Sourate: Suratul Baqara

Verset : 128

رَبَّنَا وَٱجۡعَلۡنَا مُسۡلِمَيۡنِ لَكَ وَمِن ذُرِّيَّتِنَآ أُمَّةٗ مُّسۡلِمَةٗ لَّكَ وَأَرِنَا مَنَاسِكَنَا وَتُبۡ عَلَيۡنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka sanya mu masu miqa wuya gare Ka, kuma a cikin zurriyarmu ma (Ka samar) da wata al’umma mai miqa wuya gare Ka, kuma Ka nuna mana ayyaukan ibadarmu, kuma Ka karvi tubanmu, lalle Kai Mai yawan karvar tuba ne Mai jin qai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 132

وَوَصَّىٰ بِهَآ إِبۡرَٰهِـۧمُ بَنِيهِ وَيَعۡقُوبُ يَٰبَنِيَّ إِنَّ ٱللَّهَ ٱصۡطَفَىٰ لَكُمُ ٱلدِّينَ فَلَا تَمُوتُنَّ إِلَّا وَأَنتُم مُّسۡلِمُونَ

Kuma Ibrahimu da Ya’aqubu suka yi wasiyya da wannan ga ‘ya’yansu cewa: “Ya ‘ya’yana, lalle Allah Ya zava muku addini, don haka kada ku mutu face kuna Musulmi.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 133

أَمۡ كُنتُمۡ شُهَدَآءَ إِذۡ حَضَرَ يَعۡقُوبَ ٱلۡمَوۡتُ إِذۡ قَالَ لِبَنِيهِ مَا تَعۡبُدُونَ مِنۢ بَعۡدِيۖ قَالُواْ نَعۡبُدُ إِلَٰهَكَ وَإِلَٰهَ ءَابَآئِكَ إِبۡرَٰهِـۧمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ إِلَٰهٗا وَٰحِدٗا وَنَحۡنُ لَهُۥ مُسۡلِمُونَ

Ko kuna nan ne lokacin da mutuwa ta zo wa Ya’aqubu, lokacin da ya ce wa ‘ya’yansa: “Me za ku bauta wa a bayana?” Sai suka ce: “Za mu bauta wa abin bautarka kuma abin bautar iyayenka, Ibrahim da Isma’il da Ishaq, abin bauta guda xaya, kuma mu gare Shi muke miqa wuya.”



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 52

۞فَلَمَّآ أَحَسَّ عِيسَىٰ مِنۡهُمُ ٱلۡكُفۡرَ قَالَ مَنۡ أَنصَارِيٓ إِلَى ٱللَّهِۖ قَالَ ٱلۡحَوَارِيُّونَ نَحۡنُ أَنصَارُ ٱللَّهِ ءَامَنَّا بِٱللَّهِ وَٱشۡهَدۡ بِأَنَّا مُسۡلِمُونَ

To yayin da Isa ya ga alamun kafirci a tare da su sai ya ce: “Su wane ne za su taimake ni wajen kira zuwa ga Allah?” Sai Hawariyawa suka ce: “Mu ne mataimaka addinin Allah, mun yi imani da Allah, kuma ka ba da shaida cewa, mu Musulmai ne



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 53

رَبَّنَآ ءَامَنَّا بِمَآ أَنزَلۡتَ وَٱتَّبَعۡنَا ٱلرَّسُولَ فَٱكۡتُبۡنَا مَعَ ٱلشَّـٰهِدِينَ

“Ya Ubangijinmu, mun yi imani da abin da Ka saukar, kuma mun yi xa’a ga Manzo, don haka Ka rubuta mu tare da masu shaida.”



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 67

مَا كَانَ إِبۡرَٰهِيمُ يَهُودِيّٗا وَلَا نَصۡرَانِيّٗا وَلَٰكِن كَانَ حَنِيفٗا مُّسۡلِمٗا وَمَا كَانَ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Ibrahimu bai tava zama Bayahude ba, sannan bai tava zama Banasare ba, sai dai ya kasance mai barin varna ne, Musulmi, kuma bai kasance xaya daga cikin mushirikai ba



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 111

وَإِذۡ أَوۡحَيۡتُ إِلَى ٱلۡحَوَارِيِّـۧنَ أَنۡ ءَامِنُواْ بِي وَبِرَسُولِي قَالُوٓاْ ءَامَنَّا وَٱشۡهَدۡ بِأَنَّنَا مُسۡلِمُونَ

Kuma ka tuna lokacin da Na yi wahayi zuwa ga Hawariyyawa: “Ku yi imani da Ni da Manzona,” sai suka ce: “Mun yi imani, kuma Ka shaida cewa, mu Musulmai ne.”



Sourate: Suratul A’araf

Verset : 126

وَمَا تَنقِمُ مِنَّآ إِلَّآ أَنۡ ءَامَنَّا بِـَٔايَٰتِ رَبِّنَا لَمَّا جَآءَتۡنَاۚ رَبَّنَآ أَفۡرِغۡ عَلَيۡنَا صَبۡرٗا وَتَوَفَّنَا مُسۡلِمِينَ

“Kuma ba don komai za ka azabtar da mu ba sai don kawai mun yi imani da ayoyin Ubangijinmu yayin da suka zo mana. Ya Ubangijinmu, Ka zubo mana haquri, kuma Ka karvi rayukanmu muna Musulmi.”



Sourate: Suratu Yunus

Verset : 72

فَإِن تَوَلَّيۡتُمۡ فَمَا سَأَلۡتُكُم مِّنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَى ٱللَّهِۖ وَأُمِرۡتُ أَنۡ أَكُونَ مِنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ

“To idan kuka ba da baya, to ban tambaye ku wani lada ba; ladana yana ga Allah; an kuwa umarce ni da in kasance cikin Musulmai.”



Sourate: Suratu Yunus

Verset : 84

وَقَالَ مُوسَىٰ يَٰقَوۡمِ إِن كُنتُمۡ ءَامَنتُم بِٱللَّهِ فَعَلَيۡهِ تَوَكَّلُوٓاْ إِن كُنتُم مُّسۡلِمِينَ

Musa kuma ya ce: “Ya ku mutanena, idan har kun yi imani da Allah, to a gare Shi kawai za ku dogara in kun kasance Musulmai



Sourate: Suratu Yunus

Verset : 85

فَقَالُواْ عَلَى ٱللَّهِ تَوَكَّلۡنَا رَبَّنَا لَا تَجۡعَلۡنَا فِتۡنَةٗ لِّلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai suka ce: “Ga Allah kaxai muka dogara. Ya Ubangijinmu, kada ka sanya mu zama fitina ga mutane azzalumai



Sourate: Suratu Yunus

Verset : 86

وَنَجِّنَا بِرَحۡمَتِكَ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡكَٰفِرِينَ

“Ka kuma tserar da mu da rahamarka daga mutane kafirai.”



Sourate: Suratu Yusuf 

Verset : 101

۞رَبِّ قَدۡ ءَاتَيۡتَنِي مِنَ ٱلۡمُلۡكِ وَعَلَّمۡتَنِي مِن تَأۡوِيلِ ٱلۡأَحَادِيثِۚ فَاطِرَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ أَنتَ وَلِيِّۦ فِي ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِۖ تَوَفَّنِي مُسۡلِمٗا وَأَلۡحِقۡنِي بِٱلصَّـٰلِحِينَ

“Ya Ubangijina, haqiqa Ka ba ni wani abu na mulki, Ka kuma sanar da ni wani abu daga fassarar mafarki; Ya Mahaliccin sammai da qasa, Kai ne Majivincina a duniya da lahira; ka karvi raina ina Musulmi, Ka kuma haxa ni da (mutane) salihai.”



Sourate: Suratul Hajji

Verset : 78

وَجَٰهِدُواْ فِي ٱللَّهِ حَقَّ جِهَادِهِۦۚ هُوَ ٱجۡتَبَىٰكُمۡ وَمَا جَعَلَ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلدِّينِ مِنۡ حَرَجٖۚ مِّلَّةَ أَبِيكُمۡ إِبۡرَٰهِيمَۚ هُوَ سَمَّىٰكُمُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ مِن قَبۡلُ وَفِي هَٰذَا لِيَكُونَ ٱلرَّسُولُ شَهِيدًا عَلَيۡكُمۡ وَتَكُونُواْ شُهَدَآءَ عَلَى ٱلنَّاسِۚ فَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَٱعۡتَصِمُواْ بِٱللَّهِ هُوَ مَوۡلَىٰكُمۡۖ فَنِعۡمَ ٱلۡمَوۡلَىٰ وَنِعۡمَ ٱلنَّصِيرُ

Kuma ku yi jihadi wajen (xaukaka addinin) Allah iyakar iyawarku. Shi ne Ya zave ku, bai kuma sanya muku wani qunci ba cikin addini. Addinin Babanku ne Ibrahimu. (Allah) Shi ne Ya kira ku Musulmi tuntuni, da kuma cikin wannan (Alqur’ani) don Manzo ya zama shaida a gare ku, ku kuma ku zama shaida ga (sauran) mutane. To sai ku tsai da salla kuma ku ba da zakka, ku kuma yi riqo da (addinin) Allah, Shi ne Majivincin al’amarinku; to madalla da Majivinci, kuma madalla da Mataimaki



Sourate: Suratun Namli

Verset : 31

أَلَّا تَعۡلُواْ عَلَيَّ وَأۡتُونِي مُسۡلِمِينَ

“Kada ku yi min girman kai, ku zo min kuna masu miqa wuya!”



Sourate: Suratun Namli

Verset : 42

فَلَمَّا جَآءَتۡ قِيلَ أَهَٰكَذَا عَرۡشُكِۖ قَالَتۡ كَأَنَّهُۥ هُوَۚ وَأُوتِينَا ٱلۡعِلۡمَ مِن قَبۡلِهَا وَكُنَّا مُسۡلِمِينَ

To lokacin da ta zo, sai aka ce (da ita): “Shin haka kuwa gadonki yake?” Sai ta ce: “Sai ka ce shi.” (Sulaimanu ya ce): “An kuwa ba mu ilimi tun gabaninta, kuma mun kasance Musulmi



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 36

فَمَا وَجَدۡنَا فِيهَا غَيۡرَ بَيۡتٖ مِّنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ

Sai ba mu sami wani (gida) a cikinta ba in ban da gida xaya na Musulmi[1]


1- Shi ne gidan Annabi Lux (), in ban da matarsa, ita ba ta yi imani ba.