Sourate: Suratul Mujadila

Verset : 6

يَوۡمَ يَبۡعَثُهُمُ ٱللَّهُ جَمِيعٗا فَيُنَبِّئُهُم بِمَا عَمِلُوٓاْۚ أَحۡصَىٰهُ ٱللَّهُ وَنَسُوهُۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

A ranar da Allah zai tashe su gaba xaya, sannan Ya ba su labarin abin da suka aikata. Allah Ya qididdige shi, su kuwa sun manta shi. Allah kuwa Mai ganin kowane abu ne



Sourate: Suratul Mujadila

Verset : 18

يَوۡمَ يَبۡعَثُهُمُ ٱللَّهُ جَمِيعٗا فَيَحۡلِفُونَ لَهُۥ كَمَا يَحۡلِفُونَ لَكُمۡ وَيَحۡسَبُونَ أَنَّهُمۡ عَلَىٰ شَيۡءٍۚ أَلَآ إِنَّهُمۡ هُمُ ٱلۡكَٰذِبُونَ

A ranar da Allah zai tashe su baki xaya sai su rantse Masa kamar yadda suke rantse muku, su kuma riqa tsammanin su sun yi wani abu (mai amfani). Ku saurara, lalle kam su ne maqaryata



Sourate: Suratul Hashr

Verset : 24

هُوَ ٱللَّهُ ٱلۡخَٰلِقُ ٱلۡبَارِئُ ٱلۡمُصَوِّرُۖ لَهُ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰۚ يُسَبِّحُ لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Shi ne Allah Mahalicci, Mai qagawa Mai surantawa[1]; Yana da sunaye mafiya kyau. Duk abin da yake cikin sammai da qasa yana tsarkake Shi; kuma Shi Mabuwayi ne, Mai hikima


1- Watau mai suranta kamannin abin da ya halitta yadda ya ga dama.


Sourate: Suratut Taghabun

Verset : 2

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ فَمِنكُمۡ كَافِرٞ وَمِنكُم مُّؤۡمِنٞۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٌ

Shi ne Wanda Ya halicce ku, don haka daga cikinku akwai kafiri, daga cikinku kuma akwai mumini. Allah kuwa Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Sourate: Suratut Taghabun

Verset : 3

خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّ وَصَوَّرَكُمۡ فَأَحۡسَنَ صُوَرَكُمۡۖ وَإِلَيۡهِ ٱلۡمَصِيرُ

Ya halicci sammai da qasa da gaskiya, kuma Ya suranta ku, sannan Ya kyautata surorinku; zuwa gare Shi ne kuma makomarku take



Sourate: Suratut Taghabun

Verset : 7

زَعَمَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَن لَّن يُبۡعَثُواْۚ قُلۡ بَلَىٰ وَرَبِّي لَتُبۡعَثُنَّ ثُمَّ لَتُنَبَّؤُنَّ بِمَا عَمِلۡتُمۡۚ وَذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Waxanda suka kafirta sun riya cewa ba za a tashe su ba har abada. Ka ce: “A’a, na rantse da Ubangijina tabbas za a tashe ku, sannan kuma tabbas za a ba ku labarin abin da kuka aikata. Wannan kuwa mai sauqi ne a wurin Allah



Sourate: Suratux Xalaq

Verset : 12

ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ وَمِنَ ٱلۡأَرۡضِ مِثۡلَهُنَّۖ يَتَنَزَّلُ ٱلۡأَمۡرُ بَيۡنَهُنَّ لِتَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ وَأَنَّ ٱللَّهَ قَدۡ أَحَاطَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عِلۡمَۢا

Allah ne Wanda Ya halicci sammai bakwai, qasa ma Ya halicci kwatankwacinsu (watau sammai), umarni yana sauka a tsakaninsu, don ku san cewa, Allah Mai iko ne a kan komai, kuma haqiqa Allah iliminsa ya kewaye kowane abu



Sourate: Suratul Mulk

Verset : 2

ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡمَوۡتَ وَٱلۡحَيَوٰةَ لِيَبۡلُوَكُمۡ أَيُّكُمۡ أَحۡسَنُ عَمَلٗاۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفُورُ

Wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa don Ya jarraba ku (Ya bayyana) wane ne a cikinku ya fi kyakkyawan aiki? Shi kuma Mabuwayi ne, Mai gafara



Sourate: Suratul Mulk

Verset : 3

ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ طِبَاقٗاۖ مَّا تَرَىٰ فِي خَلۡقِ ٱلرَّحۡمَٰنِ مِن تَفَٰوُتٖۖ فَٱرۡجِعِ ٱلۡبَصَرَ هَلۡ تَرَىٰ مِن فُطُورٖ

Wanda Ya halicci sammai bakwai hawa-hawa; ba za ka ga wata tangarxa cikin halittar (Allah) Mai rahama ba. Ka maimaita dubanka, shin za ka ga wata tsaga?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 37

أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ

Shin bai kasance wani xigo na maniyyi da ake zuba shi (a mahaifa) ba?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 38

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ

Sannan ya zama gudan jini sannan (Allah) Ya halicce (shi) sai Ya daidaita (shi)?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 39

فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Sannan Ya halicci dangi biyu daga gare shi, namiji da mace?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 40

أَلَيۡسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحۡـِۧيَ ٱلۡمَوۡتَىٰ

Yanzu wannan bai zama Mai iko a kan ya raya matattu ba?



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 27

ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا

Yanzu ku ne halittarku ta fi tsanani ko kuwa sama wadda Shi ne Ya gina ta?



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 28

رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Ya xaukaka rufinta Ya kuma daidaita ta[1]


1- Watau ya zama babu wata varaka ko tsagewa ko wani aibi tare da ita.


Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 29

وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Ya lulluve darenta da duhu Ya kuma fitar da hasken hantsinta



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 30

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Qasa kuma bayan haka Ya shimfixa ta



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 31

أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا

Ya fitar da ruwanta da makiyayarta daga gare ta



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 32

وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا

Duwatsu kuma Ya kafa su



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 33

مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ

Don jin daxinku da na dabbobinku



Sourate: Suratul Infixar

Verset : 7

ٱلَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ

Wanda Ya halicce ka Ya kuma daidaita ka Ya miqar da kai[1]?


1- Watau ya lura da girman ni’imar da ya yi masa yayin da bai yi masa irin halittar jaki ba ko ta biri ko ta kare.


Sourate: Suratul Infixar

Verset : 8

فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ

Ya harhaxa ka cikin irin surar da Ya ga dama?



Sourate: Suratul Buruj

Verset : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



Sourate: Suratux Xariq

Verset : 8

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ

Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi