Sourate: Suratu Abasa

Verset : 25

أَنَّا صَبَبۡنَا ٱلۡمَآءَ صَبّٗا

Cewa lalle Mu Muka zubo da ruwan sama zubowa



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 26

ثُمَّ شَقَقۡنَا ٱلۡأَرۡضَ شَقّٗا

Sannan Muka tsaga qasa tsagawa



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 27

فَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا حَبّٗا

Sai Muka tsiro da qwaya daga cikinta



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 28

وَعِنَبٗا وَقَضۡبٗا

Da inabai da ciyayi



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 29

وَزَيۡتُونٗا وَنَخۡلٗا

Da zaitun da dabino



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 30

وَحَدَآئِقَ غُلۡبٗا

Da gonaki cike da itatuwa



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 31

وَفَٰكِهَةٗ وَأَبّٗا

Da kayan marmari da makiyaya



Sourate: Suratu Abasa

Verset : 32

مَّتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ

Don jin daxinku da na dabbobinku



Sourate: Suratux Xariq

Verset : 5

فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ

To mutum ya duba mana, daga me aka halicce shi?



Sourate: Suratux Xariq

Verset : 6

خُلِقَ مِن مَّآءٖ دَافِقٖ

An halicce shi ne daga wani ruwa mai ingizar juna[1]


1- Watau maniyyi.


Sourate: Suratux Xariq

Verset : 7

يَخۡرُجُ مِنۢ بَيۡنِ ٱلصُّلۡبِ وَٱلتَّرَآئِبِ

Mai fita daga tsakanin tsatso da karankarma[1]


1- Watau daga tsakanin qashin bayan namiji da qasusuwan qirjinsa.


Sourate: Suratux Xariq

Verset : 8

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ

Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ

Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ

Da kuma sama yadda aka xaga ta?



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 19

وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ

Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 20

وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ

Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 1

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta