Sourate: Suratun Nisa’i

Verset : 163

۞إِنَّآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ كَمَآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ نُوحٖ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ مِنۢ بَعۡدِهِۦۚ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ وَٱلۡأَسۡبَاطِ وَعِيسَىٰ وَأَيُّوبَ وَيُونُسَ وَهَٰرُونَ وَسُلَيۡمَٰنَۚ وَءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ زَبُورٗا

Lalle Mun yi maka wahayi irin wahayin da Muka yi wa Nuhu da kuma annabawan da suka biyo bayansa, kuma Mun yi wahayi ga Ibrahimu da Isma’ila da Ishaqa da Ya’aqubu da kuma jikokin (Ya’aqubu) da Isa da Ayyuba da Yunusa da Haruna da Sulaimanu; kuma Muka bai wa Dawuda littafin Zabura



Sourate: Suratul An’am

Verset : 86

وَإِسۡمَٰعِيلَ وَٱلۡيَسَعَ وَيُونُسَ وَلُوطٗاۚ وَكُلّٗا فَضَّلۡنَا عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Da Isma’ilu da Alyasa’u da Yunusu da Luxu. Kowanne daga cikinsu kuma Mun fifita shi a kan (sauran) talikai



Sourate: Suratu Yunus

Verset : 98

فَلَوۡلَا كَانَتۡ قَرۡيَةٌ ءَامَنَتۡ فَنَفَعَهَآ إِيمَٰنُهَآ إِلَّا قَوۡمَ يُونُسَ لَمَّآ ءَامَنُواْ كَشَفۡنَا عَنۡهُمۡ عَذَابَ ٱلۡخِزۡيِ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَمَتَّعۡنَٰهُمۡ إِلَىٰ حِينٖ

Babu wasu mutane na wata alqarya da suka yi imani, sannan imaninsu ya amfane su, sai fa mutanen Yunusa, lokacin da suka yi imani sai Muka yaye musu azabar wulaqanci a rayuwar duniya, Muka kuma jiyar da su daxi har zuwa wani lokaci (iyakantacce)



Sourate: Suratul Anbiya

Verset : 87

وَذَا ٱلنُّونِ إِذ ذَّهَبَ مُغَٰضِبٗا فَظَنَّ أَن لَّن نَّقۡدِرَ عَلَيۡهِ فَنَادَىٰ فِي ٱلظُّلُمَٰتِ أَن لَّآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنتَ سُبۡحَٰنَكَ إِنِّي كُنتُ مِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma (ka tuna) ma’abocin kifi (wato Yunusa) lokacin da ya tafi yana cike da fushi[1], sannan ya zaci cewa ba za Mu quntata masa ba, sai ya kira (Mu) a cikin duffai[2] yana cewa: “Ba wani abin bauta da gaskiya sai Kai (ya Allah), tsarki ya tabbata a gare Ka, lallai ni na kasance cikin azzalumai!”


1- Watau saboda mutanensa sun kafe a kan kafirci sun qi yin imani.


2- Watau duhun dare da duhun kogi da duhun cikin kifi.


Sourate: Suratul Anbiya

Verset : 88

فَٱسۡتَجَبۡنَا لَهُۥ وَنَجَّيۡنَٰهُ مِنَ ٱلۡغَمِّۚ وَكَذَٰلِكَ نُـۨجِي ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Sai Muka amsa masa Muka kuma tserar da shi daga baqin ciki. Kamar haka kuwa Muke tserar da muminai



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 139

وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma lalle Yunusa tabbas yana daga cikin manzanni



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 140

إِذۡ أَبَقَ إِلَى ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ

(Ka tuna) lokacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwan da yake maqare



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 141

فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلۡمُدۡحَضِينَ

Sannan ya shiga quri’a, sai ya zama cikin waxanda aka yi galaba a kansu



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 142

فَٱلۡتَقَمَهُ ٱلۡحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٞ

Sai kifi ya haxiye shi, alhali yana abin zargi[1]


1- Watau a kan guduwa ya bar mutanensa ba tare da izinin Allah ba.


Sourate: Suratus Saffat

Verset : 143

فَلَوۡلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلۡمُسَبِّحِينَ

Ba don dai shi ya zama daga masu tsarkake Allah (da yawan tasbihi) ba



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 144

لَلَبِثَ فِي بَطۡنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

Tabbas da ya zauna a cikin cikinsa har zuwa ranar da za a tashe su[1]


1- Watau ranar alqiyama, domin zai zama shi ne qabarinsa.


Sourate: Suratus Saffat

Verset : 145

۞فَنَبَذۡنَٰهُ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٞ

Sai Muka jefa shi a tudu, a halin yana cikin rashin lafiya



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 146

وَأَنۢبَتۡنَا عَلَيۡهِ شَجَرَةٗ مِّن يَقۡطِينٖ

Muka kuma tsirar masa wata bishiya ta kabewa[1]


1- Domin ya rufe tsiraicinsa da ganyenta, ya kuma ci ‘ya’yanta, ya kuma sha inuwarta.


Sourate: Suratus Saffat

Verset : 147

وَأَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ مِاْئَةِ أَلۡفٍ أَوۡ يَزِيدُونَ

Muka kuma aika shi zuwa ga mutum dubu xari, ko kuma sama da haka



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 148

فَـَٔامَنُواْ فَمَتَّعۡنَٰهُمۡ إِلَىٰ حِينٖ

Sai suka yi imani, sai Muka jiyar da su daxi har zuwa wani lokaci



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 48

فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلۡحُوتِ إِذۡ نَادَىٰ وَهُوَ مَكۡظُومٞ

To ka yi haquri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar ma’abocin kifi (Yunus) a yayin da ya yi kira, alhali shi yana cike da baqin ciki



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 49

لَّوۡلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعۡمَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ مَذۡمُومٞ

Ba don wata rahama daga Ubangijinsa ta riske shi ba, da an jefar da shi a qungurmin daji alhali shi yana abin suka



Sourate: Suratul Qalam

Verset : 50

فَٱجۡتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Sai Ubangijinsa Ya zave shi Ya sanya shi daga (bayi) nagari