Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 3

إِنَّا جَعَلۡنَٰهُ قُرۡءَٰنًا عَرَبِيّٗا لَّعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Lalle Mu Mun sanya shi ya zamo abin karantawa cikin harshen Larabci domin ku hankalta



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 4

وَإِنَّهُۥ فِيٓ أُمِّ ٱلۡكِتَٰبِ لَدَيۡنَا لَعَلِيٌّ حَكِيمٌ

Lalle kuma shi (Alqur’ani) a cikin Littafi Lauhul-Mahafuzu a wurinmu tabbas maxaukaki ne, mai hikima



Sourate: Suratud Dukhan

Verset : 2

وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

Na rantse da Littafi mai bayyanawa (shi ne Alqur’ani)



Sourate: Suratud Dukhan

Verset : 3

إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةٖ مُّبَٰرَكَةٍۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ

Lalle Mu Muka saukar da shi a cikin dare mai albarka[1]. Lalle Mu Mun kasance Masu gargaxi


1- Shi ne daren Lailatul Qadari. Duba Suratul Qadri.


Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 2

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Saukar da Alqur’ani daga Allah ne Mabuwayi, Mai hikima



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 6

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱللَّهِ نَتۡلُوهَا عَلَيۡكَ بِٱلۡحَقِّۖ فَبِأَيِّ حَدِيثِۭ بَعۡدَ ٱللَّهِ وَءَايَٰتِهِۦ يُؤۡمِنُونَ

Waxannan su ne ayoyin Allah da Muke karanta maka su da gaskiya; to da wane zance ne za su yi imani bayan (zancen) Allah da ayoyinsa?



Sourate: Suratul Ahqaf 

Verset : 2

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Saukar da Alqur’ani daga Allah ne Mabuwayi, Mai hikima



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 77

إِنَّهُۥ لَقُرۡءَانٞ كَرِيمٞ

Lalle shi Alqur’ani ne mai girma



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 78

فِي كِتَٰبٖ مَّكۡنُونٖ

A cikin littafi abin kiyayewa (daga wani sauyi).[1]


1- Shi ne Lauhul Mahfuz.


Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 79

لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلۡمُطَهَّرُونَ

Babu mai tava shi sai tsarkakakku



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 80

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Saukakke ne daga Ubangijin talikai



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 9

هُوَ ٱلَّذِي يُنَزِّلُ عَلَىٰ عَبۡدِهِۦٓ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖ لِّيُخۡرِجَكُم مِّنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ بِكُمۡ لَرَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Shi ne Wanda Yake saukar da ayoyi bayyanannu ga Bawansa don Ya fitar da ku daga duffai zuwa haske. Kuma lalle Allah Mai tausayi ne, Mai rahama a gare ku



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 43

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi saukakke ne daga Ubangijin halittu



Sourate: Suratul Insan

Verset : 23

إِنَّا نَحۡنُ نَزَّلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ تَنزِيلٗا

Lalle Mu Muka saukar maka da Alqur’ani daki-daki