Sourate: Suratul Qamar

Verset : 55

فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ

A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 46

وَلِمَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

Duk wanda kuwa ya ji tsoron tsayuwa (gaban) Ubangijinsa yana da Aljanna biyu



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 10

وَٱلسَّـٰبِقُونَ ٱلسَّـٰبِقُونَ

Da kuma masu rige-rige (zuwa alheri)



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 11

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡمُقَرَّبُونَ

Waxannan su ne makusanta



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 12

فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

A cikin gidajen Aljanna na ni’ima



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 34

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Lalle masu taqawa suna da gidajen Aljannar ni’ima a wurin Ubangijinsu



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 23

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ

Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ

Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 29

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 31

فَمَنِ ٱبۡتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡعَادُونَ

To duk wanda ya nemi (wani abu) bayan wannan, to waxannan su ne masu qetare iyaka



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 32

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِأَمَٰنَٰتِهِمۡ وَعَهۡدِهِمۡ رَٰعُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye amanoninsu da alqawuransu



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 33

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمۡ قَآئِمُونَ

Waxanda kuma suke tsai da shaidarsu



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 34

وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ يُحَافِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye sallolinsu



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 35

أُوْلَـٰٓئِكَ فِي جَنَّـٰتٖ مُّكۡرَمُونَ

Waxannan su ne waxanda ake girmamawa cikin gidajen Aljanna



Sourate: Suratul Mursalat

Verset : 41

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي ظِلَٰلٖ وَعُيُونٖ

Lalle masu taqawa suna cikin inuwoyi da idanuwan ruwa



Sourate: Suratul Mursalat

Verset : 42

وَفَوَٰكِهَ مِمَّا يَشۡتَهُونَ

Da kuma ababan marmari daga abin da suke sha’awa



Sourate: Suratul Mursalat

Verset : 43

كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ku ci kuma ku sha kuna masu farin ciki saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa



Sourate: Suratul Mursalat

Verset : 44

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 40

وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ

Duk wanda kuma ya ji tsoron tsayuwa gaban Ubangijinsa, ya kuma hana zuciya bin abin da take so



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 22

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٍ

Lalle masu biyayya tabbas suna cikin ni’ima



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 23

عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ

A kan gadaje suna kallo



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 24

تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِهِمۡ نَضۡرَةَ ٱلنَّعِيمِ

Za ka gane hasken ni’ima a fuskokinsu[1]


1- Watau fuskokinsu suna sheqi da annuri.


Sourate: Suratul Buruj

Verset : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa