Sourate: Suratuz Zumar

Verset : 7

إِن تَكۡفُرُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَنِيٌّ عَنكُمۡۖ وَلَا يَرۡضَىٰ لِعِبَادِهِ ٱلۡكُفۡرَۖ وَإِن تَشۡكُرُواْ يَرۡضَهُ لَكُمۡۗ وَلَا تَزِرُ وَازِرَةٞ وِزۡرَ أُخۡرَىٰۚ ثُمَّ إِلَىٰ رَبِّكُم مَّرۡجِعُكُمۡ فَيُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَۚ إِنَّهُۥ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Idan kun kafirce, to lalle Allah Mawadaci ne ga barin ku, ba Ya kuma yarda da kafirci daga bayinsa. Idan kuwa kuka gode Zai yarda da godiyar taku. Kuma wani rai ba ya xaukar laifin wani. Sannan zuwa ga Ubangijinku ne makomarku take, sannan Ya ba ku labarin irin abubuwan da kuka kasance kuna aikatawa. Lalle Shi Masanin abubuwan da suke cikin qiraza ne



Sourate: Suratuz Zumar

Verset : 44

قُل لِّلَّهِ ٱلشَّفَٰعَةُ جَمِيعٗاۖ لَّهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ ثُمَّ إِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Ka ce: “Ceto gaba xaya na Allah ne; mulkin sammai da qasa nasa ne Shi kaxai; sannan kuma wurinsa ne kawai za a komar da ku.”



Sourate: Suratu Fussilat

Verset : 21

وَقَالُواْ لِجُلُودِهِمۡ لِمَ شَهِدتُّمۡ عَلَيۡنَاۖ قَالُوٓاْ أَنطَقَنَا ٱللَّهُ ٱلَّذِيٓ أَنطَقَ كُلَّ شَيۡءٖۚ وَهُوَ خَلَقَكُمۡ أَوَّلَ مَرَّةٖ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Sai Suka ce da fatunsu: “Don me kuka ba da shaida a kanmu?” Suka ce: “Allah da Ya bai wa kowane abu ikon yin furuci mu ma Shi Ya ba mu ikon furuci, Shi ne kuma Ya halicce ku tun farko, gare Shi kuma kaxai za a mayar da ku.”



Sourate: Suratuz Zukhruf 

Verset : 85

وَتَبَارَكَ ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَعِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلسَّاعَةِ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Kuma wanda Yake da mulkin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu alhairansa sun yi yawa, kuma a wurinsa sanin (ranar) alqiyama yake, wurinsa kuma za a komar da ku



Sourate: Suratul Jasiya

Verset : 15

مَنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا فَلِنَفۡسِهِۦۖ وَمَنۡ أَسَآءَ فَعَلَيۡهَاۖ ثُمَّ إِلَىٰ رَبِّكُمۡ تُرۡجَعُونَ

Duk wanda ya yi aiki nagari to kansa ya yi wa; wanda kuma duk ya munana to a kansa; sannan wurin Ubangijinku ne kawai za a mayar da ku



Sourate: Suratul Jumu’a

Verset : 8

قُلۡ إِنَّ ٱلۡمَوۡتَ ٱلَّذِي تَفِرُّونَ مِنۡهُ فَإِنَّهُۥ مُلَٰقِيكُمۡۖ ثُمَّ تُرَدُّونَ إِلَىٰ عَٰلِمِ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِ فَيُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ka ce (da su): “Lalle ita mutuwar da kuke gudun ta, lalle za ta haxu da ku; sannan za a mayar da ku wurin Masanin voye da sarari, sannan Ya ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa.”



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 10

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ

A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Faufau, babu mafaka



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ

Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 13

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 14

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ

A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 15

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ

Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makomar (taka) take