Sourate: Suratu Faxir

Verset : 29

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَتۡلُونَ كِتَٰبَ ٱللَّهِ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَأَنفَقُواْ مِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ سِرّٗا وَعَلَانِيَةٗ يَرۡجُونَ تِجَٰرَةٗ لَّن تَبُورَ

Lalle waxanda suke karanta Littafin Allah suka kuma tsai da salla suka kuma ciyar daga abin da Muka arzuta su a voye da sarari, suna burin kasuwancin da ba zai yi tazgaro ba



Sourate: Suratu Faxir

Verset : 30

لِيُوَفِّيَهُمۡ أُجُورَهُمۡ وَيَزِيدَهُم مِّن فَضۡلِهِۦٓۚ إِنَّهُۥ غَفُورٞ شَكُورٞ

Domin Ya cika musu ladansu Ya kuma qara musu daga falalarsa. Lalle Shi Mai gafara ne, Mai godiya



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 7

ءَامِنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَأَنفِقُواْ مِمَّا جَعَلَكُم مُّسۡتَخۡلَفِينَ فِيهِۖ فَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنكُمۡ وَأَنفَقُواْ لَهُمۡ أَجۡرٞ كَبِيرٞ

Ku yi imani da Allah da kuma Manzonsa, ku kuma ciyar daga abin da ya sanya ku wakilai a kansa, to waxanda suka yi imani daga cikinku, suka kuma ciyar suna da lada mai girma



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 18

إِنَّ ٱلۡمُصَّدِّقِينَ وَٱلۡمُصَّدِّقَٰتِ وَأَقۡرَضُواْ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗا يُضَٰعَفُ لَهُمۡ وَلَهُمۡ أَجۡرٞ كَرِيمٞ

Lalle masu yin sadaka maza da masu yin sadaka mata, suka kuma bai wa Allah kyakkyawan rance, to za a ninninka musu shi, suna kuma da wani ladan mai daraja



Sourate: Suratul Mujadila

Verset : 12

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا نَٰجَيۡتُمُ ٱلرَّسُولَ فَقَدِّمُواْ بَيۡنَ يَدَيۡ نَجۡوَىٰكُمۡ صَدَقَةٗۚ ذَٰلِكَ خَيۡرٞ لَّكُمۡ وَأَطۡهَرُۚ فَإِن لَّمۡ تَجِدُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan za ku gana da Manzo, to sai ku gabatar da wata sadaka kafin ganawar taku. Wannan shi ya fi muku alheri da tsarkaka. Sannan idan ba ku samu ba, to lalle Allah Mai gafara ne, Mai rahama



Sourate: Suratul Mujadila

Verset : 13

ءَأَشۡفَقۡتُمۡ أَن تُقَدِّمُواْ بَيۡنَ يَدَيۡ نَجۡوَىٰكُمۡ صَدَقَٰتٖۚ فَإِذۡ لَمۡ تَفۡعَلُواْ وَتَابَ ٱللَّهُ عَلَيۡكُمۡ فَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَأَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥۚ وَٱللَّهُ خَبِيرُۢ بِمَا تَعۡمَلُونَ

Yanzu kun samu damuwa ne ta gabatar da sadaka kafin ganawarku? To idan ba ku aikata haka ba Allah kuma ya karvi tubarku, to sai ku tsayar da salla, ku ba da zakka, ku kuma bi Allah da Manzonsa. Allah kuma Masanin abin da kuke aikatawa ne



Sourate: Suratul Munafiqun

Verset : 10

وَأَنفِقُواْ مِن مَّا رَزَقۡنَٰكُم مِّن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَ أَحَدَكُمُ ٱلۡمَوۡتُ فَيَقُولَ رَبِّ لَوۡلَآ أَخَّرۡتَنِيٓ إِلَىٰٓ أَجَلٖ قَرِيبٖ فَأَصَّدَّقَ وَأَكُن مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Kuma ku ciyar daga abin da Muka arzuta ku tun kafin mutuwa ta zo wa xayanku sannan ya riqa cewa: “Ya Ubangijina, me ya hana Ka saurara min zuwa wani xan lokaci na kusa sai in ba da gaskiya in kuma zama cikin bayi nagari.”



Sourate: Suratul Insan

Verset : 8

وَيُطۡعِمُونَ ٱلطَّعَامَ عَلَىٰ حُبِّهِۦ مِسۡكِينٗا وَيَتِيمٗا وَأَسِيرًا

Suna kuma ciyar da abinci tare da suna son sa ga miskini da maraya da kuma ribataccen yaqi



Sourate: Suratul Insan

Verset : 9

إِنَّمَا نُطۡعِمُكُمۡ لِوَجۡهِ ٱللَّهِ لَا نُرِيدُ مِنكُمۡ جَزَآءٗ وَلَا شُكُورًا

(Suna cewa): “Mu kawai muna ciyar da ku ne saboda Allah, ba ma nufin sakamako ko godiya daga wurinka



Sourate: Suratul Balad

Verset : 13

فَكُّ رَقَبَةٍ

(Watau) ‘yanta wuyaye (bawa ko baiwa)



Sourate: Suratul Balad

Verset : 14

أَوۡ إِطۡعَٰمٞ فِي يَوۡمٖ ذِي مَسۡغَبَةٖ

Ko kuma ciyarwa a wata rana ta yunwa