Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 37

وَتَرَكۡنَا فِيهَآ ءَايَةٗ لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ

Muka kuma bar aya ta wa’azi a cikinta ga waxanda suke tsoron azaba mai raxaxi



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 38

وَفِي مُوسَىٰٓ إِذۡ أَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ

Game da Musa kuma (akwai aya), lokacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir’auna da hujjoji bayyanannu



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 41

وَفِي عَادٍ إِذۡ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلۡعَقِيمَ

Kuma game da Adawa (akwai aya), lokacin da Muka aiko musu da iska marar alhairi



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 43

وَفِي ثَمُودَ إِذۡ قِيلَ لَهُمۡ تَمَتَّعُواْ حَتَّىٰ حِينٖ

Kuma game da Samudawa (akwai aya), lokacin da aka ce da su: “Ku ji daxi zuwa wani xan lokaci[1].”


1- Watau wa’adin kwana uku kacal.


Sourate: Suratul Qamar

Verset : 13

وَحَمَلۡنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلۡوَٰحٖ وَدُسُرٖ

Muka kuma xauke shi a kan (jirgin ruwa) mai alluna da qusoshi



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 14

تَجۡرِي بِأَعۡيُنِنَا جَزَآءٗ لِّمَن كَانَ كُفِرَ

Yana gudu a kan idonmu, don ya zama sakayya ga wanda aka kafirce wa (watau Nuhu)



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 15

وَلَقَد تَّرَكۡنَٰهَآ ءَايَةٗ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun bar (abin da ya faru) ya zama aya, to ko akwai mai wa’azantuwa?