Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 31

وَمَآءٖ مَّسۡكُوبٖ

Da kuma ruwa mai kwarara



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 32

وَفَٰكِهَةٖ كَثِيرَةٖ

Da ababen marmari masu yawa



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 33

لَّا مَقۡطُوعَةٖ وَلَا مَمۡنُوعَةٖ

Ba masu yankewa ba kuma ba ababen hanawa ba



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 34

وَفُرُشٖ مَّرۡفُوعَةٍ

Da shimfixu masu daraja



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 35

إِنَّآ أَنشَأۡنَٰهُنَّ إِنشَآءٗ

Lalle Mu ne Muka qage su (‘yan matan Aljanna) sabuwar qagowa



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 36

فَجَعَلۡنَٰهُنَّ أَبۡكَارًا

Sannan Muka sanya su budurwai



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 37

عُرُبًا أَتۡرَابٗا

Masu begen mazajensu, tsarekun juna



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 38

لِّأَصۡحَٰبِ ٱلۡيَمِينِ

Don ma’abota hannun dama



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 21

سَابِقُوٓاْ إِلَىٰ مَغۡفِرَةٖ مِّن رَّبِّكُمۡ وَجَنَّةٍ عَرۡضُهَا كَعَرۡضِ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ أُعِدَّتۡ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦۚ ذَٰلِكَ فَضۡلُ ٱللَّهِ يُؤۡتِيهِ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Ku yi rige-rige zuwa neman gafara daga Ubangijinku da Aljanna wadda faxinta kamar faxin sammai da qasa yake, an tanade ta don waxanda suka yi imani da Allah da manzanninsa. Wannan falalar Allah ce da Yake ba da ita ga wanda Ya ga dama. Allah kuwa Ma’abocin falala ne, Mai girma



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 22

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ

Cikin Aljanna maxaukakiya



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 23

قُطُوفُهَا دَانِيَةٞ

‘Ya’yan itatuwanta dab da dab suke



Sourate: Suratul Insan

Verset : 12

وَجَزَىٰهُم بِمَا صَبَرُواْ جَنَّةٗ وَحَرِيرٗا

Ya kuma saka musu da Aljanna da alharini saboda haqurin da suka yi



Sourate: Suratul Insan

Verset : 13

مُّتَّكِـِٔينَ فِيهَا عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِۖ لَا يَرَوۡنَ فِيهَا شَمۡسٗا وَلَا زَمۡهَرِيرٗا

Suna masu kishingixa a cikinta a kan gadaje; ba sa ganin rana ko jin tsananin sanyi a cikinta



Sourate: Suratul Insan

Verset : 14

وَدَانِيَةً عَلَيۡهِمۡ ظِلَٰلُهَا وَذُلِّلَتۡ قُطُوفُهَا تَذۡلِيلٗا

Inuwoyinta kuma suna kusa da su, an kuma hore musu ‘ya’yan itatuwanta matuqar horewa



Sourate: Suratul Insan

Verset : 15

وَيُطَافُ عَلَيۡهِم بِـَٔانِيَةٖ مِّن فِضَّةٖ وَأَكۡوَابٖ كَانَتۡ قَوَارِيرَا۠

Ana kuma kai-kawo a tsakaninsu da qorai na azurfa da kofuna waxanda suka kasance na qarau



Sourate: Suratul Insan

Verset : 16

قَوَارِيرَاْ مِن فِضَّةٖ قَدَّرُوهَا تَقۡدِيرٗا

Qarau xin na azurfa ne, sun auna su, aunawa daidai da buqata



Sourate: Suratul Insan

Verset : 17

وَيُسۡقَوۡنَ فِيهَا كَأۡسٗا كَانَ مِزَاجُهَا زَنجَبِيلًا

Ana kuma shayar da su wata giya a cikinta, wadda mahaxinta ya kasance citta mai yatsu ce



Sourate: Suratul Insan

Verset : 18

عَيۡنٗا فِيهَا تُسَمَّىٰ سَلۡسَبِيلٗا

Wani marmaro ne a cikinta da ake kiran sa Salsabilu



Sourate: Suratul Insan

Verset : 19

۞وَيَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ وِلۡدَٰنٞ مُّخَلَّدُونَ إِذَا رَأَيۡتَهُمۡ حَسِبۡتَهُمۡ لُؤۡلُؤٗا مَّنثُورٗا

Samari hadimai dawwamammu (da ba sa tsufa) kuma suna kai-kawo tsakaninsu, idan ka gan su sai ka yi tsammanin su wani lu’ulu’u ne da aka baza



Sourate: Suratul Insan

Verset : 20

وَإِذَا رَأَيۡتَ ثَمَّ رَأَيۡتَ نَعِيمٗا وَمُلۡكٗا كَبِيرًا

Idan kuma ka yi kallo a can, za ka ga ni’ima da kuma mulki qasaitacce



Sourate: Suratul Insan

Verset : 21

عَٰلِيَهُمۡ ثِيَابُ سُندُسٍ خُضۡرٞ وَإِسۡتَبۡرَقٞۖ وَحُلُّوٓاْ أَسَاوِرَ مِن فِضَّةٖ وَسَقَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ شَرَابٗا طَهُورًا

Suna sanye da korayen tufafin alharini marar kauri da na alharini mai kauri; aka kuma yi musu ado da warawarai na azurfa, Ubangijinsu kuma Ya shayar da su abin sha mai tsarki



Sourate: Suratul Insan

Verset : 22

إِنَّ هَٰذَا كَانَ لَكُمۡ جَزَآءٗ وَكَانَ سَعۡيُكُم مَّشۡكُورًا

Lalle wannan ya kasance sakamako ne a gare ku, kuma aikinku ya kasance abin godewa



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 31

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ مَفَازًا

Lalle masu taqawa suna da babban rabo



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 32

حَدَآئِقَ وَأَعۡنَٰبٗا

(Su ne) gonaki da inabai



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 33

وَكَوَاعِبَ أَتۡرَابٗا

Da ‘yan mata tsaraiku



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 34

وَكَأۡسٗا دِهَاقٗا

Da kofin (giya) cikakke



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 35

لَّا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا كِذَّـٰبٗا

Ba sa jin maganar banza a cikinta ko kuma qarya



Sourate: Suratun Naba’i

Verset : 36

جَزَآءٗ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابٗا

Sakamako ne daga Ubangijinka, kyauta ce a lissafe (gwargwadon aikin kowa)



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 25

يُسۡقَوۡنَ مِن رَّحِيقٖ مَّخۡتُومٍ

Ana shayar da su giyar da aka rufe (bakin mazubinta)



Sourate: Suratul Muxaffifin

Verset : 26

خِتَٰمُهُۥ مِسۡكٞۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلۡيَتَنَافَسِ ٱلۡمُتَنَٰفِسُونَ

(Har) qarshensa (qamshin) almiski ne. To game da wannan kuwa lalle masu gasa su yi gasa