Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 39

فَتَوَلَّىٰ بِرُكۡنِهِۦ وَقَالَ سَٰحِرٌ أَوۡ مَجۡنُونٞ

Sai ya ba da baya shi da qarfin rundunarsa, ya kuma ce: “(Musa) mai sihiri ne ko mahaukaci.”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 40

فَأَخَذۡنَٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذۡنَٰهُمۡ فِي ٱلۡيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٞ

Saboda haka Muka kama shi tare da rundunarsa, sai Muka watsa su a cikin kogi, alhali yana mai aikata abin Allah-wadai



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 41

وَلَقَدۡ جَآءَ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ ٱلنُّذُرُ

Kuma haqiqa gargaxi ya zo wa mutanen Fir’auna



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 42

كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذۡنَٰهُمۡ أَخۡذَ عَزِيزٖ مُّقۡتَدِرٍ

Suka qaryata ayoyinmu dukkaninsu, sai Muka kama su irin kamu na Mabuwayi, Mai iko



Sourate: Suratut Tahrim

Verset : 11

وَضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا لِّلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱمۡرَأَتَ فِرۡعَوۡنَ إِذۡ قَالَتۡ رَبِّ ٱبۡنِ لِي عِندَكَ بَيۡتٗا فِي ٱلۡجَنَّةِ وَنَجِّنِي مِن فِرۡعَوۡنَ وَعَمَلِهِۦ وَنَجِّنِي مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Allah kuma Ya ba da wani misali ga waxanda suka yi imani da matar Fir’auna lokacin da ta ce: “Ya Ubangijina, Ka gina min gida a wurinka cikin Aljanna, Ka kuma tserar da ni daga Fir’auna da aikinsa, kuma Ka tserar da ni daga azzaluman mutane.”



Sourate: Suratul Muzzammil

Verset : 15

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَآ إِلَيۡكُمۡ رَسُولٗا شَٰهِدًا عَلَيۡكُمۡ كَمَآ أَرۡسَلۡنَآ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ رَسُولٗا

Lalle Mu Muka aiko muku da Manzo yana mai shaida a kanku kamar yadda Muka aiko wani manzo zuwa ga Fir’auna



Sourate: Suratul Muzzammil

Verset : 16

فَعَصَىٰ فِرۡعَوۡنُ ٱلرَّسُولَ فَأَخَذۡنَٰهُ أَخۡذٗا وَبِيلٗا

Sai Fir’auna ya sava wa Manzon, sai Muka kama shi kamu mai tsanani



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 17

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

(Aka ce da shi): Ka tafi zuwa ga Fir’auna, haqiqa shi ya yi xagawa



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 18

فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ

Sai ka ce: “Shin zai yiwu gare ka kuwa ka tsarkaka?



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 19

وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ

“In kuma shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka, sai ka ji tsoron Sa?



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 20

فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Sai ya nuna masa babbar aya[1]


1- Watau ya nuna masa hannun mai haske kamar fitila da kuma sandarsa mai rikixa ta zama macijiya.


Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 21

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

Sai ya qaryata ya kuma kangare



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 22

ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ

Sannan ya ba da baya yana ta gaggawa



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 23

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

Sai ya tattara (jama’arsa) sai ya yi shela



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 24

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Sai ya ce, “Ni ne ubangijinku mafi girma!”



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 25

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ

Saboda haka Allah Ya kama shi da azabar lahira (watau Jahannama) da ta duniya (watau nutse wa a ruwa)



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 26

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ

Lalle a game da wannan tabbas akwai izina ga wanda yake tsoron (Allah)



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 10

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ

Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 11

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 12

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ

Suka kuma yawaita varna a cikinsu



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 13

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ

Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani