Sourate: Suratu Hud

Verset : 43

قَالَ سَـَٔاوِيٓ إِلَىٰ جَبَلٖ يَعۡصِمُنِي مِنَ ٱلۡمَآءِۚ قَالَ لَا عَاصِمَ ٱلۡيَوۡمَ مِنۡ أَمۡرِ ٱللَّهِ إِلَّا مَن رَّحِمَۚ وَحَالَ بَيۡنَهُمَا ٱلۡمَوۡجُ فَكَانَ مِنَ ٱلۡمُغۡرَقِينَ

(Xan) ya ce: “Ai zan fake a wani dutse wanda zai kare ni daga ruwan.” (Annabi Nuhu) ya ce: “Yau kam babu mai kariya daga al’amarin Allah sai dai wanda Ya yi wa rahama kawai.” Sai raqumin ruwa ya shiga tsakaninsu, ya zamanto cikin waxanda aka nutsar (a cikin ruwa)



Sourate: Suratu Hud

Verset : 44

وَقِيلَ يَـٰٓأَرۡضُ ٱبۡلَعِي مَآءَكِ وَيَٰسَمَآءُ أَقۡلِعِي وَغِيضَ ٱلۡمَآءُ وَقُضِيَ ٱلۡأَمۡرُ وَٱسۡتَوَتۡ عَلَى ٱلۡجُودِيِّۖ وَقِيلَ بُعۡدٗا لِّلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Aka ce: “Ke qasa, ki haxiye ruwanki, ke kuma sama ki riqe ruwanki, aka kuwa qafar da ruwan, kuma aka gama al’amarin, (jirgin) kuma ya tsaya a kan (dutsen) Judi; aka kuma ce: Halaka ta tabbata ga mutane azzalumai.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 45

وَنَادَىٰ نُوحٞ رَّبَّهُۥ فَقَالَ رَبِّ إِنَّ ٱبۡنِي مِنۡ أَهۡلِي وَإِنَّ وَعۡدَكَ ٱلۡحَقُّ وَأَنتَ أَحۡكَمُ ٱلۡحَٰكِمِينَ

Nuhu kuma ya kira Ubangijinsa sai ya ce: “Ya Ubangijina, lalle xana yana daga iyalina, lalle kuma alqawarinka gaskiya ne, kuma Kai ne Ka fi masu hukunci iya hukunci.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 46

قَالَ يَٰنُوحُ إِنَّهُۥ لَيۡسَ مِنۡ أَهۡلِكَۖ إِنَّهُۥ عَمَلٌ غَيۡرُ صَٰلِحٖۖ فَلَا تَسۡـَٔلۡنِ مَا لَيۡسَ لَكَ بِهِۦ عِلۡمٌۖ إِنِّيٓ أَعِظُكَ أَن تَكُونَ مِنَ ٱلۡجَٰهِلِينَ

(Allah) Ya ce: Ya Nuhu, lalle shi ba ya daga cikin iyalinka, lalle shi aiki ne marar kyau; to kada ka qara tambaya Ta abin da ba ka da sani a kansa; lalle Ni Ina gargaxin ka da kada ka zamanto cikin jahilai



Sourate: Suratu Hud

Verset : 47

قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَعُوذُ بِكَ أَنۡ أَسۡـَٔلَكَ مَا لَيۡسَ لِي بِهِۦ عِلۡمٞۖ وَإِلَّا تَغۡفِرۡ لِي وَتَرۡحَمۡنِيٓ أَكُن مِّنَ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni ina neman tsarinka a kan in tambaye Ka abin da ba ni da sani a kansa, idan kuwa ba Ka yafe mini ba, Ka kuma ji qai na, to zan zamo cikin asararru.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 48

قِيلَ يَٰنُوحُ ٱهۡبِطۡ بِسَلَٰمٖ مِّنَّا وَبَرَكَٰتٍ عَلَيۡكَ وَعَلَىٰٓ أُمَمٖ مِّمَّن مَّعَكَۚ وَأُمَمٞ سَنُمَتِّعُهُمۡ ثُمَّ يَمَسُّهُم مِّنَّا عَذَابٌ أَلِيمٞ

Aka ce: Ya Nuhu, ka sauka cikin aminci daga gare Mu da albarka a gare ka da kuma ga al’ummun da suke tare da kai. Wasu al’ummun kuma za Mu jiyar da su daxi, sannan kuma azaba mai raxaxi daga gare Mu ta same su



Sourate: Suratu Hud

Verset : 49

تِلۡكَ مِنۡ أَنۢبَآءِ ٱلۡغَيۡبِ نُوحِيهَآ إِلَيۡكَۖ مَا كُنتَ تَعۡلَمُهَآ أَنتَ وَلَا قَوۡمُكَ مِن قَبۡلِ هَٰذَاۖ فَٱصۡبِرۡۖ إِنَّ ٱلۡعَٰقِبَةَ لِلۡمُتَّقِينَ

Waxannan suna daga labaran gaibu da muke yi maka wahayinsu, don kai da mutanenka ba ku san su ba kafin wannan (labarin); sai ka yi haquri; haqiqa kyakkyawan qarshe yana ga masu taqawa



Sourate: Suratul Isra’i

Verset : 3

ذُرِّيَّةَ مَنۡ حَمَلۡنَا مَعَ نُوحٍۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَبۡدٗا شَكُورٗا

(Ya ku) zurriyar waxanda Muka xauko tare da Nuhu (a cikin jirgi). Lalle shi ya zamanto bawa ne mai yawan godiya



Sourate: Suratu Maryam

Verset : 58

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ أَنۡعَمَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ مِن ذُرِّيَّةِ ءَادَمَ وَمِمَّنۡ حَمَلۡنَا مَعَ نُوحٖ وَمِن ذُرِّيَّةِ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡرَـٰٓءِيلَ وَمِمَّنۡ هَدَيۡنَا وَٱجۡتَبَيۡنَآۚ إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُ ٱلرَّحۡمَٰنِ خَرُّواْۤ سُجَّدٗاۤ وَبُكِيّٗا۩

Waxannan su ne annabawa waxanda Allah Ya yi ni’ima a gare su, daga zuriyar Adamu, da kuma waxanda Muka xauko (a jirgin ruwa) tare da Nuhu, daga kuma zuriyar Ibrahimu da Isra’ila (watau Ya’aqubu), da kuma waxanda Muka shiryar da su Muka kuma zave su. Idan ana karanta musu ayoyin (Allah) Mai rahama sai su faxi su yi sujjada suna kuka



Sourate: Suratul Anbiya

Verset : 76

وَنُوحًا إِذۡ نَادَىٰ مِن قَبۡلُ فَٱسۡتَجَبۡنَا لَهُۥ فَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

(Ka tuna) lokacin da Nuhu ya roqi Ubangijinsa tun a da can[1], sannan Muka amsa masa (roqonsa) Muka tserar da shi da iyalinsa daga baqin ciki mai girma


1- Duba Suratu Nuh, aya ta 26-28.


Sourate: Suratul Anbiya

Verset : 77

وَنَصَرۡنَٰهُ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَآۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمَ سَوۡءٖ فَأَغۡرَقۡنَٰهُمۡ أَجۡمَعِينَ

Muka kuma taimake shi bisa mutanen da suka qaryata ayoyinmu. Lalle su sun kasance mutanen banza, sai Muka nutsar da su gaba xaya



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 23

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦ فَقَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥٓۚ أَفَلَا تَتَّقُونَ

Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta in ba Shi ba; me ya sa ne ba za ku yi taqawa ba.”



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 24

فَقَالَ ٱلۡمَلَؤُاْ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦ مَا هَٰذَآ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ يُرِيدُ أَن يَتَفَضَّلَ عَلَيۡكُمۡ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَأَنزَلَ مَلَـٰٓئِكَةٗ مَّا سَمِعۡنَا بِهَٰذَا فِيٓ ءَابَآئِنَا ٱلۡأَوَّلِينَ

Sai manya-manyan da suka kafirce daga mutanen nasa suka ce: “Ai wannan ba kowa ba ne face mutum irinku, yana so ne ya samu fifiko a kanku, kuma da Allah Ya ga dama da sai Ya saukar da mala’iku, mu ba mu tava jin irin wannan ba daga iyayenmu na farko



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 25

إِنۡ هُوَ إِلَّا رَجُلُۢ بِهِۦ جِنَّةٞ فَتَرَبَّصُواْ بِهِۦ حَتَّىٰ حِينٖ

“Ba kowa ba ne shi in ban da mutum da yake da (tavin) aljan, sai ku saurara masa har zuwa wani xan lokaci.”



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 26

قَالَ رَبِّ ٱنصُرۡنِي بِمَا كَذَّبُونِ

Ya ce: “Ubangijina Ka taimake ni game da abin da suka qaryata ni a kansa.”



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 27

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡهِ أَنِ ٱصۡنَعِ ٱلۡفُلۡكَ بِأَعۡيُنِنَا وَوَحۡيِنَا فَإِذَا جَآءَ أَمۡرُنَا وَفَارَ ٱلتَّنُّورُ فَٱسۡلُكۡ فِيهَا مِن كُلّٖ زَوۡجَيۡنِ ٱثۡنَيۡنِ وَأَهۡلَكَ إِلَّا مَن سَبَقَ عَلَيۡهِ ٱلۡقَوۡلُ مِنۡهُمۡۖ وَلَا تُخَٰطِبۡنِي فِي ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ إِنَّهُم مُّغۡرَقُونَ

Sai Muka yiwo masa wahayi cewa: “Ka sassaqa jirgin ruwa a qarqashin kulawarmu da umarninmu, sannan idan umarninmu (na hallaka su) ya zo, kuma tanderu ya vuvvugo da ruwa, sai ka saka ma’aurata guda biyu daga kowane jinsi a cikinsa, da kuma iyalanka, sai wanda kalmar (halaka) ta rigaya a kansa daga cikinsu; kuma kada ka ce min komai game da waxanda suka kafirta; lalle su waxanda za a nutsar ne



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 28

فَإِذَا ٱسۡتَوَيۡتَ أَنتَ وَمَن مَّعَكَ عَلَى ٱلۡفُلۡكِ فَقُلِ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي نَجَّىٰنَا مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

“To idan kai da waxanda suke tare da kai kuka daidaita a kan jirgin, sai ka ce: “Na gode wa Allah wanda Ya tserar da mu daga mutane azzalumai.”



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 29

وَقُل رَّبِّ أَنزِلۡنِي مُنزَلٗا مُّبَارَكٗا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡمُنزِلِينَ

Kuma ka ce: “Ubangijina Ka saukar da ni masauki mai albarka, Kai ne kuwa Fiyayyen masu saukarwa.”



Sourate: Suratul Mu’uminun

Verset : 30

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ وَإِن كُنَّا لَمُبۡتَلِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi, Mu kuma haqiqa Mun kasance Masu jarrabawa ne



Sourate: Suratul Furqan

Verset : 37

وَقَوۡمَ نُوحٖ لَّمَّا كَذَّبُواْ ٱلرُّسُلَ أَغۡرَقۡنَٰهُمۡ وَجَعَلۡنَٰهُمۡ لِلنَّاسِ ءَايَةٗۖ وَأَعۡتَدۡنَا لِلظَّـٰلِمِينَ عَذَابًا أَلِيمٗا

Mutanen Nuhu kuma lokacin da suka qaryata manzanni[1] sai Muka nutsar da su, Muka kuma sanya su wa’azi ga mutane, kuma Muka tanadi azaba mai raxaxi ga azzalumai


1- Watau ta hanyar qaryata Annabi Nuhu(), domin saqon duk manzanni guda xaya ne, shi ne kaxaita Allah da bauta.


Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 105

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Mutanen Nuhu sun qaryata mazanni[1]


1- Domin qaryata Annabi Nuhu () daidai yake da qaryata dukkan manzannin Allah, domin saqo iri xaya suke xauke da shi.


Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 106

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Nuhu ya ce da su: “Yanzu ba za ku kiyaye dokokin Allah ba?



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 107

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce a gare ku



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 108

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 109

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Ba na kuma tambayar ku wani lada a game da shi (isar da manzancin). Ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 110

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni.”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 111

۞قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ

Suka ce: “Yanzu ma yi imani da kai alhali qasqantattu ne mabiyanka?”



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 112

قَالَ وَمَا عِلۡمِي بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Ya ce: “Ba ni da sani game da abin da suka zamanto suna aikatawa



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 113

إِنۡ حِسَابُهُمۡ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّيۖ لَوۡ تَشۡعُرُونَ

“Hisabinsu kawai yana wajen Ubangijina ne; da za ku gane



Sourate: Suratus Shu’ara

Verset : 114

وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Ni kuma ba mai korar muminai ba ne