Sourate: Suratus Saffat

Verset : 46

بَيۡضَآءَ لَذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ

Fara fat, ga kuma daxi ga masu sha



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 47

لَا فِيهَا غَوۡلٞ وَلَا هُمۡ عَنۡهَا يُنزَفُونَ

Babu sa ciwon kai a gare ta, kuma ba za a bugar da su da ita ba



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 48

وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ عِينٞ

A wurinsu kuma akwai mataye masu taqaita kallonsu ga mazajensu, masu qwala-qwalan ido



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 49

كَأَنَّهُنَّ بَيۡضٞ مَّكۡنُونٞ

Kai ka ce su wani qwai ne a cikin kwasfa



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 71

يُطَافُ عَلَيۡهِم بِصِحَافٖ مِّن ذَهَبٖ وَأَكۡوَابٖۖ وَفِيهَا مَا تَشۡتَهِيهِ ٱلۡأَنفُسُ وَتَلَذُّ ٱلۡأَعۡيُنُۖ وَأَنتُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Ana zagayawa tsakaninsu da akusa na zinari da kofuna; a cikinta kuma akwai (duk) abin da rayuka suke sha’awa, idanuwa kuma suke jin daxin (ganinsu); ku kuma a cikinta madawwama ne



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 72

وَتِلۡكَ ٱلۡجَنَّةُ ٱلَّتِيٓ أُورِثۡتُمُوهَا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Waccan kuma ita ce Aljannar da aka gadar muku ita saboda abin da kuka kasance kuma aikatawa



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 73

لَكُمۡ فِيهَا فَٰكِهَةٞ كَثِيرَةٞ مِّنۡهَا تَأۡكُلُونَ

A cikinta kuna da `ya`yan itatuwa na marmari masu yawa, daga gare su kuma za ku riqa ci



Sourate: Suratud Dukhan

Verset : 51

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٖ

Lalle masu taqawa suna cikin wani amintaccen wuri



Sourate: Suratud Dukhan

Verset : 52

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

Cikin lambuna da idanuwan ruwa



Sourate: Suratud Dukhan

Verset : 53

يَلۡبَسُونَ مِن سُندُسٖ وَإِسۡتَبۡرَقٖ مُّتَقَٰبِلِينَ

Suna saye da tufafi na alharini mai shara-shara da mai kauri suna fuskantar juna



Sourate: Suratud Dukhan

Verset : 54

كَذَٰلِكَ وَزَوَّجۡنَٰهُم بِحُورٍ عِينٖ

Kamar haka ne, Muka kuma aura musu (‘yan matan) Hurul-Ini



Sourate: Suratud Dukhan

Verset : 55

يَدۡعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَٰكِهَةٍ ءَامِنِينَ

A cikinta (Aljannar) suna kiran a kawo musu duk wani kayan marmari, suna cikin aminci



Sourate: Suratu Muhammad

Verset : 15

مَّثَلُ ٱلۡجَنَّةِ ٱلَّتِي وُعِدَ ٱلۡمُتَّقُونَۖ فِيهَآ أَنۡهَٰرٞ مِّن مَّآءٍ غَيۡرِ ءَاسِنٖ وَأَنۡهَٰرٞ مِّن لَّبَنٖ لَّمۡ يَتَغَيَّرۡ طَعۡمُهُۥ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ خَمۡرٖ لَّذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ عَسَلٖ مُّصَفّٗىۖ وَلَهُمۡ فِيهَا مِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِ وَمَغۡفِرَةٞ مِّن رَّبِّهِمۡۖ كَمَنۡ هُوَ خَٰلِدٞ فِي ٱلنَّارِ وَسُقُواْ مَآءً حَمِيمٗا فَقَطَّعَ أَمۡعَآءَهُمۡ

Kwatankwacin Aljannar da aka yi wa masu taqawa alqawari da ita shi ne, a cikinta akwai qoramu na ruwa ba gurvatacce ba, da kuma qoramu na nono da xanxanonsa bai canja ba, da qoramu na giya masu daxi ga mashaya, da qoramu na tatacciyar zuma, kuma suna da kowane irin nau’i na ‘ya’yan itace da kuma gafara daga Ubangijinsu. Yanzu (masu waxannan sa yi) daidai da waxanda za su dawwama a cikin wuta a kuma shayar da su ruwa tafasasshe, sai ya yayyanke kayan cikinsu?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 46

وَلِمَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

Duk wanda kuwa ya ji tsoron tsayuwa (gaban) Ubangijinsa yana da Aljanna biyu



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 47

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 48

ذَوَاتَآ أَفۡنَانٖ

Ma’abota rassan bishiyoyi



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 49

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 50

فِيهِمَا عَيۡنَانِ تَجۡرِيَانِ

A cikinsu akwai idanuwa (na ruwa) guda biyu masu gudana



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 51

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 52

فِيهِمَا مِن كُلِّ فَٰكِهَةٖ زَوۡجَانِ

A cikinsu akwai (dangi) biyu na kowane abin marmari



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 53

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 54

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشِۭ بَطَآئِنُهَا مِنۡ إِسۡتَبۡرَقٖۚ وَجَنَى ٱلۡجَنَّتَيۡنِ دَانٖ

Suna kishingixe a kan shimfixu da shafin cikinsu na kakkauran alhariri ne. Kuma ‘ya’yan bishiyoyin Aljannatai biyun kusa suke (da kowa)



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 55

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 56

فِيهِنَّ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ لَمۡ يَطۡمِثۡهُنَّ إِنسٞ قَبۡلَهُمۡ وَلَا جَآنّٞ

A cikinsu akwai (mata) masu taqaita kallo (ga mazajensu, waxanda) wani mutum ko aljan bai tava shafar su ba a gabaninsu



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 57

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 58

كَأَنَّهُنَّ ٱلۡيَاقُوتُ وَٱلۡمَرۡجَانُ

Kai ka ce su yaqutu ne da murjani



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 59

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 60

هَلۡ جَزَآءُ ٱلۡإِحۡسَٰنِ إِلَّا ٱلۡإِحۡسَٰنُ

Shin akwai wani sakamako na kyautatawa in ba kyautatawa ba?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 61

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 62

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ

A qasa da su kuma akwai wasu aljannatai guda biyu