنَا مُسۡلِمَيۡنِ لَكَ وَمِن ذُرِّيَّتِنَآ أُمَّةٗ مُّسۡلِمَةٗ لَّكَ وَأَرِنَا مَنَاسِكَنَا وَتُبۡ عَلَيۡنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka sanya mu masu miqa wuya gare Ka, kuma a cikin zurriyarmu ma (Ka samar) da wata al’umma mai miqa wuya gare Ka, kuma Ka nuna mana ayyaukan ibadarmu, kuma Ka karvi tubanmu, lalle Kai Mai yawan karvar tuba ne Mai jin qai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 129

رَبَّنَا وَٱبۡعَثۡ فِيهِمۡ رَسُولٗا مِّنۡهُمۡ يَتۡلُواْ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتِكَ وَيُعَلِّمُهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَيُزَكِّيهِمۡۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka aiko da wani manzo daga cikinsu, da zai riqa karanta musu ayoyinka, kuma yana koyar da su Littafi da hikima, kuma ya riqa yi musu tarbiyya. Lalle kai Mabuwayi ne, Mai hikima.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 130

وَمَن يَرۡغَبُ عَن مِّلَّةِ إِبۡرَٰهِـۧمَ إِلَّا مَن سَفِهَ نَفۡسَهُۥۚ وَلَقَدِ ٱصۡطَفَيۡنَٰهُ فِي ٱلدُّنۡيَاۖ وَإِنَّهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ لَمِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Babu kuma wanda zai qi addinin Ibrahimu sai wanda bai san ciwon kansa ba. Kuma haqiqa Mun zave shi a duniya, kuma shi a lahira yana cikin mutanen qwarai



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 131

إِذۡ قَالَ لَهُۥ رَبُّهُۥٓ أَسۡلِمۡۖ قَالَ أَسۡلَمۡتُ لِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ka tuna lokacin da Ubangijijinsa Ya ce masa: “Ka miqa wuya”, sai ya ce: “Na miqa wuya ga Ubangijin talikai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 132

وَوَصَّىٰ بِهَآ إِبۡرَٰهِـۧمُ بَنِيهِ وَيَعۡقُوبُ يَٰبَنِيَّ إِنَّ ٱللَّهَ ٱصۡطَفَىٰ لَكُمُ ٱلدِّينَ فَلَا تَمُوتُنَّ إِلَّا وَأَنتُم مُّسۡلِمُونَ

Kuma Ibrahimu da Ya’aqubu suka yi wasiyya da wannan ga ‘ya’yansu cewa: “Ya ‘ya’yana, lalle Allah Ya zava muku addini, don haka kada ku mutu face kuna Musulmi.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 258

أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِي حَآجَّ إِبۡرَٰهِـۧمَ فِي رَبِّهِۦٓ أَنۡ ءَاتَىٰهُ ٱللَّهُ ٱلۡمُلۡكَ إِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ رَبِّيَ ٱلَّذِي يُحۡيِۦ وَيُمِيتُ قَالَ أَنَا۠ أُحۡيِۦ وَأُمِيتُۖ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ فَإِنَّ ٱللَّهَ يَأۡتِي بِٱلشَّمۡسِ مِنَ ٱلۡمَشۡرِقِ فَأۡتِ بِهَا مِنَ ٱلۡمَغۡرِبِ فَبُهِتَ ٱلَّذِي كَفَرَۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Shin ba ka ga wanda ya yi jayayya da Ibrahim ba game da lamarin Ubangijinsa, don Allah ya ba shi mulki, yayin da Ibrahimu ya ce: “Ubangijina Shi ne Yake rayawa, kuma Yake kashewa.” Sai ya ce: “Ai ni ma ina rayawa, kuma ina kashewa.” Sai Ibrahim ya ce: “To Allah Yana kawo rana daga gabas, to kai ka kawo ta daga yamma.” Sai wanda ya kafirta ya kixime. Kuma Allah ba Ya shiryar da azzaluman mutane



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 260

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ رَبِّ أَرِنِي كَيۡفَ تُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰۖ قَالَ أَوَلَمۡ تُؤۡمِنۖ قَالَ بَلَىٰ وَلَٰكِن لِّيَطۡمَئِنَّ قَلۡبِيۖ قَالَ فَخُذۡ أَرۡبَعَةٗ مِّنَ ٱلطَّيۡرِ فَصُرۡهُنَّ إِلَيۡكَ ثُمَّ ٱجۡعَلۡ عَلَىٰ كُلِّ جَبَلٖ مِّنۡهُنَّ جُزۡءٗا ثُمَّ ٱدۡعُهُنَّ يَأۡتِينَكَ سَعۡيٗاۚ وَٱعۡلَمۡ أَنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٞ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu ya ce: “Ya Ubangijina, Ka nuna mini yadda Kake rayar da matattu.” Sai ya ce: “Shin ko ba ka yi imani ba ne?” Ya ce: “A’a, (na yi imani), sai dai ina son zuciyata ta qara samun nutsuwa.” Sai Ya ce: “To ka kama tsuntsaye huxu ka tara su wajenka, sannan ka sanya yanka xaya-xaya nasu a kan kowane saman dutse, sannan ka kira su; za su zo maka da gaggawa. Kuma ka sani cewa lalle Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.”



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 65

يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ لِمَ تُحَآجُّونَ فِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَمَآ أُنزِلَتِ ٱلتَّوۡرَىٰةُ وَٱلۡإِنجِيلُ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِهِۦٓۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Ya ku Ma’abota Littafi, don me kuke yin jayayya game da Ibrahimu, alhalin ba a saukar da Attaura da Linjila ba sai bayan shuxewarsa? Yanzu ba za ku hankalta ba?



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 66

هَـٰٓأَنتُمۡ هَـٰٓؤُلَآءِ حَٰجَجۡتُمۡ فِيمَا لَكُم بِهِۦ عِلۡمٞ فَلِمَ تُحَآجُّونَ فِيمَا لَيۡسَ لَكُم بِهِۦ عِلۡمٞۚ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ وَأَنتُمۡ لَا تَعۡلَمُونَ

Ga ku nan ku waxannan kun yi jayayya kan abin da kuke da ilimi a kai, to don me kuma kuke jayayya a kan abin da ba ku da ilimi a kansa? Kuma Allah Yana sane ku ba ku sani ba



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 67

مَا كَانَ إِبۡرَٰهِيمُ يَهُودِيّٗا وَلَا نَصۡرَانِيّٗا وَلَٰكِن كَانَ حَنِيفٗا مُّسۡلِمٗا وَمَا كَانَ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Ibrahimu bai tava zama Bayahude ba, sannan bai tava zama Banasare ba, sai dai ya kasance mai barin varna ne, Musulmi, kuma bai kasance xaya daga cikin mushirikai ba



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 68

إِنَّ أَوۡلَى ٱلنَّاسِ بِإِبۡرَٰهِيمَ لَلَّذِينَ ٱتَّبَعُوهُ وَهَٰذَا ٱلنَّبِيُّ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْۗ وَٱللَّهُ وَلِيُّ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle mafi kusancin mutane da Ibrahimu su ne waxanda suka bi shi, sai kuma wannan Annabin, da kuma waxanda suka yi Imani. Kuma Allah shi ne Majivincin al’amuran muminai



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 125

وَمَنۡ أَحۡسَنُ دِينٗا مِّمَّنۡ أَسۡلَمَ وَجۡهَهُۥ لِلَّهِ وَهُوَ مُحۡسِنٞ وَٱتَّبَعَ مِلَّةَ إِبۡرَٰهِيمَ حَنِيفٗاۗ وَٱتَّخَذَ ٱللَّهُ إِبۡرَٰهِيمَ خَلِيلٗا

Kuma wane ne mafi kyawun addini fiye da wanda ya miqa fuskarsa ga Allah, yana kuma mai kaxaita Allah, sannan ya bi addinin Ibrahimu yana mai karkacewa duk wata varna? Allah kuwa Ya riqi Ibrahimu a matsayin badaxayi



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 163

۞إِنَّآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ كَمَآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ نُوحٖ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ مِنۢ بَعۡدِهِۦۚ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ وَٱلۡأَسۡبَاطِ وَعِيسَىٰ وَأَيُّوبَ وَيُونُسَ وَهَٰرُونَ وَسُلَيۡمَٰنَۚ وَءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ زَبُورٗا

Lalle Mun yi maka wahayi irin wahayin da Muka yi wa Nuhu da kuma annabawan da suka biyo bayansa, kuma Mun yi wahayi ga Ibrahimu da Isma’ila da Ishaqa da Ya’aqubu da kuma jikokin (Ya’aqubu) da Isa da Ayyuba da Yunusa da Haruna da Sulaimanu; kuma Muka bai wa Dawuda littafin Zabura



Sourate: Suratul An’am

Verset : 74

۞وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِيمُ لِأَبِيهِ ءَازَرَ أَتَتَّخِذُ أَصۡنَامًا ءَالِهَةً إِنِّيٓ أَرَىٰكَ وَقَوۡمَكَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Kuma (ka tuna) lokacin da Ibrahimu ya ce da babansa Azaru: “Yanzu ka riqi gumaka a matsayin alloli? Lalle ni ina ganin ka kai da mutanenka, kuna cikin vata mabayyani.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 75

وَكَذَٰلِكَ نُرِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ مَلَكُوتَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَلِيَكُونَ مِنَ ٱلۡمُوقِنِينَ

Kuma kamar haka ne Muke nuna wa Ibrahimu halittun sammai da qasa, domin ya kasance cikin masu sakankancewa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 76

فَلَمَّا جَنَّ عَلَيۡهِ ٱلَّيۡلُ رَءَا كَوۡكَبٗاۖ قَالَ هَٰذَا رَبِّيۖ فَلَمَّآ أَفَلَ قَالَ لَآ أُحِبُّ ٱلۡأٓفِلِينَ

To yayin da dare ya lulluve shi, ya ga tauraro, sai ya ce; “Wannan shi ne ubangijina;”[1] sannan yayin da ya vace, sai ya ce: “Ni fa ba na son abubuwa masu gushewa.”


1- Daga wannan ayar zuwa aya ta 79 Allah () ya koya wa Annabi Ibrahim () hanyar da zai yi wa mutanensa wa’azi cikin hikima da laluma don jan hankalinsu su fahimci abubuwan da suke bauta wa ba ababen bauta ne na gaskiya ba.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 77

فَلَمَّا رَءَا ٱلۡقَمَرَ بَازِغٗا قَالَ هَٰذَا رَبِّيۖ فَلَمَّآ أَفَلَ قَالَ لَئِن لَّمۡ يَهۡدِنِي رَبِّي لَأَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلضَّآلِّينَ

Sa’annan yayin da ya ga wata ya fito, sai ya ce; “Wannan shi ne ubangijina;” sannan yayin da ya gushe, sai ya ce: “Lalle idan Ubangijina bai shiryar da ni ba, haqiqa zan kasance daga cikin mutane vatattu.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 78

فَلَمَّا رَءَا ٱلشَّمۡسَ بَازِغَةٗ قَالَ هَٰذَا رَبِّي هَٰذَآ أَكۡبَرُۖ فَلَمَّآ أَفَلَتۡ قَالَ يَٰقَوۡمِ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تُشۡرِكُونَ

Sannan yayin da ya ga rana ta hudo, sai ya ce: “Wannan shi ne ubangijina, wannan shi ya fi girma;” sannan yayin da ta vace, sai ya ce: “Ya ku mutanena, haqiqa ni ba ruwana da abin da kuke haxa Allah da shi



Sourate: Suratul An’am

Verset : 79

إِنِّي وَجَّهۡتُ وَجۡهِيَ لِلَّذِي فَطَرَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ حَنِيفٗاۖ وَمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

“Lalle ni kam na juyar da fuskata ga Wanda Ya halicci sammai da qasa, ina mai kauce wa varna kuma ni ba na cikin masu yin shirka.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 80

وَحَآجَّهُۥ قَوۡمُهُۥۚ قَالَ أَتُحَـٰٓجُّوٓنِّي فِي ٱللَّهِ وَقَدۡ هَدَىٰنِۚ وَلَآ أَخَافُ مَا تُشۡرِكُونَ بِهِۦٓ إِلَّآ أَن يَشَآءَ رَبِّي شَيۡـٔٗاۚ وَسِعَ رَبِّي كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمًاۚ أَفَلَا تَتَذَكَّرُونَ

Kuma mutanensa sun yi jayayya da shi; (sai) ya ce: “Shin yanzu kwa riqa jayayya da ni game da (kaxaitakar) Allah, alhalin kuwa Ya shiryar da ni? Kuma ba na jin tsoron abin da kuke sanya wa Allah kishiya da shi, sai abin da Ubangijina Ya ga dama. Kuma ilimin Ubangijina ya yalwaci komai. Shin ba za ku wa’azantu ba?



Sourate: Suratul An’am

Verset : 81

وَكَيۡفَ أَخَافُ مَآ أَشۡرَكۡتُمۡ وَلَا تَخَافُونَ أَنَّكُمۡ أَشۡرَكۡتُم بِٱللَّهِ مَا لَمۡ يُنَزِّلۡ بِهِۦ عَلَيۡكُمۡ سُلۡطَٰنٗاۚ فَأَيُّ ٱلۡفَرِيقَيۡنِ أَحَقُّ بِٱلۡأَمۡنِۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

“To ta qaqa kuwa zan ji tsoron abin da kuka tara da (Allah), alhali ku kuma ba kwa jin tsoron kun sanya wa Allah kishiya, abin da kuwa bai saukar muku da wata hujja a kai ba? To wane vangare ne cikin vangarori biyu, ya fi dacewa da samun aminci; in har kun kasance kun sani?



Sourate: Suratul An’am

Verset : 82

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَلَمۡ يَلۡبِسُوٓاْ إِيمَٰنَهُم بِظُلۡمٍ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمُ ٱلۡأَمۡنُ وَهُم مُّهۡتَدُونَ

“Waxanda suka yi imani, kuma ba su garwaya imaninsu da zalunci ba, waxannan su suke da aminci, kuma su ne shiryayyu.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 83

وَتِلۡكَ حُجَّتُنَآ ءَاتَيۡنَٰهَآ إِبۡرَٰهِيمَ عَلَىٰ قَوۡمِهِۦۚ نَرۡفَعُ دَرَجَٰتٖ مَّن نَّشَآءُۗ إِنَّ رَبَّكَ حَكِيمٌ عَلِيمٞ

Kuma waxancan su ne hujjojinmu da Muka ba wa Ibrahimu su a kan mutanensa. Muna xaukaka darajojin waxanda Muka ga dama. Lalle Ubangijinka Mai hikima ne, Mai yawan sani



Sourate: Suratul An’am

Verset : 161

قُلۡ إِنَّنِي هَدَىٰنِي رَبِّيٓ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ دِينٗا قِيَمٗا مِّلَّةَ إِبۡرَٰهِيمَ حَنِيفٗاۚ وَمَا كَانَ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Ka ce: “Lalle ni, Ubangijina Ya shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, shi ne addini miqaqqe, addinin Ibrahimu wanda ya karkace wa varna, kuma bai zama daga masu shirka ba.”



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 114

وَمَا كَانَ ٱسۡتِغۡفَارُ إِبۡرَٰهِيمَ لِأَبِيهِ إِلَّا عَن مَّوۡعِدَةٖ وَعَدَهَآ إِيَّاهُ فَلَمَّا تَبَيَّنَ لَهُۥٓ أَنَّهُۥ عَدُوّٞ لِّلَّهِ تَبَرَّأَ مِنۡهُۚ إِنَّ إِبۡرَٰهِيمَ لَأَوَّـٰهٌ حَلِيمٞ

Neman gafarar Ibrahimu kuwa ga babansa bai kasance ba sai don kawai alqawarin da ya yi masa ne. To lokacin da ya bayyana gare shi cewa shi maqiyin Allah ne sai ya nesanta kansa da shi. Lalle Ibrahimu ya tabbata mai yawan bautar Allah ne, mai haquri



Sourate: Suratu Hud

Verset : 69

وَلَقَدۡ جَآءَتۡ رُسُلُنَآ إِبۡرَٰهِيمَ بِٱلۡبُشۡرَىٰ قَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞۖ فَمَا لَبِثَ أَن جَآءَ بِعِجۡلٍ حَنِيذٖ

Haqiqa kuma mazanninmu sun zo wa Ibrahimu da albishir, suka ce: “Aminci (a gare ku)”, ya ce: “Aminci (a gare ku kuma).” To bai zauna ba sai da ya kawo musu soyayyen xan maraqi