To lokacin da gaskiya ta zo musu daga wajenmu sai suka ce: “Ina ma da an ba shi irin abin da aka bai wa Musa?” Yanzu ashe tun da can ba su kafirce da abin da aka bai wa Musa ba; suka ce: “Su biyun sihiri ne (wato Alqur’ani da Attaura) da suke taimakon juna?” Suka kuma ce: “Lalle mu mun kafirce da su gaba xaya.”
Ka ce (da su): “To ku zo da wani littafi daga wajen Allah wanda ya fi su nuna hanyar shiriya (wato Alqur’ani da Attaura), zan bi shi idan kun kasance masu gaskiya.”
To idan ba su amsa maka ba, to ka sani cewa ba abin da suke bi sai soye-soyen zukatansu kawai. Ba kuwa wanda ya fi vacewa kamar wanda ya bi son zuciyarsa ba tare da wata shiriya daga Allah ba. Lalle Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai
Haqiqa kuma Mu Mun bai wa Musa Littafi, to kada ka kasance (kai Manzo) cikin kokwanto na saduwa da shi (Musan)[1]. Kuma Mun sanya shi ya zamanto shiriya ga Banu-Isra’ila
1- Watau haxuwar Annabi Muhammad () da Annabi Musa () a daren mi’iraji.
Haqiqa Mun bai wa Musa Littafin (Attaura), sai aka yi savani a cikinsa, kuma ba don Kalma ta gabata daga Ubangijinka ba, tabbas da an yi hukunci a tsakaninsu. Lalle kuma su, tabbas suna cikin shakka mai sa kokwanto a game da shi
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 36
أَمۡ لَمۡ يُنَبَّأۡ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ
Ko ba a ba shi labarin abin da yake cikin takardun Musa ba ne?
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 37
وَإِبۡرَٰهِيمَ ٱلَّذِي وَفَّىٰٓ
Da kuma Ibrahimu wanda ya cika alqawari?
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 38
أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٞ وِزۡرَ أُخۡرَىٰ
Cewa: “Wani rai ba ya xaukar nauyin laifin wani
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 39
وَأَن لَّيۡسَ لِلۡإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ
“Kuma mutum bai mallaki wani sakamako ba sai na abin da ya aikata
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 40
وَأَنَّ سَعۡيَهُۥ سَوۡفَ يُرَىٰ
“Kuma lalle aikin nasa ba da daxewa ba za a gan shi
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 41
ثُمَّ يُجۡزَىٰهُ ٱلۡجَزَآءَ ٱلۡأَوۡفَىٰ
“Sannan a saka masa da cikakken sakamako
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 42
وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلۡمُنتَهَىٰ
“Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makoma
Signaler l'erreur
Copier
Terminé
Erreur
Partager :
Sourate:
Suratun Najm
Verset : 43
وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضۡحَكَ وَأَبۡكَىٰ
“Kuma lalle Shi ne Ya sa a yi dariya, kuma Ya sa a yi kuka
Haqiqa Mun aiko manzanninmu da (ayoyi) mabayyana, Muka kuma saukar da littafi da ma’auni a tare da su (manzannin) don mutane su tsaya da adalci; Muka kuma saukar da baqin qarfe wanda a tare da shi akwai tsananin qarfi da kuma amfani ga mutane, don kuma Allah Ya bayyanar da wanda yake taimakon Sa da manzanninsa a voye. Lalle Allah Mai qarfi ne, Mabuwayi
Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu da Ibrahimu, Muka kuma sanya annabta da littafi cikin zuriyarsu; To daga cikinsu akwai shiryayyu, masu yawa kuwa daga cikinsu fasiqai ne