Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 17

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

(Aka ce da shi): Ka tafi zuwa ga Fir’auna, haqiqa shi ya yi xagawa



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 18

فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ

Sai ka ce: “Shin zai yiwu gare ka kuwa ka tsarkaka?



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 19

وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ

“In kuma shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka, sai ka ji tsoron Sa?



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 20

فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Sai ya nuna masa babbar aya[1]


1- Watau ya nuna masa hannun mai haske kamar fitila da kuma sandarsa mai rikixa ta zama macijiya.


Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 21

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

Sai ya qaryata ya kuma kangare



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 22

ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ

Sannan ya ba da baya yana ta gaggawa



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 23

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

Sai ya tattara (jama’arsa) sai ya yi shela



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 24

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Sai ya ce, “Ni ne ubangijinku mafi girma!”



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 25

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ

Saboda haka Allah Ya kama shi da azabar lahira (watau Jahannama) da ta duniya (watau nutse wa a ruwa)



Sourate: Suratun Nazi’at

Verset : 26

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ

Lalle a game da wannan tabbas akwai izina ga wanda yake tsoron (Allah)