Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 181

لَّقَدۡ سَمِعَ ٱللَّهُ قَوۡلَ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ فَقِيرٞ وَنَحۡنُ أَغۡنِيَآءُۘ سَنَكۡتُبُ مَا قَالُواْ وَقَتۡلَهُمُ ٱلۡأَنۢبِيَآءَ بِغَيۡرِ حَقّٖ وَنَقُولُ ذُوقُواْ عَذَابَ ٱلۡحَرِيقِ

Tabbas haqiqa Allah ya ji maganar waxannan da suka ce: “Lalle Allah mataulaci ne, mu ne mawadata.” Da sannu za Mu rubuta abin da suka faxa, da kuma kisan da suka riqa yi wa annabawa ba tare da wani haqqi ba, kuma za Mu ce: “Ku xanxani azaba mai quna



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 81

وَيَقُولُونَ طَاعَةٞ فَإِذَا بَرَزُواْ مِنۡ عِندِكَ بَيَّتَ طَآئِفَةٞ مِّنۡهُمۡ غَيۡرَ ٱلَّذِي تَقُولُۖ وَٱللَّهُ يَكۡتُبُ مَا يُبَيِّتُونَۖ فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ وَكِيلًا

Kuma sukan ce: “Ai ba mu da wani abu sai biyayya.” To idan suka fita daga wajenka, sai wata qungiya daga cikinsu, su riqa qulla wani abu daban cikin dare, savanin abin da suke faxa; Allah kuwa Yana rubuta duk wani abu da suke qullawa da daddare; to ka kawar da kai daga kansu, kuma ka dogara ga Allah. Allah kuwa Ya isa abin dogaro



Sourate: Suratu Yunus

Verset : 21

وَإِذَآ أَذَقۡنَا ٱلنَّاسَ رَحۡمَةٗ مِّنۢ بَعۡدِ ضَرَّآءَ مَسَّتۡهُمۡ إِذَا لَهُم مَّكۡرٞ فِيٓ ءَايَاتِنَاۚ قُلِ ٱللَّهُ أَسۡرَعُ مَكۡرًاۚ إِنَّ رُسُلَنَا يَكۡتُبُونَ مَا تَمۡكُرُونَ

Idan kuma Muka xanxana wa mutane daxi bayan wahala ta same su, sai ga su suna qulla makirci ga ayoyinmu. Ka ce: “Allah Ya fi gaggawar (sakayya a kan) makirci.” Lalle manzanninmu suna rubuta abin da kuke qullawa na makirci



Sourate: Suratul Isra’i

Verset : 13

وَكُلَّ إِنسَٰنٍ أَلۡزَمۡنَٰهُ طَـٰٓئِرَهُۥ فِي عُنُقِهِۦۖ وَنُخۡرِجُ لَهُۥ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ كِتَٰبٗا يَلۡقَىٰهُ مَنشُورًا

Kuma kowane mutum Mun xaura masa littafin aikinsa a wuyansa, za kuma Mu fito masa da wani littafi a ranar alqiyama da zai same shi a buxe



Sourate: Suratul Isra’i

Verset : 14

ٱقۡرَأۡ كِتَٰبَكَ كَفَىٰ بِنَفۡسِكَ ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكَ حَسِيبٗا

(A ce da shi): “Karanta littafinka; a yau ka isa ka yi wa kanka hukunci da kanka.”



Sourate: Suratul Isra’i

Verset : 71

يَوۡمَ نَدۡعُواْ كُلَّ أُنَاسِۭ بِإِمَٰمِهِمۡۖ فَمَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَقۡرَءُونَ كِتَٰبَهُمۡ وَلَا يُظۡلَمُونَ فَتِيلٗا

Ranar da za Mu kirawo kowanne (jinsin) mutane da shugabansu, sannan wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na dama to waxannan za su karanta littafinsu, sannan ba za a zalunce su ko da gwargwadon zaren qwallon dabino ne ba



Sourate: Suratul Kahf 

Verset : 49

وَوُضِعَ ٱلۡكِتَٰبُ فَتَرَى ٱلۡمُجۡرِمِينَ مُشۡفِقِينَ مِمَّا فِيهِ وَيَقُولُونَ يَٰوَيۡلَتَنَا مَالِ هَٰذَا ٱلۡكِتَٰبِ لَا يُغَادِرُ صَغِيرَةٗ وَلَا كَبِيرَةً إِلَّآ أَحۡصَىٰهَاۚ وَوَجَدُواْ مَا عَمِلُواْ حَاضِرٗاۗ وَلَا يَظۡلِمُ رَبُّكَ أَحَدٗا

Aka kuma ajiye littafin (ayyukansu), sannan sai ka ga masu laifi suna cike da tsoron abin da yake cikinsa, suna kuma cewa: “Kaiconmu, me ya sami wannan littafin, ba ya barin (aiki) qarami balle babba sai ya qididdige su. Suka kuma sami (duk) abubuwan da suka aikata an zo da su. Ubangijinka kuwa ba zai zalunci kowa ba



Sourate: Suratu Maryam

Verset : 79

كَلَّاۚ سَنَكۡتُبُ مَا يَقُولُ وَنَمُدُّ لَهُۥ مِنَ ٱلۡعَذَابِ مَدّٗا

A’a, ba haka ba ne. Za Mu rubuta abin da yake faxa, za Mu kuma qara masa azaba ninkin-ba-ninkin



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 62

وَلَا نُكَلِّفُ نَفۡسًا إِلَّا وُسۡعَهَاۚ وَلَدَيۡنَا كِتَٰبٞ يَنطِقُ بِٱلۡحَقِّ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Ba Ma kuwa xora wa kowane rai wani abu sai wanda zai iya. Kuma a wurinmu akwai littafi da yake furuci da gaskiya, kuma su ba za a zalunce su ba



Sourate: Suratu Yasin

Verset : 12

إِنَّا نَحۡنُ نُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰ وَنَكۡتُبُ مَا قَدَّمُواْ وَءَاثَٰرَهُمۡۚ وَكُلَّ شَيۡءٍ أَحۡصَيۡنَٰهُ فِيٓ إِمَامٖ مُّبِينٖ

Lalle Mu ne za Mu raya matattu, Muke kuma rubuta irin abubuwan da suka gabatar (a rayuwarsu) da kuma abin da suka bari a bayansu (bayan mutuwa). Kowane abu kuma Mun qididdige shi a cikin Lauhul-Mahafuzu



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 19

وَجَعَلُواْ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ ٱلَّذِينَ هُمۡ عِبَٰدُ ٱلرَّحۡمَٰنِ إِنَٰثًاۚ أَشَهِدُواْ خَلۡقَهُمۡۚ سَتُكۡتَبُ شَهَٰدَتُهُمۡ وَيُسۡـَٔلُونَ

Suka kuma mai da mala’iku waxanda suke bayin (Allah) Arrahmanu ne `ya`ya mata. Shin sun halarci sanda aka halicce su ne? To za a rubuta shaidarsu, za kuma a tambaye su (a lahira)



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 80

أَمۡ يَحۡسَبُونَ أَنَّا لَا نَسۡمَعُ سِرَّهُمۡ وَنَجۡوَىٰهُمۚ بَلَىٰ وَرُسُلُنَا لَدَيۡهِمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko suna tsammanin cewa Mu ba Ma jin asirinsu da ganawarsu ne? Ba haka ba ne, manzanninmu suna tare da su suna rubutawa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 28

وَتَرَىٰ كُلَّ أُمَّةٖ جَاثِيَةٗۚ كُلُّ أُمَّةٖ تُدۡعَىٰٓ إِلَىٰ كِتَٰبِهَا ٱلۡيَوۡمَ تُجۡزَوۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Za kuma ka ga kowace al’umma a durqushe, kowace al’umma ana kiran ta zuwa ga littafinta, a wannan rana ne za a saka muku abin da kuka kasance kuna aikatawa



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 29

هَٰذَا كِتَٰبُنَا يَنطِقُ عَلَيۡكُم بِٱلۡحَقِّۚ إِنَّا كُنَّا نَسۡتَنسِخُ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

(Za a ce da su): “Wannan Littafinmu ne da yake yi muku furuci da gaskiya[1]. Lalle Mu mun kasance Muna rubuta abin da kuka kasance kuna aikatawa[2].”


1- Watau littafin da mala’iku suka rubuta na ayyukansu yana ba da shaida a kansu da tsantsar gaskiya.


2- Domin Allah ne da kansa ya umarci waxannan mala’ikun su riqa rubuta ayyukan mutane a duniya.


Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 19

فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقۡرَءُواْ كِتَٰبِيَهۡ

To duk wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na dama zai ce: “Ku karvi littafina ku karanta



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 25

وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُوتَ كِتَٰبِيَهۡ

Amma kuma wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na hagun sai ya ce: “Kaicona, ina ma da ba a ba ni littafina ba!



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 29

وَكُلَّ شَيۡءٍ أَحۡصَيۡنَٰهُ كِتَٰبٗا

Kuma kowane abu Mun qididdige shi a rubuce



Sourate: Suratut Takwir

Verset : 10

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتۡ

Idan kuma takardun (ayyuka) aka baza su[1]


1- Watau don kowa ya karanta takardarsa da kansa.


Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 7

كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلۡفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٖ

Tabbas, lalle littafin fajirai yana cikin Sijjinu



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 8

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سِجِّينٞ

Me kuma ya sanar da kai me ake ce wa Sijjinu?



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 9

كِتَٰبٞ مَّرۡقُومٞ

Littafi ne rubutacce[1]


1- Watau wanda ya qunshi cikakkun ayyukan fajirai cif-cif ba daxi babu ragi.


Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 18

كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلۡأَبۡرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ

Tabbas! Lalle littafin mutanen kirki haqiqa yana cikin Illiyyuna



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 19

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ

Me ya sanar da kai mene ne Iliyyuna?



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 20

كِتَٰبٞ مَّرۡقُومٞ

Wani littafi ne rubutacce[1]


1- Watau wanda aka tanada domin rubuta kyawawan ayyukan muminai cif-cif.


Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 21

يَشۡهَدُهُ ٱلۡمُقَرَّبُونَ

(Mala’iku) makusanta suke halartar sa



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 7

فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ

To amma duk wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na dama



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 8

فَسَوۡفَ يُحَاسَبُ حِسَابٗا يَسِيرٗا

To za a yi masa hisabi mai sauqi[1]


1- Watau ta hanyar bijiro ayyukansa a dunqule ba tare da binciken qwaqwaf ba.


Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 9

وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ مَسۡرُورٗا

Ya kuma juyo zuwa ga iyalinsa yana farin ciki



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 10

وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهۡرِهِۦ

Amma wanda kuwa aka bai wa littafinsa ta bayan bayansa



Sourate: Suratul Inshiqaq

Verset : 11

فَسَوۡفَ يَدۡعُواْ ثُبُورٗا

To zai yi kiran halaka