Sourate: Suratul Baqara

Verset : 51

وَإِذۡ وَٰعَدۡنَا مُوسَىٰٓ أَرۡبَعِينَ لَيۡلَةٗ ثُمَّ ٱتَّخَذۡتُمُ ٱلۡعِجۡلَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَنتُمۡ ظَٰلِمُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka yi wa Musa wa’adin (ganawa da shi) na kwana arba’in, sannan ku kuma kuka kama bautar xan maraqi a bayansa, alhalin kuna masu zaluntar kawunanku



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 52

ثُمَّ عَفَوۡنَا عَنكُم مِّنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Sannan sai Muka yi muku afuwa bayan haka, don ku yi godiya



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 53

وَإِذۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡفُرۡقَانَ لَعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka ba wa Musa Littafin (Attaura) da abin da yake rarrabewa (tsakanin gaskiya da qarya) don ku shiriya



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 54

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ يَٰقَوۡمِ إِنَّكُمۡ ظَلَمۡتُمۡ أَنفُسَكُم بِٱتِّخَاذِكُمُ ٱلۡعِجۡلَ فَتُوبُوٓاْ إِلَىٰ بَارِئِكُمۡ فَٱقۡتُلُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ عِندَ بَارِئِكُمۡ فَتَابَ عَلَيۡكُمۡۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma ku tuna lokacin da Musa ya cewa mutanensa: “Ya ku mutanena, lalle ku kun zalunci kawunanku ta hanyar mayar da xan maraqi abin bauta, don haka ku tuba zuwa ga Mahaliccinku, kuma ku kashe kawunanku; wannan shi ne ya fi alheri a gare ku a wajen Mahaliccinku. Lalle shi Mai yawan karvar tuba ne, Mai yawan jin qai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 55

وَإِذۡ قُلۡتُمۡ يَٰمُوسَىٰ لَن نُّؤۡمِنَ لَكَ حَتَّىٰ نَرَى ٱللَّهَ جَهۡرَةٗ فَأَخَذَتۡكُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَأَنتُمۡ تَنظُرُونَ

Kuma ku tuna lokacin da kuka ce: “Ya Musa ba za mu yi imani da kai ba har sai mun ga Allah a sarari”, sai tsawa ta halaka ku, alhali kuma kuna kallo



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 56

ثُمَّ بَعَثۡنَٰكُم مِّنۢ بَعۡدِ مَوۡتِكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Sannan sai Muka tashe ku bayan mutuwarku, don ku yi godiya



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 57

وَظَلَّلۡنَا عَلَيۡكُمُ ٱلۡغَمَامَ وَأَنزَلۡنَا عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَنَّ وَٱلسَّلۡوَىٰۖ كُلُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا رَزَقۡنَٰكُمۡۚ وَمَا ظَلَمُونَا وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Kuma Muka yi muku inuwa da girgije, kuma Muka saukar muku da mannu da (soyayyun) tsuntsayen salwa, ku ci daga daxaxan abin da Muka arzuta ku da shi; kuma ba su zalince Mu ba, sai dai kawunansu kaxai suke zalunta



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 58

وَإِذۡ قُلۡنَا ٱدۡخُلُواْ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةَ فَكُلُواْ مِنۡهَا حَيۡثُ شِئۡتُمۡ رَغَدٗا وَٱدۡخُلُواْ ٱلۡبَابَ سُجَّدٗا وَقُولُواْ حِطَّةٞ نَّغۡفِرۡ لَكُمۡ خَطَٰيَٰكُمۡۚ وَسَنَزِيدُ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka ce: “Ku shiga wannan alqaryar ku ci daga (kayan marmarinta ta) inda kuka ga dama cikin yalwa, kuma ku shiga qofar garin a duqe, kuma ku ce: “(Allah Ka) kankare mana laifuffukanmu”, za Mu gafarta muku laifuffukanku. Kuma za Mu qara wa masu kyautatawa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 59

فَبَدَّلَ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ قَوۡلًا غَيۡرَ ٱلَّذِي قِيلَ لَهُمۡ فَأَنزَلۡنَا عَلَى ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ رِجۡزٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

Sai waxanda suka yi zalunci suka canza maganar da aka faxa musu, sai Muka saukar da wata azaba daga sama a kan waxanda suka yi zalunci saboda abin da suke aikatawa na fasiqanci



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 60

۞وَإِذِ ٱسۡتَسۡقَىٰ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ فَقُلۡنَا ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡحَجَرَۖ فَٱنفَجَرَتۡ مِنۡهُ ٱثۡنَتَا عَشۡرَةَ عَيۡنٗاۖ قَدۡ عَلِمَ كُلُّ أُنَاسٖ مَّشۡرَبَهُمۡۖ كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ مِن رِّزۡقِ ٱللَّهِ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Musa ya roqa wa mutanensa ruwan sha, sai Muka ce: “Ka bugi dutse da sandarka”, sai idanuwan marmaron ruwa goma sha biyu suka vuvvugo daga cikinsa. Haqiqa kowaxanne mutane sun san mashayarsu. (Muka ce): “Ku ci kuma ku sha daga arzikin Allah, kuma kada ku yaxa varna a bayan qasa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 61

وَإِذۡ قُلۡتُمۡ يَٰمُوسَىٰ لَن نَّصۡبِرَ عَلَىٰ طَعَامٖ وَٰحِدٖ فَٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُخۡرِجۡ لَنَا مِمَّا تُنۢبِتُ ٱلۡأَرۡضُ مِنۢ بَقۡلِهَا وَقِثَّآئِهَا وَفُومِهَا وَعَدَسِهَا وَبَصَلِهَاۖ قَالَ أَتَسۡتَبۡدِلُونَ ٱلَّذِي هُوَ أَدۡنَىٰ بِٱلَّذِي هُوَ خَيۡرٌۚ ٱهۡبِطُواْ مِصۡرٗا فَإِنَّ لَكُم مَّا سَأَلۡتُمۡۗ وَضُرِبَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلذِّلَّةُ وَٱلۡمَسۡكَنَةُ وَبَآءُو بِغَضَبٖ مِّنَ ٱللَّهِۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ كَانُواْ يَكۡفُرُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَيَقۡتُلُونَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ بِغَيۡرِ ٱلۡحَقِّۚ ذَٰلِكَ بِمَا عَصَواْ وَّكَانُواْ يَعۡتَدُونَ

Kuma ku tuna lokacin da kuka ce: “Ya Musa, ba za mu iya haquri a kan abinci iri xaya ba, don haka ka roqa mana Ubangijinka Ya fitar mana (wani abincin) daga abin da qasa take tsirarwa, daga mabunqusanta da gurjinta da alkamarta da wakenta da albasarta.” Sai ya ce, “Yanzu kwa nemi musanya qasqantaccen abu da wanda yake shi ne mafifici? To ku sauka kowane gari, domin za ku samu abin da kuka roqa (a cikinsa).” Don haka sai aka sanya musu qasqanci da talauci, kuma suka koma da fushin Allah. Hakan ya faru gare su ne saboda sun kasance suna kafirce wa ayoyin Allah, kuma suna kashe annabawa ba tare da wani haqqi ba. Hakan ya faru saboda savon da suka yi da kuma ta’addancin da suka riqa yi



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 62

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَادُواْ وَٱلنَّصَٰرَىٰ وَٱلصَّـٰبِـِٔينَ مَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَلَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Lalle waxanda suka yi imani da Yahudawa da Nasara da Sabi’awa[1], duk wanda ya yi imani da Allah da ranar Lahira kuma ya yi aiki na qwarai, to suna da ladansu a wurin Ubangijinsu, kuma babu tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba


1- Waxanda suka yi imani, su ne al’ummar Annabi Muhammadu (). Yahudawa, ana nufin mabiya Annabi Musa () kafin a shafe addininsa, ko kafin su gurvata shi. Nasara, ana nufin mabiya Annabi Isa () kafin a shafe addininsa ko kafin su gurvata shi. Sabi’awa, wasu qungiyoyi ne, daga cikinsu akwai masu aqidar kaxaita Allah da haramta duk wata alfasha da zalunci, duk da kasancewarsu ba bisa wani addini suke ba, to amma ba sa aikata shirka.


Sourate: Suratul Baqara

Verset : 63

وَإِذۡ أَخَذۡنَا مِيثَٰقَكُمۡ وَرَفَعۡنَا فَوۡقَكُمُ ٱلطُّورَ خُذُواْ مَآ ءَاتَيۡنَٰكُم بِقُوَّةٖ وَٱذۡكُرُواْ مَا فِيهِ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka xauki alqawari mai qarfi daga gare ku, kuma Muka xaga dusten Xuri a kanku (Muka ce): “Ku karvi abin da Muka ba ku da qarfi (Attaura), kuma ku tuna abin da yake cikinsa, don ku yi taqawa.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 64

ثُمَّ تَوَلَّيۡتُم مِّنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَۖ فَلَوۡلَا فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ وَرَحۡمَتُهُۥ لَكُنتُم مِّنَ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Sannan bayan haka sai kuka juya da baya, to ba domin falalar Allah da rahamarsa a gare ku ba, lalle da kun kasance daga cikin asararru



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 65

وَلَقَدۡ عَلِمۡتُمُ ٱلَّذِينَ ٱعۡتَدَوۡاْ مِنكُمۡ فِي ٱلسَّبۡتِ فَقُلۡنَا لَهُمۡ كُونُواْ قِرَدَةً خَٰسِـِٔينَ

Kuma haqiqa kun san waxanda suka yi shisshigi daga cikinku game da ranar Assabar, sai Muka ce da su: “Ku zama birrai kuna qasqantattu.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 66

فَجَعَلۡنَٰهَا نَكَٰلٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهَا وَمَا خَلۡفَهَا وَمَوۡعِظَةٗ لِّلۡمُتَّقِينَ

Sai Muka sanya ta (wannan uqubar) ta zama izina ga (al’ummomin) da suke zamanin faruwarta da kuma (garuruwan) da suke daura da su, kuma don ta zama wa’azi ga masu taqawa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 67

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦٓ إِنَّ ٱللَّهَ يَأۡمُرُكُمۡ أَن تَذۡبَحُواْ بَقَرَةٗۖ قَالُوٓاْ أَتَتَّخِذُنَا هُزُوٗاۖ قَالَ أَعُوذُ بِٱللَّهِ أَنۡ أَكُونَ مِنَ ٱلۡجَٰهِلِينَ

Kuma ku tuna lokacin da Musa ya ce wa mutanensa: “Allah Yana umartar ku da ku yanka saniya”, sai suka ce: “Yanzu ka riqa yi mana izgili?” Sai ya ce: “Ina neman Allah Ya kiyaye ni da in zama cikin jahilai!”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 68

قَالُواْ ٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُبَيِّن لَّنَا مَا هِيَۚ قَالَ إِنَّهُۥ يَقُولُ إِنَّهَا بَقَرَةٞ لَّا فَارِضٞ وَلَا بِكۡرٌ عَوَانُۢ بَيۡنَ ذَٰلِكَۖ فَٱفۡعَلُواْ مَا تُؤۡمَرُونَ

Sai suka ce: “Ka roqa mana Ubangijinka Ya yi mana bayanin yaya take?” Sai ya ce: “Lalle Shi Yana cewa, lalle ita saniya ce, ba tsohuwa ba kuma ba budurwa ba, tana tsakatsakin haka.” Don haka ku aikata abin da ake umartar ku



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 69

قَالُواْ ٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُبَيِّن لَّنَا مَا لَوۡنُهَاۚ قَالَ إِنَّهُۥ يَقُولُ إِنَّهَا بَقَرَةٞ صَفۡرَآءُ فَاقِعٞ لَّوۡنُهَا تَسُرُّ ٱلنَّـٰظِرِينَ

Sai suka ce: “Ka roqa mana Ubangijinka Ya bayyana mana mene ne launinta?” Sai ya ce, “Lalle Shi Yana cewa, lalle ita saniya ce mai launin fatsi-fatsi mai tsananin cizawa, tana faranta wa masu kallon ta rai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 70

قَالُواْ ٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُبَيِّن لَّنَا مَا هِيَ إِنَّ ٱلۡبَقَرَ تَشَٰبَهَ عَلَيۡنَا وَإِنَّآ إِن شَآءَ ٱللَّهُ لَمُهۡتَدُونَ

Sai suka ce: “Ka roqa mana Ubangijinka Ya bayyana mana yaya take, lalle shanu sun rikitar da mu, kuma lalle mu, insha Allahu masu shiryuwa ne.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 71

قَالَ إِنَّهُۥ يَقُولُ إِنَّهَا بَقَرَةٞ لَّا ذَلُولٞ تُثِيرُ ٱلۡأَرۡضَ وَلَا تَسۡقِي ٱلۡحَرۡثَ مُسَلَّمَةٞ لَّا شِيَةَ فِيهَاۚ قَالُواْ ٱلۡـَٰٔنَ جِئۡتَ بِٱلۡحَقِّۚ فَذَبَحُوهَا وَمَا كَادُواْ يَفۡعَلُونَ

Ya ce: “Lalle Shi Yana cewa, ita saniya ce wadda ba horarriya ba ce da take noma kasa, kuma ba ta shayar da shuka; lafiyayya ce, babu dabbare-dabbare a jikinta”. Sai suka ce: “Yanzu ne ka zo da gaskiya”. Sai suka yanka ta, kamar dai ba za su aikata ba



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 87

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَقَفَّيۡنَا مِنۢ بَعۡدِهِۦ بِٱلرُّسُلِۖ وَءَاتَيۡنَا عِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ٱلۡبَيِّنَٰتِ وَأَيَّدۡنَٰهُ بِرُوحِ ٱلۡقُدُسِۗ أَفَكُلَّمَا جَآءَكُمۡ رَسُولُۢ بِمَا لَا تَهۡوَىٰٓ أَنفُسُكُمُ ٱسۡتَكۡبَرۡتُمۡ فَفَرِيقٗا كَذَّبۡتُمۡ وَفَرِيقٗا تَقۡتُلُونَ

Kuma haqiqa Mun ba wa Musa Littafi, kuma Muka biyo bayansa da manzanni, kuma Mun bai wa Isa xan Maryam hujjoji bayyananu, kuma Mun qarfafe shi da Ruhi mai tsarki. Ashe yanzu duk sa’adda wani manzo ya zo muku da abin da zukatanku ba sa so, sai ku yi girman kai, don haka sai ku qaryata wasu, kuma ku kashe wasu?



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 92

۞وَلَقَدۡ جَآءَكُم مُّوسَىٰ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ ثُمَّ ٱتَّخَذۡتُمُ ٱلۡعِجۡلَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَنتُمۡ ظَٰلِمُونَ

Haqiqa Musa ya zo muka da hujjoji bayyanannu, sannan kuka bauta wa xan maraqi bayansa alhalin kuna azzalumai



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 153

يَسۡـَٔلُكَ أَهۡلُ ٱلۡكِتَٰبِ أَن تُنَزِّلَ عَلَيۡهِمۡ كِتَٰبٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِۚ فَقَدۡ سَأَلُواْ مُوسَىٰٓ أَكۡبَرَ مِن ذَٰلِكَ فَقَالُوٓاْ أَرِنَا ٱللَّهَ جَهۡرَةٗ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ بِظُلۡمِهِمۡۚ ثُمَّ ٱتَّخَذُواْ ٱلۡعِجۡلَ مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُمُ ٱلۡبَيِّنَٰتُ فَعَفَوۡنَا عَن ذَٰلِكَۚ وَءَاتَيۡنَا مُوسَىٰ سُلۡطَٰنٗا مُّبِينٗا

Ma’abota Littafi (Yahudawa da Nasara) suna tambayar ka cewa, ka saukar musu da wani cikakken littafi daga sama. To haqiqa da ma can sun tambayi Musa abin da ya fi wannan girma, da suka ce: “Ka nuna mana Allah a fili,” sai tsawa ta far musu a sanadiyyar zaluncinsu. Sannan kuma suka riqi xan maraqi abin bauta bayan hujjoji sun zo musu, sai Muka yi (musu) afuwa a kan haka. Kuma Muka bai wa Musa hujja bayyananniya



Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 164

وَرُسُلٗا قَدۡ قَصَصۡنَٰهُمۡ عَلَيۡكَ مِن قَبۡلُ وَرُسُلٗا لَّمۡ نَقۡصُصۡهُمۡ عَلَيۡكَۚ وَكَلَّمَ ٱللَّهُ مُوسَىٰ تَكۡلِيمٗا

(Muka) kuma aiko manzanni waxanda Muka ba ka labarinsu tun da farko, da waxansu manzannin daban da ba Mu ba ka labarinsu ba; kuma Allah Ya yi magana da Musa kai-tsaye



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 20

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ يَٰقَوۡمِ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَةَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ إِذۡ جَعَلَ فِيكُمۡ أَنۢبِيَآءَ وَجَعَلَكُم مُّلُوكٗا وَءَاتَىٰكُم مَّا لَمۡ يُؤۡتِ أَحَدٗا مِّنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma (ka tuna) lokacin da Musa ya ce wa mutanensa: “Ya ku mutanena, ku tuna ni’imar Allah da Ya yi muku, yayin da Ya sanya annabawa da yawa a cikinku, kuma Ya sanya ku sarakuna, kuma Ya ba ku irin abin da bai ba wa wani cikin talikai ba



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 21

يَٰقَوۡمِ ٱدۡخُلُواْ ٱلۡأَرۡضَ ٱلۡمُقَدَّسَةَ ٱلَّتِي كَتَبَ ٱللَّهُ لَكُمۡ وَلَا تَرۡتَدُّواْ عَلَىٰٓ أَدۡبَارِكُمۡ فَتَنقَلِبُواْ خَٰسِرِينَ

“Ya ku mutanena, ku shiga qasar nan mai tsarki[1], wadda Allah Ya wajabta muku (shigarta), kuma kada ku yarda ku juya baya, sai ku komo kuna hasararru.”


1- Qasa mai tsarki ita ce Baitul Maqdis.


Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 22

قَالُواْ يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّ فِيهَا قَوۡمٗا جَبَّارِينَ وَإِنَّا لَن نَّدۡخُلَهَا حَتَّىٰ يَخۡرُجُواْ مِنۡهَا فَإِن يَخۡرُجُواْ مِنۡهَا فَإِنَّا دَٰخِلُونَ

Suka ce, “Ya kai Musa, lalle a cikinta akwai waxansu mutane masu tsananin qarfi, kuma mu ba za mu shige ta ba har sai sun fita daga cikinta, don haka idan suka fita daga cikinta, to lalle za mu shiga.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 23

قَالَ رَجُلَانِ مِنَ ٱلَّذِينَ يَخَافُونَ أَنۡعَمَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمَا ٱدۡخُلُواْ عَلَيۡهِمُ ٱلۡبَابَ فَإِذَا دَخَلۡتُمُوهُ فَإِنَّكُمۡ غَٰلِبُونَۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَتَوَكَّلُوٓاْ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Waxansu mutane biyu daga cikin masu jin tsoron (Allah), waxanda Allah Ya yi musu ni’ima (ta imani), suka ce: “Ku shigar musu ta qofar (garin); idan har kun shige shi, to lalle ku masu cin nasara ne. Kuma ga Allah kaxai za ku dogara, idan kun kasance ku muminai ne.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 24

قَالُواْ يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّا لَن نَّدۡخُلَهَآ أَبَدٗا مَّا دَامُواْ فِيهَا فَٱذۡهَبۡ أَنتَ وَرَبُّكَ فَقَٰتِلَآ إِنَّا هَٰهُنَا قَٰعِدُونَ

Suka ce; “Ya kai Musa, lalle mu fa ba za mu tava shigar ta ba har abada, matuqar suna cikinta; sai ka je kai da Ubangijinka ku yi yaqin, lalle mu kam muna nan a zaune.”