Sourate: Suratu Sad

Verset : 45

وَٱذۡكُرۡ عِبَٰدَنَآ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ أُوْلِي ٱلۡأَيۡدِي وَٱلۡأَبۡصَٰرِ

Ka kuma tuna bayinmu Ibrahimu da Is’haqa da Yaqubu ma’abota qarfi da basira



Sourate: Suratu Sad

Verset : 46

إِنَّآ أَخۡلَصۡنَٰهُم بِخَالِصَةٖ ذِكۡرَى ٱلدَّارِ

Lalle Mun kevance su da wata kevantacciyar xabi’a, (ita ce) tuna lahira



Sourate: Suratu Sad

Verset : 47

وَإِنَّهُمۡ عِندَنَا لَمِنَ ٱلۡمُصۡطَفَيۡنَ ٱلۡأَخۡيَارِ

Kuma lalle su a wurinmu tabbas suna daga cikin zavavvu nagari



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 26

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِيمُ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦٓ إِنَّنِي بَرَآءٞ مِّمَّا تَعۡبُدُونَ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu ya ce da Babansa da mutanensa: “Lalle ni ba ruwana da abin da kuke bautawa



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 27

إِلَّا ٱلَّذِي فَطَرَنِي فَإِنَّهُۥ سَيَهۡدِينِ

“Sai dai wanda Ya halicce ni, to lalle Shi ne Zai shirye ni.”



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 28

وَجَعَلَهَا كَلِمَةَۢ بَاقِيَةٗ فِي عَقِبِهِۦ لَعَلَّهُمۡ يَرۡجِعُونَ

Ya kuma sanya ta (kalmar Tauhidi ta zama) kalma ce mai wanzuwa a cikin zuri’arsa don (mutanen Makka) su komo (kan hanya).”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 24

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ

Shin labarin baqin Ibrahimu masu girma[1] ya zo maka?


1- Su ne mala’iku da Allah ya aiko.


Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 25

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ

Lokacin da suka shiga wurinsa sai suka ce: “Muna maka sallama;” ya ce: “Aminci ya tabbata gare ku, (ku) mutane ne da ba sanannu ba.”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 26

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجۡلٖ سَمِينٖ

Sai ya saxaxa da sauri zuwa ga iyalinsa, sai ya zo da wani xan maraqi mai mai



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 27

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيۡهِمۡ قَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ

Sai ya kusanta shi gare su, ya ce: “Yanzu ba za ku ci ba?”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 28

فَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ

(Da suka qi ci) sai ya tsorata da su, suka ce: “Kada ka tsorata;” suka kuma yi masa albishir da samun yaro mai ilimi[1]


1- Watau Annabi Ishaq ().


Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 29

فَأَقۡبَلَتِ ٱمۡرَأَتُهُۥ فِي صَرَّةٖ فَصَكَّتۡ وَجۡهَهَا وَقَالَتۡ عَجُوزٌ عَقِيمٞ

Sannan sai matarsa ta gabato su cikin wata qara, sai ta mari fuskarta ta ce: “Yanzu tsohuwa bakarara (ita ce za ta haihu?)”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 30

قَالُواْ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ

Suka ce, “Kamar haka Ubangijinki Ya ce, lalle Shi Mai hikima ne, Masani.”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 31

۞قَالَ فَمَا خَطۡبُكُمۡ أَيُّهَا ٱلۡمُرۡسَلُونَ

(Ibrahimu) ya ce: “To me yake tafe da ku, ya ku waxannan manzanni?”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 32

قَالُوٓاْ إِنَّآ أُرۡسِلۡنَآ إِلَىٰ قَوۡمٖ مُّجۡرِمِينَ

Suka ce: “Lalle mu an aiko mu ne zuwa ga wasu mutane masu manyan laifuka[1]


1- Su ne mutanen Annabi Lux () masu neman maza da sha’awa.


Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 33

لِنُرۡسِلَ عَلَيۡهِمۡ حِجَارَةٗ مِّن طِينٖ

“Don mu zuba musu qonannun duwatsu na tavon (wuta)



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 34

مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلۡمُسۡرِفِينَ

“Waxanda aka yi wa alama daga wurin Ubangijinka saboda mavarnata.”



Sourate: Suratun Najm

Verset : 37

وَإِبۡرَٰهِيمَ ٱلَّذِي وَفَّىٰٓ

Da kuma Ibrahimu wanda ya cika alqawari?



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 26

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحٗا وَإِبۡرَٰهِيمَ وَجَعَلۡنَا فِي ذُرِّيَّتِهِمَا ٱلنُّبُوَّةَ وَٱلۡكِتَٰبَۖ فَمِنۡهُم مُّهۡتَدٖۖ وَكَثِيرٞ مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu da Ibrahimu, Muka kuma sanya annabta da littafi cikin zuriyarsu; To daga cikinsu akwai shiryayyu, masu yawa kuwa daga cikinsu fasiqai ne



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 4

قَدۡ كَانَتۡ لَكُمۡ أُسۡوَةٌ حَسَنَةٞ فِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَٱلَّذِينَ مَعَهُۥٓ إِذۡ قَالُواْ لِقَوۡمِهِمۡ إِنَّا بُرَءَـٰٓؤُاْ مِنكُمۡ وَمِمَّا تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ كَفَرۡنَا بِكُمۡ وَبَدَا بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكُمُ ٱلۡعَدَٰوَةُ وَٱلۡبَغۡضَآءُ أَبَدًا حَتَّىٰ تُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ وَحۡدَهُۥٓ إِلَّا قَوۡلَ إِبۡرَٰهِيمَ لِأَبِيهِ لَأَسۡتَغۡفِرَنَّ لَكَ وَمَآ أَمۡلِكُ لَكَ مِنَ ٱللَّهِ مِن شَيۡءٖۖ رَّبَّنَا عَلَيۡكَ تَوَكَّلۡنَا وَإِلَيۡكَ أَنَبۡنَا وَإِلَيۡكَ ٱلۡمَصِيرُ

Haqiqa kyakkyawan abin koyi ya kasance a gare ku game da Ibrahimu da waxanda suke tare da shi, lokacin da suka ce da mutanensu: “Lalle mu ba ruwanmu da ku, har ma da abin da kuke bauta wa ba Allah ba, mun kafirce muku, kuma gaba da qiyayya sun bayyana a tsakaninmu da ku har abada, har sai kun yi imani da Allah Shi kaxai, in ban da faxar Ibrahimu ga babansa cewa: ‘Lalle zan nema maka gafara, ba na kuma amfana maka komai game da (sakamakon) Allah’; ya Ubangijinmu gare Ka muka dogara, kuma zuwa wurinka muka mayar da lamuranmu, kuma makoma zuwa gare Ka ne



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 5

رَبَّنَا لَا تَجۡعَلۡنَا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ وَٱغۡفِرۡ لَنَا رَبَّنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Ya Ubangijinmu, kada Ka sanya mu fitina ga waxanda suka kafirta, Ka kuma gafarta mana ya Ubangijinmu; lalle Kai ne Mabuwayi, Mai hikima.”



Sourate: Suratul Mumtahana

Verset : 6

لَقَدۡ كَانَ لَكُمۡ فِيهِمۡ أُسۡوَةٌ حَسَنَةٞ لِّمَن كَانَ يَرۡجُواْ ٱللَّهَ وَٱلۡيَوۡمَ ٱلۡأٓخِرَۚ وَمَن يَتَوَلَّ فَإِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡغَنِيُّ ٱلۡحَمِيدُ

Haqiqa abin koyi kyakkyawa ya kasance a gare ku game da su, ga duk wanda ya kasance yana kyakkyawan fatar haxuwa da Allah da ranar lahira. Duk kuma wanda ya ba da baya, to lalle Allah Shi ne Mawadaci, Sha-Yabo



Sourate: Suratul A’ala

Verset : 19

صُحُفِ إِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ

Littattafan Ibrahimu da Musa