Sourate: Suratu Muhammad

Verset : 3

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱتَّبَعُواْ ٱلۡبَٰطِلَ وَأَنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّبَعُواْ ٱلۡحَقَّ مِن رَّبِّهِمۡۚ كَذَٰلِكَ يَضۡرِبُ ٱللَّهُ لِلنَّاسِ أَمۡثَٰلَهُمۡ

Wannan (sakamako) kuwa saboda waxanda suka kafirta sun bi varna, waxanda kuwa suka yi imani sun bi shiriya daga Ubangijinsu. Kamar haka ne Allah Yake buga wa mutane misalansu



Sourate: Suratul Fat’h

Verset : 28

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ رَسُولَهُۥ بِٱلۡهُدَىٰ وَدِينِ ٱلۡحَقِّ لِيُظۡهِرَهُۥ عَلَى ٱلدِّينِ كُلِّهِۦۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ شَهِيدٗا

Shi ne Wanda Ya aiko Manzonsa da shiriya da kuma addini na gaskiya don Ya xora shi a kan kowane addini. Allah kuma Ya isa Mai shaida



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 19

وَجَآءَتۡ سَكۡرَةُ ٱلۡمَوۡتِ بِٱلۡحَقِّۖ ذَٰلِكَ مَا كُنتَ مِنۡهُ تَحِيدُ

Kuma magagin mutuwa ya zo da gaskiya; wannan ne abin da ka kasance kana kakkauce wa



Sourate: Suratun Najm

Verset : 28

وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـٔٗا

Kuma ba su da wani ilimi game da haka; ba abin da suke bi sai zato; shi kuma zato, lalle ba ya wadatar da komai game da gaskiya



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 95

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Lalle wannan (bayani na cikin wannan Surar) shi ne haqiqanin gaskiya



Sourate: Suratus Saff 

Verset : 8

يُرِيدُونَ لِيُطۡفِـُٔواْ نُورَ ٱللَّهِ بِأَفۡوَٰهِهِمۡ وَٱللَّهُ مُتِمُّ نُورِهِۦ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡكَٰفِرُونَ

Suna nufin su dusashe hasken Allah da bakunansu, Allah kuwa Mai cika haskensa ne ko da kafirai sun qi



Sourate: Suratus Saff 

Verset : 9

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ رَسُولَهُۥ بِٱلۡهُدَىٰ وَدِينِ ٱلۡحَقِّ لِيُظۡهِرَهُۥ عَلَى ٱلدِّينِ كُلِّهِۦ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡمُشۡرِكُونَ

Shi ne Wanda Ya aiko Manzonsa da shiriya da kuma addinin gaskiya don Ya xora shi a kan kowane addini, ko da kuwa mushirikai sun qi



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Kuma lalle shi tabbas gaskiya ce ta sakankancewa



Sourate: Suratul Asr

Verset : 3

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡحَقِّ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ

Sai dai waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, suka kuma yi wa juna wasiyya da gaskiya, suka kuma yi wa juna wasiyya da haquri